Daga
Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng
Da
Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736
Bahaushe kan ba abin da aka haifa masa suna ta la’akari da lokacin da haihuwar ta auku tun daga wayewar gari har zuwa tsakiyar dare. Sakamakon haka ne ya haifar da samuwar sunaye kamar:
a. Dare: Wanda aka haifa da
tsakiyar dare ko da daddare, wasu kan kira shi Ɗandare. A wasu wuraren kamar Sifawa sukan
ce Dari, wasu su ce Adare, Baƙo, ko Baƙondi, ko Baƙon-dare, mace kuwa ana kiran ta da sunaye
kamar haka: Maidare, ko Baƙuwa.
b. Nahantsi: Wanda aka haifa da
hantsi, wato lokacin da rana ta fito sosai kafin ta kai tsaka. A wasu garuruwan
kai-tsaye suke kiransa Hantsi.
c. Ranau: Wanda aka haifa da
rana. Mace kuwa ana kiran ta Tarana.
d. Sammako: Wanda aka haifa tun da sassafe, kafin fitowar rana.
Manazarta
Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.