Ticker

6/recent/ticker-posts

Samar Da Sunayen Mutane Daga Sunayen Dabbobi Da Tsuntsaye Da Kwari Da Tsirrai

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Samar Da Sunaye Daga Dabbobi

A wasu lokutan, sakamakon mu’amalar da Bahaushe ke yi da dabbobi ne ya sa yakan ɗauki sunayen wasu daga cikinsu ya sa wa ‘ya’yansa. Yakan yi haka ne ko don saboda jaruntakarsu, ko don faɗan da ke gare su, ko kuma domin lalacin su. Yakan yi haka ne domin sunayen su yi tasiri a rayuwar ‘ya’yan nasa. Misalai daga cikin irin sunayen su ne:

Jad. na 2: Sunayen Hausawa Daga Dabbobi

 

Suna

Dalilin Sakawa

1.       

Zaki

Saboda ƙarfinsa ake sa wa namiji sunan zaki

2.       

Giwa

Saboda ƙarfinta ake sa wa mace suna giwa

3.       

Doki

Saboda ƙarfinsa ake sa wa namiji suna doki

4.       

Kura

Saboda zalunci da tsoronta ake sawa mace suna kura

5.       

Dila

Saboda wayonsa ake sa wa namiji suna dila

6.       

Gwamki

Saboda ƙarfinsa ake sa wa namiji suna gwamki

 

Samar da Sunaye Daga Tsuntsaye

Bahaushe bai taƙaita kansa ga sanya wa ‘ya’yansa sunayen dabbobi ba, har ma yakan ba su na tsuntsaye. Yakan bayar da sunayen ne yayin da ‘ya’yan suka kai wani munzili suka rinƙa aiwatar da wasu halaye. Misali:

Jad. na 3: Samar da Sunayen Hausawa Daga Tsuntsaye

 

Suna

Dalilin Sakawa

1.       

Kaza

Ya kankira mace “kaza” saboda yawan haihuwa.

2.       

Kuti

Yakan kira mace “kuti” (agwagwa) saboda yawan tsabta.

3.       

Maiki

Akan sanya wa mutum sunan ne domin ya kasance da siga irin ta wannan

Tsuntsu wanda ya kasance mai bajinta da hangen nesa da jin ƙanshin wani abu daga nisan zango da tashi sama can ƙololiya da nisa.

4.       

Zabuwa

Akan kira mace “zabuwa” saboda ta kasance mai yawan tsabta da kwalliya tamkar yadda sifar zabuwa take.

5.       

Zakara

Yakan kira namiji “zakara” saboda ya fiye son matarsa

6.       

Suda

Yakan kira mace “suda” saboda ta fiye surutu.

Samar da Sunaye Daga Ƙwari

Bahaushe kan sa wa ‘ya’yansa sunayen ƙwari, ta la’akari da halayen wanda aka ba wa. Wani zubin kuma yakan bayar da sunan ne da nufin laƙabin ya yi tasiri ga mai amsa shi. Misali:

a. Zuma akan ba da sunan ne ga mutum mai kyauta da faɗa. Wasu lokutan akan ba abin haihuwa sunan ne domin ya kasance tamkar zuma yayin da ya girma. Wato ya zama mai daɗaɗa wa al’umma tare da rashin ɗaukar reni kamar zuma. Ya zama mai son haɗin kai da sauran al’umma don samar da cigaba da riga-kafin aukuwar annobar ƙare dangi (East da Imam, 1986 p. 293).

b. Ƙuda akan ba da sunan ne ga abin haihuwa domin ya kasance mai kaifin gani da hangen nesa da kazar-kazar da rashin kasala da taka-tsantsan wajen gudanar da kowane irin lamarin rayuwar duniya (East da Imam, 1986 p. 261-262). 

Samar da Sunaye Daga Tsirrai

Su ma tsirai Bahaushe bai ƙyale su ba, saboda muhimmancinsu ga rayuwarsa. Wannan ne ya sa ya samar wa ‘ya’yansa da garuruwansa sunaye daga gare su. Misali:

Jad. na 4: Samar da Sunayen Hausawa Daga Tsirrai

 

Suna

Tushe

1.       

Kalgo

Sunan gari ne

2.       

Sabara

Sunan gari ne

3.       

Dogon Kaɗe

Sunan gari ne

4.       

Tsamiya

Sunan mutum ne

5.       

‘Yartsamiya

Sunan gari ne

6.       

‘Yarkuka

Sunan gari ne

7.       

Gamji

Sunan gari ne, kuma ana kiran mutum Gamji

8.       

Sure

Sunan mutum ne

9.       

Kurna

Sunan mutum ne

10.   

Tumfafiya

Sunan mutum ne

 Samar da Sunaye Daga Sararin Samaniya

Hausawa kan ba ‘ya’yansu sunayen abubuwan da ke sararin samaniya, saboda yadda suka ɗauke ta da muhimmanci a rayuwarsu ta yau-da-kullum. Domin ta nan ne suke fahimtar lokutan yini da makamantan haka. Misalan irin waɗannan sunaye sun haɗa da: Hadari, Walƙiya, Zara da sauransu. 

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083

Post a Comment

0 Comments