𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum malam khamis ga tambaya game da zubar da ciki, ni ce muke tare da mijina muna zaman lafiya amma ya ce mun ba ya son haihuwa, in na samu ciki sai ya sani dole na zubar, meye hukuncina a wurin Ubangijina? Kuma Macen da ta ke da ƙaramin goyo sai kuma ta samu wanin cikin. Ko za ta iya zubar da shi saboda neman lafiyar jaririnta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam
Warahmatullahi Wabarkatuhu.
A asali bai halatta a
zubar da ciki ba kome ƙanƙantansa, sai in akwai wata larura ƙaƙƙarfa. Kamar idan an
samu tabbaci ko marinjayin zaton cewa haihuwar za ta saka rayuwar mahaifiyar ko
na abin haihuwar ko kuma na su duka a cikin matsanancin hali. Misali idan mace
tanada ciki kuma likitoci suka tabbatar dacewa bazata iya haihuwa ba za ta mutu
to koda cikin yakai wata nawa idan akwai yanda za ayi azubar dashi aceci
rayuwarta to ya halatta domin rayuwarta tafi muhimmanci fiyada wanda yake ciki
domin shi baizo duniyarba.
Zubar da ciki don
tsoron talauci yana daga cikin manyan zunubai domin shima kisan kai ne. In dai
cikin yakai wata huɗu zuwa sama. Idan
cikin yakai wata huɗu to sannan an riga
an busa masa rai. Idan an zubar dashi da gangan, sai an biya diya yiah zuwa ga
Waliya yian jaririn (wato dangin Ubansa). Diya yiar jariri shi ne kwatankwacin
Rakuma guda biyar. Wato Ushurin diya yiar Mace ke nan. Kuma bayan haka za a
'yantar da Kuyanga guda, idan babu kuyangar sai ayi azumi Sittin amatsayin
kaffara.
Manyan malamai
(Rahimahumul Laah) sun sha bamban a kan haka. Dubi tattaunawa a kan mas’alar a
cikin littafin Al-Mausuu’atul Fiƙhiya yiatul
Muyassarah (6/256) na As-Shaikh Husayn Bn Audah Al-Awaayishah (Hafizahul Laah).
Amma abin da fatawar Shaikhul-Islaam Ibn Taymiyah (Rahimahul Laah) ta nuna shi
ne:
1. Wajibi ne su bayar
da cikakken bawa ko baiwa ko kuma farashinsa na ushurin (1/10) diya yia ga
sauran dangin wannan jaririn ban da su. Domin a ƙa’ida
wanda ya kashe wani ba kuma zai ci gadonsa ba.
2. Ushurin diya yia
shi ne dinare hamsin idan cikakkiyar diya yiar ita ce dinare ɗari biyar (500). Amma
idan dinare dubu (1, 000) ne kamar yadda hadisin Amr Bn Shu’aib ya nuna, ushurinsa
zai zama dinare ɗari ɗaya (100) ke nan a
yau.
3. Sannan kuma a wurin
yawancin malamai akwai kaffara a kansu na ’yanta bawa ko baiwa. Idan kuma ba su
samu ba sai su yi azumin watanni biyu a jere. Idan kuma ba su iya yi ba sai su
ciyar da miskinai guda sittin. (Majmuu’ul Fataawaa: 34/161).
Duk wanda suke da
hannu cikin kashe jaririn duk za su haɗu su biya diya yiar. Kuma kowannensu sai ya
'Yanta Kunyanga ko kuma ya yi azumi Sittin. Hujjah a nan ita ce Hadisin nan na
6910 acikin Sahihul Bukhariy, kuma na 1681 acikin Sahihu Muslim. Duk sun
ruwaito Hukuncin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yanke ma matar
data kwada ma wata Mai juna biyu dutse wanda ya yi sanadiya yiar mutuwarta da
kuma jaririnta. Amma idan cikin bai kai wata huɗu da samuwa ba, To babu diya yia ko
kaffara amma duk da haka dai Zunubi ne mai girma. Don Ƙarin bayani aduba
cikin MATALIBU ULIN NUHAA (juzu'i na 6 shafi na 50).
Duk wani laifi da aka
tilasta wa mutum ya yi shi, to idan ya yi wannan laifi saboda an fi ƙarfinsa, to Allah ba
zai kama shi da laifin wannan aiki ba, saboda hadisin da Abu Zharril Gifáriy ya
ruwaito cewa: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Lallai
Allah ya share wa al'ummata abin da suka yi da kuskure, da abin da suka yi da
mantuwa, da abin da aka tilasta masu yin sa". Ibn Majah 2043. Lallai shi
mijin ne za a ɗora wa laifin idan ya
tilasta miki zubar da ciki, musamman ma idan cikin ya kai watanni huɗu an hura masa rai.
Allaah Maɗaukakin Sarki Ya ce:
وَلَا
تَقْتُلُوا أَوْلَادَكُمْ مِنْ إِمْلَاقٍ نَحْنُ نَرْزُقُكُمْ وَإِيَّاهُم
Kuma kar ku kashe
’ya’yanku domin talauci (wanda kuke cikinsa), mu muke azurta ku da su kansu.
(Surah Al-An’am: 151).
Sannan kuma ya ce:
وَلَا
تَقْتُلُوا أَوْلَادَكُمْ خَشْيَةَ إِمْلَاقٍ نَحْنُ نَرْزُقُهُمْ وَإِيَّاكُم
Kuma kar ku kashe
’ya’yanku domin tsoron talauci (a gare su), mu muke azurta su da ku kanku.
(Surah Al-Israa’: 31).
Don haka, bai halatta
a kashe abin da ke cikin ciki ba domin tsoron talaucin da ake fama da shi yanzu,
ko wanda ake tsoron aukuwarsa nan gaba. Haka ma ko ba domin tsoron talauci ba
ne bai halatta a kashe jariri ba, matuƙar dai ya kai girman
da aka hura masa rai wato watanni huɗu. Kuma ko da bai kai watanni huɗun ba ma, malamai ba
su yarda a dakatar da tsarin halittar ɗan ta yin da ke cikin ciki haka nan siddan, ba
tare da wani dalili ƙwaƙƙwara ba.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.