Ticker

6/recent/ticker-posts

Sunayen Hausawa Daga Musulunci

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Zuwan addinin Musulunci ya wanzar da samuwar sababbin sunaye a farfajiyar ƙasar Hausa. Wannan ya faru ne sakamakon yadda al’ummar Hausawa suka karɓi addinin Musuluncin da suka tsunduma gadan-gadan wajen koyon fannonin iliminsa. Hakan ya wanzar da samuwar mashahuran masana a cikin al’ummar, waɗanda suka taimaka wajen baza sunayen da suka dace al’ummar su raɗa wa ‘ya’yansu, tamkar yadda sunna ta bayyana.

Masanan sun yi ƙoƙari bayyana wa al’ummar muhimmancin saka wa abin da aka haifa sunayen da suke nuni ga bayar da wuya ga Allah Maɗaukakin Sarki. Irin waɗannan sunaye sun haɗa da:

a. Abdul-Alim

b. Abdul-Aziz

c. Abdul-Ganiyyu

d. Abdul-Hakam

e. Abdul-Jabbar

f. Abdul-Jalil

g. Abdul-Ƙadir

h. Abdul-Karim

i. Abdullahi

j. Abdul-Malik

k. Abdul-Muminu

l. Abdul-Wahhab

m. Abdur-Rahman

n. Abdur-Razaƙ

o. Abdus-Salam, da sauransu.

Haka sun yi ƙoƙarin bayyana wa al’ummar Hausa sunayen Annabawan Allah da ManzanninSa da ya kamata su rinƙa raɗa wa ‘ya’yansu maza. Daga cikin irin wannan sunayen sun haɗa da:

1. Adamu

2. Al-Yasa

3. Ayyub

4. Dawud

5. Dhul-Kifl

6. Harun

7. Hud

8. Ibrahim

9. Idris

10. Ilyas

11. Is’haƙ,

12. Isa

13. Isma’il

14. Lut

15. Muhammad

16. Musa

17. Nuh

18. Salih

19. Shith

20. Shu’aibu

21. Sulaiman

22. Uzair

23. Ya’ƙub

24. Yahya

25. Yunus.

26. Yusha’u

27. Yusuf

28. Zakariyya

Sun kuma kawo tsarin sunayen matan Annabi S. A. W. domin a yi amfani da su wajen raɗa wa ‘ya’ya mata da aka haifa. Daga cikin irin waɗannan sunayen akwai:

1. A’ishah

2. Hafsah

3. Jamilah

4. Juwairiya

5. Khadija

6. Maimunah

7. Mariyah

8. Raihanah

9. Ramlah

10. Safiyyah

11. Saudah

12. Umm Salamah

13. Zainab

Darussalam, (2004 p. 1-134) da Hareeri & Tahir, (2009 p. 79).

Sun kawo jerin sunayen ‘ya’yan Annabi S. A. W. duka domin al’ummar Musulmi su yi amfani da su wajen raɗa wa ‘ya’yansu. Sunayen kuwa su ne kamar haka:

1. Abdullahi

2. Fatimah

3. Ibrahim

4. Ƙasim

5. Ruƙayya

6. Umm Kulthum

7. Zainab

(Hareeri & Tahir, 2009 p. 79).

Ba nan kaɗai suka tsaya ba, sun kawo jerin sunayen waɗanda aka yi wa albishir da shiga Aljanna. Mutanen kuwa sun haɗa da:

1. Abdur-Rahman bin Auf

2. Abubakar Siddiƙ

3. Ali bin Abu Talib

4. Amir bin Abdullah bin Al-Jarrah

5. Sa’d bin Abu Waƙƙas

6. Sa’id bin Zaid

7. Talhah bin Ubaidullah

8. Umar bin Al-Khattab

9. Uthman bin Affan

10. Zubair bin Al-Awwam

(Hareeri & Tahir, 2009 p. 79).

Sun kuma kawo jerin sunayen waɗanda suka yi shahada a fagen yaƙin Badar. Shuhada’un kuwa su ne:

1. Aƙil bin Bukair bin Abd Yalil

2. Ammar bin Ziyad

3. Auf ko Audh bin ‘Afra’

4. Harithah bin Suraƙah

5. Mihja’ bin Salih

6. Mu’awwidh bin ‘Afra’

7. Mubasshshir bin Abdul Mundhir

8. Rafi’ bin Mu’alla

9. Sa’d bin Khaithamah Al-Ansari

10. Sa’d bin Mu’alla

11. Ubaidah bin Harith bin Muttalib

12. Umair bin Abd Umair

13. Umair bin Abu Waƙƙas

14. Umair bin Humam

15. Yazid bin Harith

(Hareeri & Tahir, 2009 p. 80)

Hasali ma sun yi ƙoƙarin bayyana sunayen waɗanda suka halarci yaƙin Badar daga ɓangaren Muhajuruna da kuma na Ansar.

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083

Post a Comment

0 Comments