Ticker

6/recent/ticker-posts

Falalar Sahun Farko

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum mal. Khamis da fatan kana cikin koshin lafiya. Tambaya ta ita ce; Mene ne falalar sahun farko?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh.

Falalar sahun farko a cikin sallah ta jam'i tana da babban matsayi a Musulunci, inda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya nuna cewa ladanta da kima a wajen Allah sun yi yawa matuka har ma mutane da sun san abin da ke ciki da sun yi riga-ka-fi ko sun jefa ƙuri'a don samun damar tsayawa a ciki.

Sahun farko yana da matuƙar falala, musamman ga maza, saboda shi ne mafi alherin sahu, kuma yana daga cikin abubuwan da ake ƙarfafa musulmi ya yi gaggawar zuwa masallaci domin ya samu.

Daga cikin falalar gaggauta zuwa sahun farko akwai abin da Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce:

«لَوْ يَعْلَمُ النَّاسُ مَا فِي النِّدَاءِ وَالصَّفِّ الأَوَّلِ، ثُمَّ لَمْ يَجِدُوا إِلَّا أَنْ يَسْتَهِمُوا عَلَيْهِ لَاسْتَهَمُوا»

Ma'ana: “Da mutane sun san falalar da ke cikin kiran sallah (adhaan) da sahun farko, sannan ba su samu wata hanya ba sai sun yi kuri'a a kansu, da sun yi kuri'a.” (Bukhari da Muslim).

Daga Abi Hurairata R.A Ya ce: Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Mafi alkhairi sahun maza shi ne sahun farko, kuma mafi sharrin sahun maza, shi ne sahun karshe kuma mafi alkhairin sahun mata na karshe, mafi shirrin sahun mata na farko) (رواه مسلم).

A wani hadisi Aisha R.A tana cewa: Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Lallai Allah da mala'ikunsa suna yin Salati ga wadanda suke sadar da sahu, kuma wanda yacike wani gurbi acikin sahu, Allah zai daukaka darajarsa. (حسنه الألباني)

Daga Anas R.A ya ce Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Ku daidaita Sahunku domin daidaita sahu yana cikin cikar sallah (متفق عليه)

Daga Ibn Umar R.A lallai Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Ku tsayar da sahunku domin kuna yin sahune da Sahun mala'iku, ku daidaita tsakanin kafadunku, ku daidaita tsakaninku, ku hade tsakaninku, kada ku barwa Shaidan, duk wanda ya sadar da sahu, Allah zai sadar dashi, kuma wanda ya yake sahu Allah ya yanke sa (صححه الألباني).

Daga cikin neman samun falalar sahun farko, bai kamata mutum ya bar sahun farko ba, sai ya yi ƙoƙarin samun matsayinsa. Amma kada ya matsa wa wani ko ya cutar da shi saboda neman sahun farko, domin hakan na iya jefa shi cikin abin da bai dace ba.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments