Citation: Magaji, A. (2026). “Gudummuwar Harshen Hausa ta Fuskar Sasanci a Jihar Katsina.” In Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies, Vol. 04, No. 01, Pp. 16 – 21. www.doi.org/10.36349/djhs.2026.v04n01.003.
GUDUMMUWAR HARSHEN HAUSA TA FUSKAR SASANCI
A JIHAR KATSINA
Na
Adam Magaji
Ɗalibin
Ph.D., Sashen Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Umaru Musa Yar’adua, Katsina
Tsakure:
Wannan takarda ta gudanar da nazari ne kan
irin gudummuwar da harshen Hausa yake bayarwa wajen ƙulla sulhu da samar da
tsaro a Jihar Katsina. Manufar wannan takarda ita ce, nazarin irin rawar da
harshen Hausa yake takawa wajen sasanta tsakanin al’umma da masu garkuwa da
mutane da jami’an tsaro da shuwagabannin al’umma. An yi amfani da nau’in bincike
na bayani. An tattauna da masu ruwa da tsaki da kuma nazarin ayyukan masana. An
yi amfani da ra’in sulhu (Conflict Resolution Theory), a wannan bincike. An
gano cewa, harshen Hausa yana taka gaggarumar rawa wajen ƙulla sulhu da sasanci a
tsakanin al’umma. An gano cewa, amfani da harshen, yana ceton ɗimbin rayukan mutane daga salwanta fiye da yin amfani
da ƙarfi,
ko bindiga. An bayar da shawara a kan yadda za a ƙarfafa horo ga jami’an
tsaro dangane da dabarun iya sadarwa da harshen Hausa, domin a magance matsalar
tsaro. Hukuma ta riƙa
sanya shuwagabannin al’umma na gargajiya da malamai a cikin tsarin tsaro. Yin
hakan zai taimaka wajen gano bakin zaren wuraren da matsala take.
Muhimman Kalmomi: Harshe, Sulhu, Garkuwa.
1.0 Gabatarwa
Tsaro dai shi ne ginshiƙi na ci gaban kowace
irin al’umma (Funtua, 2021). Domin
haka, Allah (S.W.A) a cikin alƙur’anisa mai tsarki yana cewa, “Ku ji tsoron fitina wadda
idan ta zo, ba ta tsayawa ga waɗanda
suka jawo ta, tana shafar har ma wanda babu ruwansa ma” (Suratul Amfal: aya ta
25). A ɓangare
guda, masu iya magana suna cewa, “tsaro maganin tsoro.” Duk yadda wata ƙasa take da girma, idan tana fama
da rashin tsaro, ba za ta iya bunƙasa tattalin arzikinta yadda ya kamata ba. A Nijeriya, musamman jihohin da suke Arewa
maso-yamma,
suna fuskantar matsalar garkuwa da mutane a cikin
shekaru goma da suka gabata. Waɗannan
jihohi sun haɗa da Kaduna da Kano da Katsina da Jigawa da Zamfara da
Sakkwato da kuma Jihar Kebbi. Bugu da ƙari, daga cikin jihohin da wannan matsala ta fi
yin ƙamari
su ne Zamfara da Kaduna da Katsina da kuma Sakkwato.
A ƙoƙarin daƙile irin wannan matsala, hukumomi su kan yi amfani
da ƙarfin
tuwo ko makamai domin tunkararlamarin. Sai dai wannan bincike da aka gudanar
ya nuna cewa, yin sulhu da tattaunawa da harshen Hausa ya fi muhimmanci. Duba da cewa, harshen Hausa shi ne harshen da mafi yawan al’umma gami da masu
aikata laifin suke fahimta. Wannan ya sa, ya taka muhimmiyar rawa wajen yin sulhu a
tsakanin al’umma da masu garkuwa da mutane a Jihar Katsina.
Muradin wannan takarda, shi ne nazartar yadda harshen Hausa ya zama ɗaya daga cikin muhimman
kayan aiki na samar da tsaro fiye da ƙarfi, ko amfani da bakin bindiga a Jihar Katsina. Harshen ya taka wannan rawa ne ta fuskar kafafen sadarwa
da lallashi da girmama juna da karin magana da wa’azi gami da nasiha.
