Daga
Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng
Da
Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736
Wasu sunayen Hausawa na iya kasancewa waɗanda aka alaƙanta su da wani zamani da aka haifi abin haihuwar a cikinsa. Wannan ne dalilin da mai sunan kan karɓa laƙabin. Irin waɗannan sunaye sukan danganci jinsin maza da na mata. Misali:
a. Ɗankaka: Shi ne wanda aka haifa a lokacin
da ake girbin (cire) amfanin gona. A
wasu wurare akan kira shi Ƙosau. Mace kuwa akan kira ta da laƙabin Kaka, ko Nakaka,
mace kuwa a kira ta Kakale. A wasu sassan ƙasar Hausa akan kira namiji da laƙabin
Yalwa, haka ita ma mace takan karɓa
wannan sunan.
b. Ganau: Shi ne wanda aka haifa
a lokacin da sabon wata ya fita (tsaya). A wasu yankunan ƙasar
Hausa akan kira shi da laƙabin Magawata.
c. Sallau: Shi ne wanda aka haifa
a lokacin biki.
d. Shanono: Shi ne wanda aka haifa a lokacin da saniya ta haihu.
Manazarta
Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.