Ticker

6/recent/ticker-posts

Shin Zuwa Malamin Boka Shirka Ce?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum Dan Allah mlm inada tmby wani mutume ne a kauye yake bada taimako amma kafin kafadi tambaya yafada ma kuma idan yabada magani yanayi shine nake so najiya shin zuwa wurinsa shirka ce ko ya abin yake ngd

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Waalaikumussalamu. Baiwar Allah, Bai halatta kije neman magani gurinsa ba Domin wannan malamin boka ne Kuma kafirine tantagarya Kuma zuwa wajensa shirka ne Domin dukkan wanda zai fada maka abin da yake tafe dakai tun kafin ka fada masa Babu shakka boka ne Saboda haka haramun ne zuwa gurin irin wadannan masu bada maganin Mutukar kika je kika tambayeshi wani abu to Allah baze karbi sallarki ta kwana arba'in 40 ba. Idan kuwa kika gasgata maganar sa to kin kafircewa Abun da Annabin (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya zo mana dashi.

Saboda haka shari'a bata hana neman magani ba domin neman magani halal ne kuma musulunci ya tsara hanyar da ake bi a nemi magani Saboda haka waccan hanyar batacciyar hanya ce kuma haramtacciyar hanyar neman magani ce Kada ki rudu da cewa maganinsa yanayi kawai ki tsarkake niyya ki yadda cewa Allah shine ke warkar da cuta tare da neman taimakon sa ki garzaya cibiyoyin masu bada magani na musulunci ku nemi magani idan ma cutar ta shafi jinnu zasuyi muku magani kuma su kori shaidanu da Ayoyin Al'ƙurani ta hanyar ruƙiyya da addu'o'in da suka tabbata a sunnah.

Sannan kuma babu lefi kuyi mana bayanin cutar ko akwai wani taimakon da za a iya baku na addu'o'i daga Al'ƙurani da sunnah.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Zaku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam   

Post a Comment

0 Comments