Daga
Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng
Da
Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736
Daga cikin mata ma akwai Sahabbai da suka taka muhimmiyar rawa wajen yaɗa addinin Musulunci ta fuskoki da dama. Masana sun yi ƙoƙarin kawo jerin sunayensu domin al’ummar Hausawa da suka rabauta da karɓar Musulunci su raɗa wa ‘ya’yansu mata. Waɗannan mata Sahabbai su ne:
1. Asma’ bint Abu Bakr As-Siddiƙ
2. Asma’ bint Umais bin Ma’d
3. Asma’ bint Yazid
4. Fatimah bint Al-Khattab
5. Fatimah bint Ƙais
bin Khalid
6. Hamna bint Jahsh
7. Hind bint Utbah
8. Khansa’ bint Amr Tamadir
9. Khaulahbint Hakim
10. Rubayyi bint Mu’awwidh bin
Afra, da sauransu
(Hareeri & Tahir, 2009 p.
104)
Haka kuma, akwai sahabbai mata da
suka hardace Alƙur’ani
Maitsarki, waɗanda
suka haɗa da: A’ishah
Siddiƙah,
Hafsa, Umm Salamah, da kuma Umm Warƙah. Wasu Sahabban mata sun koyi wani ɓangare ne na Alƙur’anin. Irin waɗannan matan sun haɗa da:
1. Hind bint Usaid
2. Ra’itahbint Hayyan
3. Umm Hisham bint Harithah
4. Umm Sa’d bint Sa’d bin Ar-Rabi
(Hareeri & Tahir, 2009 p.
106-7).
Haka kuma, sun yi ƙoƙarin
kawo matan da suka mallaki ilimin tafsiri. Misali, A’ishah Siddiƙa, tana kuma ɗaya daga cikin waɗanda Allah Ya yi wa baiwa da sanin hadisan
Annabi S. A. W. Haka kuma, akwai ‘yar’uwarta Asma bint Abu Bakar, da Fatimah
bint Ƙais,
da Umm Atiyyah Al-Ansariyah, da Umm Hani Al-Ansariyyah da kuma Umm Salamah
(Hareeri & Tahir, 2009 p. 106-7).
Sahabbai mata kuwa da Allah Ya
hore musu fahimtar ilimin fiƙihu sun haɗa
da:
1. A’ishah Siddiƙa
2. Asma bint Abubakar
3. Fatimah Az-Zahra’
4. Fatimah bint Ƙais
5. Hafsah bint Umar
6. Haula bint Tuwait
7. Laila bint Ƙanif
8. Maimunah, da Safiyyah
9. Sahlah bint Suhail
10. Umm Ad-Darda’ Khairah bint
Abu Hadrad Al-Aslami
11. Umm Aiman
12. Umm Atiyyah
13. Umm Habibah
14. Umm Salalah
15. Umm Sharik
16. Zainab bint Abu Salamah
(Hareeri & Tahir, 2009 p,
107-8)
Akwai wasu keɓaɓɓantu fannonin da Allah Ya yi wa waɗannan mata Sahabbai baiwa
da su. Misali, Aishah Assaddiƙa ta shahara wajen naƙaltar
fasaha. Ita kuwa Ummu Salamah an yi mata baiwa da naƙaltar ciki da wajen Shara’a. Yayin da Asma’ bint Yazid bin Sakan aka
yi mata baiwa da fasahar magana. A ɓangaren
fassarar mafarki kuwa babu kamar Asma bint Umais bin Ma’ad (Hareeri &
Tahir, 2009 p. 108).
Shahararru a fannin magani da
aikin tiyata a tsakanin Sahabbai mata, babu kamar waɗannan:
1. Hamnah bint Jahsh
2. Laila Al-Ghifariyah
3. Mu’adhah Al-Ghifariyah
4. Rubayyi bint Mu’awwidh
5. Rufaidah Aslamiyyah (har ta
mallaki asibiti)
6. Umaimah bint Ƙais
7. Umm Atiyya
8. Umm Kabashah Al-Ƙuda’iyyah
9. Umm Muta Al-Aslamiyah
10. Umm Sulaim
(Hareeri & Tahir, 2009 p.
109).
An kawo waɗannan sunaye ne domin Hausawan da suka karɓi Musulunci su yi amfani da
su a madadin sunayen gargajiya da sukan raɗa
wa ‘ya’yansu. Saɓanin
a baya da sukan ba wa ‘ya’yansu laƙabi akan ƙudurin sunayen abubuwan da sukan yi
tasiri ga wanda aka ba.
Ta fuskar addinin Musulunci kuwa,
maƙasudin
amfani da suna shi ne, domin wanda aka ba sunan ya kasance mai halaye da ɗabi’u da tsoron Allah tare
da bin dokokin Mahalicci sau-da-kafa, tamkar mai shi na asali. Wannan ne Ya sa
akan sanya wa mutane sunayen Ma’iku, saboda su ba sa saɓa umarnin Ubangijinsu. Kodayake dai al’umomi
da dama sun fi raɗa wa
‘ya’yansu suna kamar:
1. Jibrilu
2. Rilwanu
3. Maliki
Sukan saka waɗannan sunaye ne kasancewar
su Mala’iku ne da sukan zo da abubuwan rahama ga al’umma. Don haka ne ake kwaɗayin mai bin sunan ya
kasance kamar yadda halayensu da ayyukansu suke. An guji sanya sunayen Mala’iku
kamar Azara’ilu da Raƙibi da Atidu, domin kauce wa tasirin ayyukansu ga mai sunan.
Hasali ma Hausawa sukan ce: “Suna linzami” domin sanin yadda yakan yi tasiri ga
mai shi.
Manazarta
Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.