Idan aka zurfafa bincike za a tarar da cewa, kusan kowace al’umma da take raye a farfajiyar wannan sararin duniya ba ta rasa sunayen gargajiya da take amfani da su, saboda matuƙar muhimmancinsu ga rayuwarsu. Ire-iren waɗannan sunaye an gaje su ne tun daga kakannin-kakanni. Irin waɗannan sunaye sun sha bamban daga wannan ƙabila zuwa waccan, kamar yadda al’adu da ɗabi’u da launin fata da abinci da yanayin sutura da harsuna da tsagen fuska da ita kanta kamannun fuskoki suka bambanta. Haka sunayen gargajiya suka sha bamban a tsakanin wannan al’umma zuwa waccan. Hasali ma za a tarar cewa, kowace al’umma tana da nata al’adu da ta shahara da su, haka lamarin ya kasance ta fuskar sunayen gargajiya.
A gargajiyance za a tarar cewa, duk sunan da aka kira wani da
shi, idan aka bi diddigi sosai
za a ga yana ƙunshe
da wata ma’ana ta musamman da dalilin da ya sa aka sanya wa mutum ake kuma kiran sa da
shi. Misali, a zamanin jahiliyya, Larabawa sukan sanya wa ‘ya’yansu munanan sunaye, kamar KALBU
(kare) da DARAR (cuta) da ZI”IBU (kura). Yayin da sukan sa wa bayinsu kyawawan sunaye, kamar: MARZUƘ (abin arzutawa), kamar yadda Sufi, (1993 p. 97)ya kawo. Hadisai
da dama sun kawo ire-iren waɗannan sunaye, kamar: ASIAHعاصية (Mai Zunubi) da AL-‘AASالعاص (Mai Fitina) da GHURAB غراب (Hankaka) da SHIHABشهاب (Harshen Wuta) da HARB حرب(Yaƙi), Muslim: 2139 da
Tirmidhi: 2828, suka kawo shi.
Sun yi haka ne domin ‘ya’yan nasu su sami tasirin abubuwan nan da aka ba su
sunayen su, ta yadda za su kasance masu aiki da halayya da ɗabi’u abin tsoro. Kamar
yadda abubuwan da suka karɓi sunayen nasu suke a tsakanin al’umma, kuma a fagen fama
(yaƙi) su zama gwarzaye. Yayin da bayinsu sukan zama masu sanyaya zukata da biyayya ga umarnin iyayen gidansu.
Hadisai da dama sun nuna Annabi
S. A. W. ya sami Larabawa suna amfani
da irin waɗannan sunaye. Yayin ba wa abin da aka haifa suna, sukan yi la’akari da nau’in halittar da ba kasafai ɗan’adam yakan fuskance su ya wanye lafiya ba. Wannan ne ya sa suke ba ‘ya’yansu irin sunayen abubuwan domin su yi tasiri
ga rayuwarsu, musamman
ma idan aka yi la’akari da yanayin wancan zamani
da suke tattare da yaƙe-yaƙe a tsakanin ƙabilun Larabawa. Zuwan addinin Musulunci
bai hana Larawa sanya wa ‘ya’yansu irin waɗannan sunaye ba, kamar:
Jad. na 1: Waɗansu Sunayen Larabawa da Ma’anoninsu
|
|
Suna |
Ma’ana |
|
1. |
Asad |
Zaki |
|
2. |
Fahad |
Dare |
|
3. |
Ghazala |
Barewa |
|
4. |
Hamamatu |
Tantabara |
|
5. |
Hamman |
Masai/Banɗaki |
|
6. |
Khatam |
Zobe |
|
7. |
Laila |
Dare |
|
8. |
Mal’una |
Tsinanniya |
|
9. |
Ni’aal |
Takalmi |
|
10. |
Saddam |
Mairushewa |
A babukan da ke biye, za a mayar da hankali wajen kawo yadda lamarin sunaye ya kasance tsakanin waɗansu al’ummu makusanta ga Hausawa.
Manazarta
Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.