Ticker

6/recent/ticker-posts

Samar Da Suna Ta La’akar Da Sunaye ta Fuskar Saɓanin Zamantakewar Auratayya

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Al’ummar Hausawa sukan sa wa ‘ya’yan da aka haifa musu sunaye ta kula da wata rashin jituwa da ta auku da kan haddasa rabuwar aure idan ba a kai zuciya nesa ba. Wasu lokutan kuma shigar juna biyu kan zama sanadin sasantawa. Wani zubin kuwa sai an haihu ɗin ne akan sasanta. La’akari da irin wannan halayyar ne Bahaushe ya tanadi sunaye da suke nuni ga yadda yanayin yake kafin ko bayan an haifi abin haihuwar. Wannan ne ya samar da sunaye kamar:

a. Dawai: Yaron da aka saki mahaifiyarsa da ciki, sai ta haife shi bayan ta yi wani aure.

b. Gwanda: Laƙabin da akan yi wa wanda shigar cikinsa ya hana mutuwar auren mahaifiyarsa. A wasu sassan garuruwan ƙasar Hausa akan kira shi da Sadau.

c. Tagudu: Wadda aka haifa a lokacin da mahaifiyarta ta yi yaji (tashi)wato fushi ta bar gidan miji, a cikin wannan yanayin sai aka haife ta.

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083

Post a Comment

0 Comments