Ticker

6/recent/ticker-posts

Sunayen Alkunya Bayan Zuwan Musulunci

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Zuwan addinin Musulunci a ƙasar Hausa ya wanzar da samuwar sababbin sunayen alkunya a tsakanin alummar Hausawa. Irin waɗannan sunayen sun ƙunshi waɗanda suke ishara da dangantaka ta jini, ko ta mulki ko ayyukkan da suka jiɓinci ibada da sauransu, kamar yadda za a gani ɗaya bayan ɗaya.

Dangantaka ta Jini

Yayin da Musulunci ya shigo ƙasar Hausa, ya tarar da alummar Hausawa ba sa ambaton haƙiƙanin sunayen iyayensu. Wannan ne ma ya sa akan ji ko Bamagujen ƙasar Hausa bai faɗar sunan mahaifinsa ko na surikinsa, sai dai ka ji sukan kira shi da Maigida da sauransu. Da Musulunciya zo sai ya ƙarfafa wannan alkunyar har aka samu kalmomin harshen Larabci da ake amfani da su, saboda irin tasirin da addinin ya yi a gare su. Irin wannan tasirin ne ya sa idan aka haifa wa mutum ɗa ko ‘ya, ya sanya mata ko masa sunan mahaifiya ko mahaifi yakan yi amfani da laƙubban alkunya wajen sakayawa. Misali:

a. Abba: Wanda aka raɗa wa sunan kakansa, al’ummar wannan gidan, saboda jin nauyin (kunyar) faɗar sunan, sukan kira shi da suna Abba, ko Babangida.

b. Ummi: Wadda aka raɗa wa sunan kakarta, al’ummar wannan gidan sukan riƙa ambaton ta da suna Ummi, saboda jin nauyin (kunyar) ambaton sunan domin girmamawa gare ta. Don haka sukan kira ta da suna Ummi.

Alkunya da ta Danganci Shugabanci

A ƙasar Hausa, alummar Hausawa, sukan ji nauyin faɗar (ambaton) sunan wanda Allah Ya shugabantar a kansu ta fuskar ɗaukar nauyin jan ragamar lamuran rayuwarsu ta yau-da-kullum. Wannan ne ya sa ba sa faɗin sunan shugabansu domin girmamawa gare shi. Kuma an ɗauki duk wanda yake ambaton sunan shugabansa na yanka a matsayin marar ta’ido (kunya). Ire-iren waɗannan sunayen sun haɗa da:

a. Alƙali: Wanda aka naɗa domin gudanar da shari’a tare da yanke hukunci a tsakanin masu jayayya a kan wani abu ko wata matsala, domin sasanta su ko tsawatarwa.

b. Hakimi: Wanda aka naɗa domin ya shugabanci al’ummar wata gunduma da take ƙarƙashin riƙon wata masarauta.

c. Ladan: Wanda ya zamanto yana kiran salla domin faɗakar da al’ummar Musulmi lokacin gudanar da ita ya yi.

d. Liman: Wanda ya kasance yana jagorancin al’umma wajen gudanar da sallolin farilla na yini da na Juma’a.

e. Malam: Wanda ya nemi ilimin addinin Musulunci, ya kuma mallake shi, har ya zamanto yana koyar da shi a tsakanin al’umma. Mace kuwa akan kira ta Malama.

f. Muhuti: Malami mai ba Alƙali shawara game da hukunci da ya dace a zartar.

g. Na’ibi: Wanda yakan wakilci liman wajen jagorancin salla a duk lokacin da wata lalura ta hana liman halartar masallacin.

h. Sarki: Wanda aka naɗa ya shugabanci al’ummar gari ko ƙasar da take tattare da garuruwa a ƙarƙashinta.

i. Sayyadi: Alkunya ce da ake yi wa kowane Musulmi domin girmamawa.

j. Waziri: Babban mai ba sarki shawara wajen gudanar da mulkin masarauta.

k. Yari: Wanda aka naɗa a matsayin shugaban da yake kula da gidan turu (kurkuku).

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083

Post a Comment

0 Comments