𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Malam dan Allah wane irin ƙunci ne da azaba ke tattare da ƙabari?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Ƙuncin kabari a
addinin Musulunci ya ƙunshi abubuwa kamar matsawar ƙasa, tambayoyi masu
tsanani daga mala'iku MUNKAR da NAKIR, da kuma azaba ga masu laifi.
Duk wani nau'i na ƙunci akwaishi aƙabari sedai kawai
azabar lahira tafi tsanani ne, sunzo a ayoyi da hadisai daban-daban bari inkawo
miki misalin, Allah S.W yace:
اَلنَّارُ يُعۡرَضُوۡنَ عَلَيۡهَا غُدُوًّا وَّعَشِيًّا ۚ
وَيَوۡمَ تَقُوۡمُ السَّاعَةُ اَدۡخِلُوۡۤا اٰلَ فِرۡعَوۡنَ اَشَدَّ الۡعَذَابِ
"Wuta za a dinga
sanyasu akanta yini da dare (a cikin ƙabari) kuma ranan
tashin Alƙiyama za ace kushigarda iyalan fir'auna mafi tsananin
azaba" (suratu gafir ayata 46).
Ibn kathir yace
acikin tafsirinshi "haka Ahlissunnah suka yarda duk wanda beyin aiki na ƙwarai za a yimishi
irin wannan azabar tun a ƙabari" 4/82.
An karbo daga barra'a
dan azib R.A yace; "munfita tare da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) zuwa jana'izan wani mutun daga mutanen madina se mukakai maƙabarta, alokacinda za
a yimishi ƙabarin lahadi ne se Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam)
ya zauna se muka zauna agefenshi, kuma kaman kace akwai tsuntsuwa akawunan mu,
kuma ahannunshi akwai sanda yana caccaka ƙasa da ita se yadaga
kansa sama yace; Kunemi tsari Allah daga azaban ƙabari, kunemi tsarin
Allah daga azaban ƙabari sau 2 ko sau 3 yana maimaitawa sannan sai ya fadi
sannan se ya fadi yanda ake ansan ran mumini dakuma ni'iman da mumini yake samu
acikin ƙabari. Sannan yace ammashi kafiri inyazo rabuwa da duniya
kuma yazo fuskantan lahira, wasu mala'iku zasu sakkomishi masu baƙaƙen fuskoki taredasu
akwai jaka sesu zauna tare da shhi iya
ganin idonshi har sai mala'ikan mutuwa yazo seya zauna agun kanshi se yace: Ke
wannan Ran gurbatacciya, kifita zuwa tsinuwan Allah da fushin Allah, seta
bubbugo daga jikinshi se ya fizgota kaman yanda ake fizgo tsinken tsire daga
tsire seya dauketa, inya dauketa baya barinta ahannunshi dede da ƙiftawan ido harse ya
sanyata acikin kwandonnan, kuma mummunan wari irin na mushe wanda aka tsinta
abanƙasa yana fitowa daga cikinta, se suyi sama da ita, Aduk
lokacin da suka haɗu da wasu taron
Mala'iku sesu tambayesu: wannan wata raice gurbatacciya haka? Sesuce ai wannan
wane ne ɗan wane suna kiranshi
da mummunan sunan da suke kirnshi aduniya, har se ankawoshi zuwa sama ta farko,
se anemi abudemishi iya se aƙi yarda abudemishi saman, sannan anan
se Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya karanto ayan cikin suratu A'araf
ayata 40 [wacce take bada labarin hakan].
اِنَّ
الَّذِيۡنَ كَذَّبُوۡا بِاٰيٰتِنَا وَاسۡتَكۡبَرُوۡا عَنۡهَا لَا تُفَتَّحُ لَهُمۡ
اَبۡوَابُ السَّمَآءِ وَلَا يَدۡخُلُوۡنَ الۡجَـنَّةَ حَتّٰى يَلِجَ الۡجَمَلُ
فِىۡ سَمِّ الۡخِيَاطِ ؕ وَكَذٰلِكَ نَجۡزِى الۡمُجۡرِمِيۡنَ
"Lalle ne waɗanda suka ƙaryatã
game da ãyõyinMu, kuma suka yi
girman kai daga barinsu, bã zã
a bubbuɗe musu kõfõfin sama
ba, kuma bã su shiga Aljanna sai raƙumi ya shiga kofar
allũra, kuma kamar wannan ne Muke sãka
wa mãsu laifi. (Surah: Al-A'raaf, Ayat: 40)
Sannan se Allah SW
yace kurubuta sunanshi acikin sijjin (littafin sunayen 'yan wuta) acikin sama
ta ƙasa,
se ajeho Ran nashi, anan se Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya karanto aya
ta 30 cikin suratu Hajj:
ذٰلِكَ
وَمَنۡ يُّعَظِّمۡ حُرُمٰتِ اللّٰهِ فَهُوَ خَيۡرٌ لَّهٗ عِنۡدَ رَبِّهٖؕ
وَاُحِلَّتۡ لَـكُمُ الۡاَنۡعَامُ اِلَّا مَا يُتۡلٰى عَلَيۡكُمۡ فَاجۡتَنِبُوا
الرِّجۡسَ مِنَ الۡاَوۡثَانِ وَاجۡتَنِبُوۡا قَوۡلَ الزُّوۡرِۙ
"Wancan ne. Kuma
wanda ya girmama hukunce-hukuncen Allah to shĩ ne mafĩfĩci a gare shi, a wurin
Ubangijinsa. Kuma an halatta muku dabbõbin ni'ima fãce abin da ake karantãwa a
kanku. Sabõda haka ku nĩsanci ƙazanta daga gumãka
kuma ku nĩsanci ƙazanta daga shaidar
zur. (Surah: Al-Hajj, Ayat: 30).