1.1 Muhimman Kalmomin Bincike
A wannnan muhallin, aka bayyana
ma’anoni na kalmomin da suka kzamo fitulu na wannan
nazari. Kalmomin da aka bayyana ma’anoninnsu su ne, harshen Hausa da tsaro da
sulhu da
kuma garkuwa.
1.1.1 Harshen Hausa
Lado (1964 sh11) cikin Yakasai, (2012, sh3)
ya bayyana cewa, harshe shi ne rai, ko zuciya ta duk wani tunani na aikin ɗan’adam, musamman kan abin da mutum yake ji da game da
kansa ko ƙasarsa,
ko addininsa ko kuma yadda shi kansa ya ɗauki kansa. Ma’anar da
aka bayar, ta bayar
da hasken cewa, harshen Hausa ana amfani
da shi a mafiya yawan yankunan da suke Afirka ta Yamma. Harshen ya mamaye
yankunan Nigeriya (musamman Arewacin ƙasar) da Nijar da Ghana da
Kamaru da sauransu. Ana kallon harshen a matsayin harshen sadarwa da cikniki a
faɗin nahiyar Afirka ta Yamma.
1.1.2 Tsaro
Tsaro shi ne shirya, ko gyara, ko jere wani abu domin samar da wata kariya
daga ɓarna (Sarkin Gulbi, 2016, sh. 372). Bisa fahimtar wannan ma’ana, takardar tana ganin tsaro
a matsayin hanyar kiyayewa, ko lura da duk wani abu da zai iya janyo hasara ko
kuma rasa rayuwar wani mutum ko dabba ko kuma wani abu da ake amfanuwa da shi
daga matsaloln ɓata-gari walau ɓarayi ko kuma ‘yan ta’adda.
1.1.3 Sulhu
Sulhu dai hanya ce ta sasanta da shiga tsakanin masu husuma biyu, ko daban-daban domin shirya
tsakaninsu (Sarkin Gulbi, 2016). La’akari
da irin bayanin da ya gabata, wannan takarda ta bayyana sulhu
a matsayin wata hanya ta daidaita ɓangarori guda biyu masu savani da
juna.
1.1.4 Garkuwa
Garkuwa ita ce, wani faffaɗan abu
da ake yi da ƙirgi ko ƙarfe don kare kai wajen yaƙi (Cibiyar Nazarin Harsunan
Nigeriya, 2006, sh. 159). Wannan takarda, tana ganin garkuwa a
matsayin kama wani mutum, ko
wani abu na amfani da nufin neman
kuɗin fansa, a wurin makusantansa.
2.0 Manufar Bincike
Manufar wannan takarda ita ce, nazarin
irin rawar da harshen Hausa yake takawa ta fuskar sasanta tsakanin masu
garkuwa da mutane da sauran al’umma da jami’an tsaro da shuwagabannin al’umma.
3.0 Hanyoyin Gudanar da Bincike
Dogara ga irin bayanan da aka tattaro da
kuma masaniyar ganin cewa, wannan bincike ne na bayani, ya sa aka yi bayanin
irin hanyoyin da aka bi wajen ƙulla sulhu da masu garkuwa da mutane a Jihar Katsina.
An yi amfani da hanyoyi guda biyu ya yin tattara bayanai. Hanya ta farko
(primary data) ita ce, ta tattaunawa da wasu jami’an tsaro da sarakunan
gargajiya da malamai da kuma ‘yan uwana waɗanda
aka sace, ko aka yi garkuwa da su. Haka
kuma, an dubi wasu rahotanni da
suka shafi tsaro waɗanda wasu masu ruwa da tsaki suka rubuta. Bugu
da ƙari,
takardar ta waiwayi wasu daga cikin ayyukan da aka gudanar a kan tsaro. An dai
dubi ayyukan da aka gudanar ne gwagwadon matakan ilimi daban-daban.
4.0 Ra’in Bincike
Wannan takarda da aka gudanar, an ɗora ta ne a bisa ra’in Sulhu (Conflict Resolution
Theory), wanda Adeyanju ya samar a (2018). Wannan ra’i, yana nuna cewa, fahimtar
juna ta hanyar tattaunawa da harshe tana magance rikici tsakanin al’umma,
musamman idan aka yi amfani da harshen da ɓangarorin guda biyu na masu rigima da juna suke
sadarwa da shi. Domin a cika irin waɗannan
sharuɗɗan, ya sa aka yi amfani da harshen Hausa a matsayin
harshen hulɗa da sadarwa a tsakanin al’umma da masu garkuwa da mutane
yayin gudanar da nazari.
