Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Amfani Da Lakabi a Matsayin Suna a Addinin Musulunci

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Matsayin Laƙabi a Addinin Musulunci

Sanya laƙabi sunna ce a addinin Musulunci a yi wa yaro tamkar yadda shara’a ta shata. Laƙabi yana iya ɗaukar ABU wato “Baban” a haɗa shi da wani suna.

Sanya laƙabi ga ‘ya’ya yana haifar da fa’idoji masu amfani ga rayuwar al’umma, irin waɗannan fa’idojin sun haɗa da:

i. Sanya tunani da ladabi da mutumci a cikin zukatan al’umma.

ii. Bunƙasa kyawawan ɗabi’un zama da jama’a, har yaro ya riya a zuciyarsu shi babba ne.

iii. Yana sa yaro ya tashi da son al’umma tare da jin daɗi ta hanyar kiransa da wannan kyakkyawan laƙabi.

A sakamakon irin waɗannan fa’idoji da ke tattare da laƙubba ne, ya sa Annabi S. A. W. yake yi wa yara tare da ambatonsu da su. Hadisi ya tabbatar da haka, a inda aka nuna cewa:

An karɓo daga Anas R. A., ya ce: “Manzon Allah S. A. W. shi ne mafi kyawon ɗabi’u. Ina da ɗan’uwa da ake kira Abu-Umayr,, wanda nake tunanin sabon yaye ne. Duk lokacin da aka kai shi gun Annabi S. A. W. Manzon Allah S. A. W. yakan ce masa: “Ya kai Abu-Umayr! Me An-Nughayr (yautai) ya aikata?

Haƙƙin Sanya Suna Da Laƙabi

A tsarin addinin Musulunci, kowane al’amari an aza shi a bisa wani tsari na musamman, ba a bar abubuwa haka kurum kara zube ba. Wannan ne ya sa Musulunci ya shimfiɗa ƙa’idar zaɓar wa abin da aka haifa sunan da za a raɗa masa tare da laƙabin da za a iya yi masa.

A shara’ar Musulunci, uba ne aka ba haƙƙin sa wa ɗansa suna, ba uwa ba. Kamar yadda nassin Alƙur’ani Maitsarki ya zo da shi. A inda Allah Maɗaukakin Sarki Yake cewa:

Ku kira su ga ubanninsu, shi ne mafi adalci a wurin Allah, (Alƙur’ani, 33:5).

Haka kuma nassin hadisi ya tabbatar mana da cewa, uba ne ke da alhakin zaɓar wa ɗansa suna ba uwa ba. Kamar yadda wannan hadisin ya zo da bayani. A inda aka bayyana cewa:

An ruwaito daga Anas R. A. cewa: “Manzon Allah S. A. W. ya ce:An haifa mini ɗa namiji yau da yamma, na sa masa sunan kakana Ibrahim”, (Muslim ne ya ruwaito shi).

Duk da wannan damar da aka ba uba na zaɓar wa abin da aka haifa masa suna, bai halatta ga uban ko wani maga’isarsa ya sanya wa abin da aka haifa mummunan suna ba. Irin waɗannan munanan suna su ne kamar: AWAR (Mai’ido-ɗaya) ko ARAJ (Gurgu) ko makamancin waɗannan sunayen, tamkar yadda Allah Ya hana a inda Yake cewa:

… Kuma kada ku jefi juna da miyagun sunaye na laƙabi. Tir da suna na fasicci a bayan Imani. . . (Alƙur’ani, 49:11).

 Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083

Post a Comment

0 Comments