Ticker

6/recent/ticker-posts

Lakubban Ranakun Mako a Matsayin Sunayen Hausawa

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Bayyanar addinin Musulunci a farfajiyar ƙasar Hausa, shi ya kawo wanzuwar sunayen ranakun mako, waɗanda da can babu. Kafin zuwan Musulunci, Hausawa sukan yi amfani da lokutan da kasuwar garuruwa ne ke ci a wajen lissafinsu ko yi wa abin haihuwa laƙabi. Misali, wanda aka haifa ranar Talata, sai su kira shi Ɗanmafara. Idan kuma lissafin ranaku ne, sai a dinga faɗar ranar kasuwar Katsina, ko Daura, ko Kiyawa, ko Zariya, ko kuma Kano da sauransu. Samuwar sunayen mako a ƙasar Hausa, ya samar da wani sabon tsarin lissafin ranakun mako ya kuma ba Bahaushe wata dama ta yi wa yaron ko yarinyar da aka haifa masa laƙabi da suna na ranar haihuwarsa/ta. Irin waɗannan sunayen akwai waɗanda suka jiɓinci maza da kuma mata, kamar yadda za a gani ɗaya bayan ɗaya:

Jad. na 10: Misalan Laƙubban Ranakun Mako a Sunayen Hausawa

Sunan Rana

Laƙabin Namiji

Laƙabin Mace

Juma’a

A Hausar Gabas wanda aka haifa ranar Juma’a akan yi masa laƙabi da Jumare, wasu su ce Jume ko Najuma. Yayin da a Hausar Yamma kuwa sukan kira shi Ɗanjuma ko Ɗanjummai.

A Hausar Gabas wadda aka haifa ranar Juma’a akan yi mata laƙabi da Jummai, ko Juma ko Tajume. Yayin da a Hausar Yamma kuwa sukan kira ta Jimmai ko Jumma.

Asabar

Wanda aka haifa ranar Asabar akan kira shi Ɗan’asabe.

Wadda aka haifa ranar Asabar a Hausar Gabas akan kira ta Asabe. A Hausar Yamma kuwa sukan kira ta Assibi ko Asshibi ko Shibo, musamman a Masarautar Maradun da ke Jahar Zamfara.

Lahadi

Wanda aka haifa ranar Lahadi, akan kira shi Ɗanladi. A gundumar Katsina da wasu da ke makwabtaka da ita sukan kira shi Lado ko Nalado.

Wadda aka haifa ranar Lahadi, a Hausar Gabas akan kira ta Ladi ko Ladiyo ko Ladingo, Lando musamman a karin harshen Zazzaganci. Yayin da a Hausar Yamma sukan kira ta Ladidi.

Litinin

Wanda aka haifa ranar Litinin a Hausar Gabas akan kira shi Ɗanliti ko Ɗantine. A Hausar Yamma kuwa sukan kira shi Altine ko Alti. Ana kuma kiransa Tanimu

Wadda aka haifa ranarLitinin, a Hausar Gabas akan kira ta Atine. A Hausar Yamma kuwa su kira ta Tanin ko Tantano.

Talata

Wanda aka haifa ranar Talata a Hausar Gabas da wasu garuruwan akan kira shi Ɗantala ko Ɗantalatu ko Bature. A yankin Zamfara da maƙwabtansu akan kira shi Ɗanmafara. Haka akan kira shi Batula, kamar yadda Abubakar (2015 p. 46) ya bayyana.

Wadda aka haifa ranar Talata akan kira ta Talatu ko Talatuwa ko Tala. Haka akan kira ta da Lantana.

Laraba

Wanda aka haifa ranar Laraba akan kira shi Bala, ko Balarabe ko Ɗanlarai.

Wadda aka haifa ranar Laraba akan kira ta Balaraba ko Laraba ko Larai. A Masarautar Bakura da wasu yankuna sukan kira ta Laraiba.

Alhamis

Wanda aka haifa ranar Alhamis akan kira shi Ɗanlami ko Nalami.

Wadda aka haifa ranar Alhamis, a Hausar Gabas akan kira ta Lami. Yayin da a Hausar Zazzau sukan kira ta Laminde. A Hausar Yamma kuwa sukan kira ta Lamiso. A masarautar Bakura da Mafarfari kuwa su kira ta Lamso.

Daɗin daɗawa, bayan irin waɗannan sunayen da aka samar ta la’akari da ranakun da aka yi haihuwar. Akwai wasu na yanka da ake sa wa abin haihuwa da suke da alaƙa da ranar da aka haihu saboda wasu dalilai na ma’ana. Misali, ɗan da aka haifa ranar Juma’a akan sanya masa suna Adamu (Adam) in mace ce a sa mata suna Hauwa’u (Eve), saboda Juma’a ce ranar farko ta mako.

Yayin da aka haifi yarinya ranar Talata, akan yi mata laƙabi da suna Baturiya. Wannan na nuni da cewa, ita mai arziki ce kamar yarinya Baturiya. An ɗora (aza) wannan ne bisa ma’aunin kalmar talata wadda take ƙunshe da ma’anar dubu uku na kuɗin wuri (3000) waɗanda a zamanin da kuɗi ne masu yawa, kamar yadda Newman (2000 p. 345) ya nuna. 

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083

Post a Comment

0 Comments