5.0 Taƙaitaccen
Tarihin Matsalar Garkuwa da Mutane a Jihar Katsina
Masu azancin magana suna cewa, “idan
gemun ɗan’uwanka ya kama da wuta, to, ka shafa wa naka ruwa”.
Abin a bayyane yake, a shekarun baya, idan ana yin zancen garkuwa da mutane,
babu inda tunanin mai karatu, ko sauraro za ya nufa illa kudancin Nijeria. A
kwana a ta shi, sai wani sauyi ya faru a Arewacin Nijeriya, inda Fulani makiyaya suka riƙa kore tare da kwashe dabbobin ‘yan’uwansu. Sai dai
kash! Sai hukumomi da masu ruwa da tsaki suka yi wa matsalar abin da Hausawa suke cewa: “kallon raina kama ka ga gayya.” Wannan ya sa, abin ya ci gaba da fantsama a yankuna daban-daban. Kafin a farga, har wannnan matsala ta rikiɗe zuwa fashi da makami. Haka zalika, irin wannan
matsala, ta zama ruwan-dari a Jihohin Zamfara da Kaduna waɗanda
suke maƙwaftaka
da Jihar Katsina. Daga satar shanu ta rikiɗe
zuwa fashi da makami, inda suke shiga gari su ƙwace kuɗi da abinci da fasa shagunan mutane domin sata dukiyoyin jama’a.
Daga baya, sai abin ya koma garkuwa gami da kashe mutane waɗanda ba su ji ba, kuma ba su gani ba.
A Jihar Katsina, wannan matsala ta garkuwa
da mutane ta yi ƙamari
sosai, tun daga shekara ta (2015), zuwa ƙarshen shekar ta (2025), musamman a ƙananan hukumomin
Batsari da Jibia da Safana da Ƙanƙara da Faskari da Sabuwa da kuma Dutsinma. Sannu a hankali, matsalar
ta ci gaba da yaɗuwa zuwa wasu ƙananan hukumomi na Jihar Katsina, waɗanda suka haɗa
da: Ɗandume
da Funtuwa da Bakori da Musawa. Baya ga waɗannan ƙanan hukumomi, matsalar
ta ci gaba da fallatsa zuwa Kurfi da Malumfashi, a ƙarshen shekara ta
(2025).
Bugu da ƙari, masu yin garkuwa da
mutane sun ci gaba da kai hare-hare a kan ɗaiɗaikun mutane da manoma da ɗalibai da matafiya da ma’aikata da sauran jama’a waɗanda ba su gi ba, bas u gani ba. A wasu lokutan, a kan sami nasara ta kuɓutar da mutanen da aka sace, ko aka yi garkuwa da su,
ta hanyar yin amfani da ƙarfi, ko da bakin bindiga. A wasu lokutan ana samun
nasara ta hanyar shiga tsakani na shuwagabannin al’umma na gargajiya da kuma
malaman addinin Musulunci.
6.0 Gudummawar Harshen Hausa a Fagen Sasanci
Kamar yadda ya gabata, tsaro shi ne ginshiƙi na ci gaban kowace
irin al’umma (Funtua, 2021). Haka
kuma, tattaunawa da harshen da masu rikici da juna suke fahimta yana bayar da
damar a samu wata gaba ta ƙulla sulhu a tsakanin ɓangarori daban-daban na masu rigima da juna) Adeyanju,
2018). Wannan ya sa, harshe ya kasance hanyar sadarwa a tsakanin mutane ta
baka, ko ta rubutu, ko ta amfani da waɗansu
alamomi (Magaji, sh. 1). Hakan ya sa a cikin wannan takarda, aka yi nazarin yadda
harshen Hausa yake taka rawa a matsayin harshen sadarwa da shiga tsakani domin
yin sulhu
da sasanci tsakanin al’umma. Har
wa yau, takarda ta fito da tasirin da harshen yake da shi wajen daƙile ayyukan masu garkuwa da mutane. Duka waɗannandarajoji
suna faruwa ne saboda kasancewar
Hausa a matsayin harshen da al’umma da masu munanan laifukan ta’addancin suke fahimta, kuma suke hulɗa da ita a tsakaninsu. Wannan takarda ta yi la’akari
da matsayin da harshe yake da shi inda ta dube su ƙarƙashin waɗanda matakai da suke ƙasa:
6.1 Kalamai
Na Girmama Juna
Abin a bayyane yake, Hausawa suna da wata
al’ada ta girmama wanda suke magana da shi, ta hanyar zaɓen kalmomi na ladabi waɗanda
suke rage tsanani na wani abu da yake damun ɗan’uwansu.
