Daga
Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng
Da
Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736
Shimfiɗa
Sanadiyyar albarkatun ƙasa da Allah Ya shimfiɗa a farfajiyar ƙasar Hausa, an sami al’ummomi da dama da suka dinga yin sintiri a sassa daban-daban na cikinta. Dangogin al’ummomin da suka cuɗanya da Hausawa har sunayensu suka yi tasiri a tsakaninsu sun haɗa da: Larabawa, Barebari da kuma Fulani, kamar yadda za a gani ɗaya bayan ɗaya.
Larabawa
Tun a wajen ƙarni na 12 Larabawa suka
soma zuwa ƙasar
Hausa domin harkar ciniki da ƙoƙarin yaɗa addinin Musulunci.
Misali, Shehu Abdurrahman Al-Magili, ya zo Kano a zamanin Sarkin Kano Muhammadu
Rumfa (1463–1499). Ya ziyarci Katsina. Sun koya wa Hausawa addinin Musulunci. Hasali ma suka zauna tare da su suka cuɗanya
da su. Wannan ya haifar da muhimman sauyi ta fuskar ilimi
da sunayen Hausawa da ma rayuwarsu ta
yau-da-kullum. Daga cikin sauyin da aka samu ta fuskar sunayen yanka kamar yadda addinin Musulunci ya shata. An kuma sami bayyanar sunayen laƙubban da suka danganci addinin,
kamar yadda Ibrahim,
(1978 p. 98-9).
Zuwan Musulunci Ƙasar Hausa da Wanzuwar Sababbin Sunaye
Addinin Musulunci ya shiga Nijeriya
ta Arewa a tsakanin ƙarni na
11 zuwa na 14 miladiyya. Masana kamar Ilor,
(1971) da Galadanci,
(1982) da Ibrahim,
(1982) da Gusau,
(1989 p. 31) sun bayyana cewa, Musulunci ya sadu da Daular Kanemin-Barno a ƙarni na goma
sha ɗaya
(11). Ana hasashen har ma
Mai Hummi Jilmi ɗan Selemma (1085-1097m)
shi ne ake jin wanda ya fara kaɓar Musulunci a cikin sarakunan Barno. Daga nan ne ma ya juya (sauya) wa kansa suna zuwa
Muhammadu.
A ƙasar Hausa kuwa, addinin Musulunci
ya shigo ne
a mabambantan lokuta. An soma karɓar Musulunci a Kano a cikin ƙarni na 14. Sarkin Kano Aliyu Yaji (1349 zuwa
1385m) shi ne sarki na farko da ya fara amincewa da Musulunci. Ya kuma yi ƙoƙarin yaɗa shi cikin ƙasarsa.
A Katsina kuwa, Musulunci ya samu shiga ne a zamanin Sarkin Katsina Muhammadu
Korau (1320 zuwa 1353m). Tun daga lokacin
aka cigaba da yaɗa shi
a garin, musamman zamanin
Sarkin Katsina Ibrahim Maje (1494 zuwa1520m). A lokacinsa ne Musulmi suka sami ranar shanya garinsu.
A Zazzau kuwa, an
sami rabauta da addinin Musulunci
ne a zamanin mulkin Sarkin Zazzau Muhammadu Rabo a daidai ƙarshen ƙarni na goma
sha biyar (15). Duk da kasancewar an sha kai da kawowa na rikicin gida da ya addabi ƙasar, an yi ƙoƙarin yaɗa addinin Musulunci gwargwadon hali.
Daga baya ma a wajen ƙarni na
19, Daular Zazzau ta zama babbar Cibiyar Koyar
da Ilimin Addinin Musulunci
da Lugga. Wannan ya wanzar
da samuwar almajirai masu neman ilimi suka dinga tururuwa
a cikin Zazzau domin ɗaukar karatu. Ƙasar
ta ɗaukaka
ta fannin ilimin nahawu da lugga, kamar yadda (Galadanci, 1982 p. 28-33) da
(Ibrahim, 1982 p. 29-35) da (Gusau, 1989 p. 31-32) suka bayyana.
A ƙasar Zamfara kuwa, ana kyautata zaton cewa, a cikin ƙarni na 17 suka karɓi Musulunci ta hannun tawagar Barebari Malamai da suka fito daga Barno. Kuma su ne suka taimaka wajen musuluntar da sarakunan Zamfara a cikin ƙarni na 17 ɗin, kamar yadda Nadama (1977 p. 185) ya nuna. Sarkin Zamfara Aliyu ɗan Daka ne Sarkin Zamfara na farko da ya fara karɓar Addinin Musulunci. Kuma shi ne ya soma gina masallatai a Birnin Zamfara. Hasali ma, duk garin da ya ci da yaƙi yakan gina masallaci, kamar yadda (Nadama, 1977 p. 185) da (Nalado, 1999 p. 16) suka nuna.
Manazarta
Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.