𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU. Mallam Khamis barka da yamma, da fatan ka yini lafiya. Ya aiki, ya iyalai? Muna rokon Allah Ya karawa rayuwa, Ilimi da iyalai albarka, ameen!
Mallam don Allah
inada wata tambaya ne wanda na keso a warware min: "Da farko dai gaskiya
ina fama da matsanancin ciwo na wasiwasi, ta yanda duk wani abu da nayi na
Ibadah sai naga kamar banyi daidai ba, ko kuma bai inganta ba. Haka ina yawan
samun wasiwasi da kokonto a dukkan wasu aiyukana na Ibadah kamar su tsarki,
Alwala da kuma sallah. Idan nayi sai naga kamar baiyi ba, ko Alwalar ya karye,
ko akwai kuskure a ciki.
Toh inata iya
kokarina domin naga naki biyewa duk wasu wasiwasin a dukkan abinda zai fadamin
dangane da Ibadah ta, toh sai gashi yau kuma ya sake billomin da wani abu mai
sarkakiya.
Mallam dazu ne da
nayi Alwala domin yin Sallah, toh a yayin chanja Tufafina, sai naji kamar
hannuna ta Shafa/taɓa azzakarina cikin
kuskure, amman banda tabbaci. (Nafi ganin kamar saman azzakarin wajen kasan
mara ya taɓa cikin kuskure yayin
chanja Kaya). Toh don gudun matsalata ta wasiwasi, sai na tafi nayi sallah ta
tunda bawai na tabbatar azzakarin hannuna ya Shafa ba, ina tunanin kamar idan
nayi sallar na idar zai tafi ya kyaleni.
Toh bayan na idar da
Sallar kuma, sai wasiwasin ya dawomin sosai akan cewa nayi sallah babu Alwala,
cewa ai tunda hannuna ya shafa azzakarina yayin chanja Kaya, toh Alwala ta ta
riga ta karye. Kuma ni maganar gaskiya shi ne banda tabbaci akan cewa
azzakarina hannuna ya shafa yayin chanja kayan, ko kuma kasan mara wajen gashi
ta taɓa, shi ne nace bari
na rubuta tambayar, domin neman fatawa wajen warware wannan matsalar kokonton
tawa.. Nagode Mallam!
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh
Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam yace: "idan ɗayanku ya tayar da sallah, toh sheɗan zaizo yana masa
waswasi acikin sallar, ko ya nuna masa cewa alwalarsa ta karye don ya ɓata maka sallah. Har
wani lokacin ma ka kanji iska a tsakanin duburarka kamar kayi butu. Toh Annabi
(Sallallahu Alaihi Wasallam) Yace idan kaji haka kada ka katse sallarka har sai
kaji doyin tusar ko kaji sautin fitar tusar.
Sannan sahabbai sun
taɓa samun Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam suka ce dashi "mutum ne yana sallah zai dinga
ji ana raya masa cewa 'yayi butu (tusa)' yaji ana ce masa alwalarka ta karye a
zuciyarsa. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yace idan ɗayan ku yaji haka toh
yace KARYA NE!
Hadisi ya tabbata
daga Usman ɗan Abul Ási (Allah ya
qara masa yarda) cewa: Shi Usman ɗin ya zo wurin Manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) sai ya ce: Ya Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) lallai
shaiɗan ya shiga tsakanina
da sallata, yana rikita mini karatun sallata, sai Manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) ya ce: "Wannan wani shaiɗani ne da ake kiransa da KHANZAB, duk
lokacin da ka ji shi ka nemi tsarin Allah a kansa, ka tofa a ɓangaren hagunka sau
uku", sai Usman ɗin ya ce: Sai ko na
aikata hakan, sai Allah ya tafiyar da shi daga gare ni. Muslim 2203.
Wannan sai ya nuna
cewa duk lokacin da mai sallah ya yawaita jin waswasi da tunanin zuci a
sallarsa, to ya yi 'A'UZU BILLAHI MINA SHAIƊANI RAJIM' ya tofa a ɓarin hagunsa sau uku,
in Allah ya so, Allah zai tafiyar masa da wannan waswasin.
Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) Yace "sheɗan ba zai kyale ɗayanku ba sai ya
dinga zuwa yana yi masa tambayoyi a cikin zuciyarsa. "tambayoyin da zasu
jefa ka cikin bala'i" yazo ya ce maka wa ya halicci sama? sai ka ce ALLAH,
yace wa ya halicci kasa? kace ALLAH, wa ya halicci kaza? Kace ALLAH, toh a
karshe fa zai ce ma toh shi kuma ALLAHN wa ya halicce shi?? Toh sai manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) Yace idan kaji wannan sai ka ce:
آمنتُ
باِللًهِ ورُسلُه
"Na yi imani da
Allah da Manzanninsa"
ko kace:
هُوَ
الْأَوَّلُ وَالْآخِرُ وَالظَّاهِرُ وَالْبَاطِنُ ۖ وَهُوَ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمٌ
"Shi ne Na
farko, Shi ne Na karshe, Shi ne Bayyananne, Shi ne Ɓoyayye, kuma Shi
Masani ne akan komai.
Allah ya bamu ka'ida
kwara ɗaya dangane da
sha'anin waswasi wanda shi ne "isti'aza" wanda duk lokacin da kaji
sheɗan yana taɓa maka zuciya acikin
sallah toh sai kayi "isti'aza kace:
أَعُوذُ
بِاللَّهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ
kayi sau uku kamar
yadda Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya koyar koda kuwa atsaye kake a
sallar ko a zaune ko cikin sujadah.
Mai yawan waswasi
acikin sallah yayi kokari wajan yin sallah cikin jama'a wato tare da liman,
Sannan mutum ya rika yin bakin kokarinsa wajen fitar da waswasi ko kokwanton
daga zuciyarsa.
Malamai suka ce
"wanda kokwanto ya aureshi, to ya rika yin sujadah bayan sallama".
Wato ka lazimta ma
kanka yin sujadah bayan sallama duk lokacin da ka idar da sallah. Amma ba sai
ka sake sallar ba.
Idan mutum ya taɓa azzakarinsa da
fatar hannunsa kai tsaye (ba tare da wani shamaki ba kamar riga ko wando),
malaman fikihu irin su Malikiyya, Shafi'iyya, da Hanabila sun tafi a kan cewa
alwalarsa ta warware, kuma wajibi ne ya sake sabuwar alwala kafin yin sallah.
Idan mutum ya taɓa al'aurarsa ta kan
riga ko wando (ba tare da fatar hannu ta haɗu da fatar azzakari ba), alwalarsa ba ta
warwarewa.
Idan ya shafa
azzakarinsa domin neman jin daɗi (sha'awa) alwala ta warware ba tare da wani shakka ba.
Idan ya taɓa shi ba da niyyar
jin daɗi ba (kamar don gyara
zama ko wanka), akwai malaman da suka ce alwalar tasa tana nan, amma mafi yawan
malaman mazhabar sun tafi a kan cewa shafar gabaki ɗaya tana warware
alwalar.
Malaman suna ba da
shawarar cewa duk lokacin da aka samu haduwa tsakanin fatar tafin hannu da
al'aura, to a kiyaye addini ta hanyar sabunta alwala.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.