Misali, irin
kalmomin da suke yin amfani da su ya yin tattaunawa da wanda suke yin magana da
shi sun haɗa da:
§ Dan
Allah a saurare mu: idan aka lura za a fahimci cewa, faɗin domin Allah a saurare mu da Hausawa suke cewa, baya
nuna tsoro, ko fargaba illa dai ladabi na magana a tsakaninsu da wanda suke
tattaunawa da shi. Hakan, yana bayar da dama zaunawa domin a fahimci juna.
§ Mu
zauna lafiya: Hausawa sukan yi amfani da irin wannan ladabi ne, domin su
kwantar da hankali na waɗanda suke yin rikici da juna a tsakaninsu.
§ A
riƙa yin haƙuri da juna: A kullum
Bahaushe mutum ne wanda yake son a zauna lafiya. Domin haka, z aka ji yana
cewa, mu riƙa
haƙuri da juna, tun da
Allah ya haɗa mu, dole ne sai wani ya vatawa wani a cikinmu.
§ Mu
‘yan’uwan juna ne: Za ka ji suna faɗar
cewa, Bahaushe da Bafulatani ‘yan’uwan juna ne, yin rikici a tsakaninmu abin
kunya ne.
Idan aka lura, za a fahimci cewa, yin amfani da
irin waɗannan kalmomin sukan rage girman tashin hankalin da
al’umma suka tsinci kansu a tsakaninsu da masu aikata garkuwa da mutane a Jihar
Katsina.
6.2 Azancin Magana
Bahaushe mutum ne mai tarin azanci da hikima
ta sarrafa harshe lokacin da yake tattaunawa, ko zance da abokin mu’amalarsa,
yakan saƙa
karin maganar da za ta jawo hankalinsa gami da nusar da shi dangane da yanayin
da ake a ciki. Misalan karin maganar da ake amfani da su a lokacin sasanci da
masu garkuwa da mutane a Jihar Katsina su ne:
§ Zaman
lafiya ya fi zama ɗan sarki: Wannan karin magana yana bayyana wa mai
sauraro cewa, idan babu zaman lafiya, sarki ma ba za ya iya gudanar da mulki
ba. Haka ma, sai da zaman lafiya ne al’umma suke ci gaba ta fuskar tatalin
arziki da lumana.
§ Duk
abin da ya taɓa hanci; idanuwa ruwa suke yi: Abin da wannan karin
magana yake nunawa a tsakanin Bahaushe da Bafulatani akwai danƙon zumunci, wannan ya sa
ake ce masu Hausa Fulani. Sakamakon irin wannan dangantaka suke ganin duk abin
da tava Bafulatani, babu makawa ya tava Bahaushe. Lura da cewa, akwai auratayya
da kasuwanci da dai sauran al’amiransu.
§ Abin
da arziki bai kawo ba, tsiya ba za ta kawo shi ba:
Kai-tsaye wannan azancn magana yana bayyana nuhimmancin zaman lafiya a tsakanin
vangarori guda biyu masu rigima da juna.
§ Ai
hankali ya fi ƙarfin
tuwo: Duk da irin muhimmancin tuwo ga rayuwar Bahaushe, idan aka lura za a
fahimci cewa, ya nuna hankali ya fi shi. Haka kuma, duk abin da aka bi a
hankali za a cimma nasarar warware shi.
Idan aka lura za a ga cewa, yin amfani da
irin waɗannan kalamai suna nuna muhimmancin sulhu, wanda kuma shi ne yake
haifar da zaman lafiya mai ɗorewa,
a tsakanin ɓangarori guda biyu masu rikici da juna.
