Ticker

6/recent/ticker-posts

Samar Da Suna Ta La’akar Da Yanayin Da Abin Haihuwa Ya Sami Kansa

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Bahaushe kan yi la’akari da halin da jinjiri ya tsinci kansa a tsakanin iyalinsa bayan an haife shi, na rashin uwa ko uba, wajen sanya wa jinjirin suna. A sakamakon wannan falsafar ce aka samar da sunayen kamar haka:

a. Abaici: Wanda aka haifa bayan rasuwar mahaifinsa. A wasu sassan garuruwan ƙasar Hausa ana kiransa da sunaye nau’i-nau’i da suka haɗa da: Mayau, ko Maida, ko Audi ko Baita ko Baitu. A ƙasar Ɓurmi (Bakura) akan ce, Kamaye. Mace kuwa ana kiran ta Baito. A wasu sassan kuwa sunaye kamar: Baita, da Baitu ko Audi, sun kasance na tarayya, wato ana kiran namiji da mace da su, (CNHN, 2006 p. 320)

b. Ɗanmaraya: Wanda iyayensa biyu suka rasu tun yana yaro ƙarami.

c. Tallafi: Wanda mahahaifiyarsa ta rasu (mutu) ta bari bayan an haife shi, tun yana jinjiri. Mace kuwa ana kiran ta Talle. Wasu ƙasashen kuwa Talle yana matsayin suna na tarayya, musamman a ƙasar Faki da ke cikin Lardin Zazzau.

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083 

Post a Comment

0 Comments