Se Ran nashi ta dawo
jikinshi. Se mala'iku biyu suzomishi suzauna agefenshi sesucemashi; Waye
Ubangijinka ? Se yace; Hahh Hahh! Bansaniba, Meye addinika? Se yace: Hahh Hahh!
bansaniba, Se sucemishi me kakecewa akan wannan mutumin da aka turomuku (wato
Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam)? Se yace: Hahh Hahh! Bansaniba.
(sahabbai suka tambayi Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa: Aiko Mumini
inyaga Mala'ika tare da shhi baze iya
ansa wannan tambayarba? Se Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) yajawomusu ayata
27 na Suratu Ibrahim wacce take nuna Allah ze tabbatar da mumini ya Ansasu
dedai:
يُثَبِّتُ
اللّٰهُ الَّذِيۡنَ اٰمَنُوۡا بِالۡقَوۡلِ الثَّابِتِ فِى الۡحَيٰوةِ الدُّنۡيَا
وَفِى الۡاٰخِرَةِ ۚ وَيُضِلُّ اللّٰهُ الظّٰلِمِيۡنَ ۙ وَيَفۡعَلُ اللّٰهُ مَا
يَشَآءُ
"Allah Yanã
tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni da
magana tabbatacciya a cikin rãyuwar dũniya, da cikin Lãhira, Kuma Allah Yanã ɓatar da azzãlumai,
kuma Allah Yanã aikata abin da Yake so. (Surah: Ibrahim, Ayat: 27).
Se wani me kira ya
kira cewa Ƙarya yayi danhaka kuyimishi shimfida na Wuta, kuma ku
budemishi wata ƙofa zuwa wuta, se zafinta da ƙunanta ta dinga
zuwamishi kuma se ƙabarinshi ya haɗe dashi har sai ƙashin haƙarƙarishi ya haɗu da juna.
Daganan se Aturomishi
da wani makaho kuma kurma yana riƙe da guduman Ƙarfe wanda ake fasa
dutsedashi wanda inda za a duke dutsen dashi da dutsen se yazama Ƙasa, se adukeshi da
wannan Gudumar duk duniya kowwa zeji ƙara amma banda mutun
da Aljani, se yazama turbaya se aƙara dawomishi da Rai,
se wani mutun me Mummunan fiska me mummunan kaya sannan me mummunan wari
yazomishi se yace: Inamaka Bishara da abinda ze saka Ƙunci yaune Ranan da
akayimaka Alƙawari, se yace kai waye domin fiskanka fiskace wacce
zatazo da sharri? Se yace ai nine aikinka Gurbatacce (wanda kayi aduniya), se
yace: Ya Allah karka kawo ranan tashin Alƙiyama. Ya Allah karka
kawo Ranan tashin Alƙiyama. Ahmad ya ruwaito 17803, Abu daud 4753. Muhaddith
ya ingantashi acikin ahkamul Jana'iz shafi na 156.
Annabi (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya wuce ta kusa da kaburbura biyu, sai yace: "Lalle ana
azabtar da su, kuma ba a azabtar da su saboda wani babban abu ba (a tunaninku):
Ɗaya
daga cikinsu ya kasance ba ya kiyaye kansa daga fitsari (ya na shafa kazanta),
shi kuma dayan ya kasance yana yawo da annamimanci (gulma tsakanin
mutane)." (Sahih al-Bukhari da Muslim).
A Wani Hadiain Annabi
(Sallallahu Alaihi Wasallam) Yace; annunamai mutane hudu wanda akemusu azaba aƙabari;
1. Wanda ake karo da
dutse dakansa yana rugurgujewa yana ihu harzuwa ranan tashin Alƙiyama. Wanna
mahaddacin Ƙur'anine se ya watsardashi kuma mara zuwa Sallan farilla.
2. Me yagan
kumatunshi, Hancinshi da idanunshi harzuwa ƙeya da Lauje. Wannan
kuma me ƙaryane.
3. Wanda aka tubesu
tsirara aka sasu awata tukunya kaman tandan waina, ana yimusu azaba suna ihu.
Wannan kuma masu zina Mata da Maza.
4. Wanda akasashi
acikin wani abu Ja kaman jini, ana jifanshi da dutse yana shigewa bakinshi
harzuwa cikinshi wannan kuma me cin ribane. Bukhari 1386, fathul Bari 12/445.
Sayyidina Usman bin
Affan (RA) idan ya tsaya a kusa da kabari ya kan yi kuka sosai har sai gemunsa
ya jike da hawaye, idan aka tambaye shi sai yace naji Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) yace: "Lalle ne kabari shi ne mataki na farko na gidan
Lahira. Idan mutum ya tsira a cikinsa, abin da ke bayansa ya fi sauƙi; idan kuma bai
tsira a cikinsa ba, to abin da ke bayansa ya fi tsanani." Sannan ya ce:
"Ban taba ganin wani abin tsoro ba wanda ya fi kabari muni."
(Tirmidhi da Ibn Majah).
Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kasance yana koyar da neman tsari daga kuncin
da azabar kabari a karshen kowace Sallah kafin sallama:
اللَّهُمَّ
إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنْ عَذَابِ الْقَبْرِ، وَمِنْ عَذَابِ جَهَنَّمَ، وَمِنْ
فِتْنَةِ الْمَحْيَا وَالْمَمَاتِ
Ya Allah! Lallai ni
ina neman tsarinka daga azabar kabari, da azabar wuta ta Jahannama, da fitinar
rayuwa da mutuwa.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Zaku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.