6.3 Sarakunan
Gargajiya
Iyayen ƙasa watau sarakuna, shuwagabanni ne na gargajiya waɗanda suke da matuƙar ƙima a idanun talakkawansu, musamman idan aka lura da
yadda suke a ƙarƙashin jagorancin
masarautar Katsina (Katsina Emirate Council), suna taka muhimmiyar rawa domin shiga tsakani a
matsayinsu na iyayen ƙasa, ta hanyar kiran kowane vangare na masu rigima da
juna a zauna domin a ɗinke bakin zaren
matsalar da take farua.
La’akari da kasancewarsu a matsayin waɗanda
suka fi kusa da al’umma, ya sa al’ummar da suke jagoranta, a kullum suke ganin
su a matsayin wasu mutane masu hikima da gaskiya da riƙon amana. Domin haka,
kalamansu suna da matuƙar
tasiri wajen ƙulla
sulhu da samar da zaman lafiya a tsakanin ɓangarorin
guda biyu Wannan ya sa sarakunan gargajiya na Hausa suke naɗa su a matsayin sarkunan have ko na arɗo, hakan yana faruwa ne duk domin a samar da zaman
lafiya a cikin al’umma. Kazalika, waɗannan
sarakuna na have, suna taka rawa domin ganin sun hukunta duk wani mai laifi
daga cikin iiyalansu.
6.4 Malaman
Addini
Malaman addini a Jihar Katsina, suna taimakawa ta fuskar wanzar da zaman lafiya ta hanyar amfani da harshen Hausa, domin tunatar da masu aikata laifin yin garkuwa da mutane da sauraran wasu laifuffuka dangane da hukuncin da
ya shafi addini. Bayan haka, suna yi musu gargaɗi a
kan sakamakon da masu aikata laifi za su ci karo da shi, tun daga nan gidan
duniya har na gobe ƙiyama. Malama suna kiran su
domin su gaggauta tuba a kan ba za su ƙara aikata makamancin laifi irin sa ba. Irin wannan
gargaɗi, yana tasiri ga masu aikata laifin, musamman idan aka yi shi a cikin hikima
da tausayi.
Ganin cewa, babban harshen hulɗa da masu aikata garkuwa da sauran al’umma suke yin
mu’amala da shi, shi ne harshen Hausa. Sakamakon haka, malanan addini suke
amfani da shi wajen kira da yin gargaɗi
kan a zauna lafiya.
6.5 Tattaunawa da Jami’an Tsaro
Jami’an tsaro manyan ginshiƙai ne na samar da zaman
lafiya a tsakanin al’umma. A lokacin da ake tattunawa domin ƙulla sulhu da masu
garkuwa da mutane, jami’an tsaro sukan yi amfani da harshen Hausa kasancewar kowane ɓangare na al’umma da masu garkuwa suke fahimta, a
maimakon amfani da harshen Ingilishi. Hakan ya kawar da shakku, tare da samun
amincewa daga kowane ɓangare. Soba (2017 shafi 110) ya ambato tattaunawa da sa’ido da
bayar da wani muƙami da
za a ɗora wa alhakin lura da matsalar tsaro a matsayin dabarun
tsaro na gargajiya. Wannan dabara ta
rage tsoro daga masu aikata garkuwa da mutane. A taƙaice, amfani da wannan
hikima tana kawo sauƙi ƙwarai ta fuskar samun
damar tattaunawa
da masu garkuwa da mutane.
7.0 Ƙalubale
Kowane irin abu yana da irin nasa
cikas ko kuma ƙalubale. Sakamakon
haka, wannan takarda ta fahimci cewa, nasara ba za ta samu ba idan aka
sami ɗaya daga cikin waɗannan
abubuwa:
i. Ƙarancin ingantaccen horo na musamman a fannin sulhu ga
jami’an tsaro, wani babban cikas ne na ɗorewar zaman lafiya a tsakanin jama’a.
ii. Bambancin
harshe tsakanin ɓangarori guda biyu yana taimakawa wajen hana samun fahimtar juna. Sakamakon kowane vangare za ya fahimci cewa, kamar
ba za a yi masa adalci ba.
iii. Savanin
fahimta da rashin haɗin kai tsakanin jami’an tsaro da shugabannin al’umma yana kawo tarnaƙi ga abin da aka sa a gaba.
iv. Tasirin
kafafen sada zumunta na zamani wajen yada tsoro a tsakanin mutane wani babban ƙalubale ne wanda yake ƙara
haifar da koma baya a tsakanin al’umma. Misali, ‘yanta’adda za su kasha mutane
goma; amma sai ka ji a kafafen watsa labarai sun sanar da cewa, dubban mutane
suka rasa ransu sakamakon harin da ‘yanta’adda suka kai.
8.0 Sakamakon Bincike
Sakamakon wannan takarda da aka gudanar ta
gano cewa, harshen Hausa yana taka gaggarumar gudummuwa wajen ƙulla sasanci a tsakanin
masu garkuwa da mutane da sauran al’umma. An
gano yin amfani da harshen yana Rage tashin hankali da saka nishaɗi da
juna ta hanyar ladubban magana da
saka azanci da hikima gami
da yafewa juna.
Bugu da ƙari,
takardar ta gano cewa, harshen Hausa yana bayar da gudummawa wajen kuɓutar da rayukan mutane da dukiyoyinsu cikin
lumana. Daga ƙarshe, an fahimci cewa,
harshen Hausa ya zama ɗaya
daga cikin muhimman kayan aiki na samar da tsaro fiye da ƙarfi, ko yin amfani da
bakin bindiga a Jihar Katsina.
9.0 Shawarwari
Wasu daga cikin shawarwarin da wannan
takarda take
ganin idan an yi amfani da su za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a
jihar Katsina sun haɗa da:
i. Horar
da jami’an tsaro dabarun sadarwa da harshen Hausa, wani mataki ne na haɗa kan al’umma tare da fahimtar yanayin da suke ciki.
ii. Akwai buƙatar hukuma ta riƙa sanya shuwagabannin
al’umma na gargajiya da malamai a cikin tsarin tsaro. Yin hakan zai taimaka wajen gano bakin zaren
wuraren da matsala take.
iii. Yana
da kyau a kafa cibiyoyin samar da sulhu a tsakanin al’umma. Kafa cibiyoyin zai taimaka wajen kashe wutar
rikicin da za ta iya tashi tun ba ta kai ga ruruwa ba.
iv. Yana
da kyau a ƙara
inganta shirye-shiryen gidajen rediyo domin bunƙasa zaman lafiya ta hanyar
tattaunawa da fitattun magabata waɗanda
suka yi gwagwarmaya a rayuwarsu, wajen ƙara samun sababbin dabaru
da za su ƙara
tabbatar da ɗorewar zaman lafiya a tsakanin al’umma.
10.0 Kammalawa
Wannan takarda, ta yi ƙoƙari wajen fito da irin
gudummuwar da harshen Hausa yake bayarwa ta fuskar ƙulla sulhu gami da samar da
tsaro a Jihar Katsina. Haka
kuma, an yi tsokaci game da manufa da hanyoyin gudanar da bincike. Har wa yau,
takardar ta bayyana ra’in da aka jingina wannan nazari akai. Sai aka bayyana
matakan da aka yi amfani da su wajen samar da sulhu tsakanin ‘yanta’adda masu
garkuwa da mutane da sauran al’umma. Daga nan, takardar ta kawo sakamakon da
aka gano gami da shawarwari.
Manazarta
Adeyanju, D. (2018). Language and
conflict resolution in Nigeria. University Press.
Cibiyar Nazarin Harsunan Nigeriya, (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Ahmadu Bello
University Press.
Funtua, A. (2021). Security challenges in
Northwestern Nigeria. Journal of Peace Studies, 12(3), 44–60.
Magaji A. (2023), The impact of
audio-lingual method on the comprehension of Hausa written prose among
secondary schools students of Katsina State, Nigeria. (Masters Theasis),
Department of Arts and Social Science. Ahmadu Bello University.
Sarkin Gulbi, A. (2016).
Dabarun tsaro a ƙasar Hausa: bin diddiginsu a masarautar
Gummi. (Conference paper), National conference
for the Hausa Scholars Association, Kaduna State University.
Sarkin Gulbi, A. (2016).
Sulhu a gargajiyance: darasi daga daular
Sakkwato da
Kabi. (Takardar ƙarawa
juna sani), Tsangayar Fasaha da Addimin Musulunci, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Soba, A. S. (2017).
Tanadin tsaron gargajiya
a ƙasar
Zazzau: (waiwaye cikin zamunnan sarakunan
Haɓe 1435-1804). (Kundin digiri
na uku).
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Yakasai, S. A. (2012). Jagorar ilimin walwalar harshe. Amal Printing Press.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.