Hausawa al’umma ce fitacciya, kuma suna ɗaya daga cikin mutane mafiya shahara a doron ƙasa. Shaharar su da amon sunansu ya karaɗe farfajiyar Afirka da ma duniya baki ɗaya. Hausa ita ce harshensu na uwa da suke amfani da shi wajen sadarwa.
Hausawa wankan tarwaɗa ne,
ba baƙaƙe ne ƙirin ba. Akan samu farare
a cikinsu, sakamakon auratayya
da wasu baƙin al’ummomi, kamar Larabawa da Fulani da Azbinawa da
makamantansu. Ba su da dogon gashin
kai, ƙirar jikinsu
da kamanninsu daidai yake da na al’ummar Aryaniyawa (Aryan), waɗanda suka zauna
a tsakanin ƙasashen
Turai da na Asiya, kamar yadda Adamu (2011 p. 16) ya nuna.
Hausawa suna da nagartattun halaye da suka shahara
da su. Suna ɗaya daga cikin shahararrun ƙabilun da ake girmamawa a farfajiyar Afirka. Su manoma ne, masu ƙwazon noma da tanadin abinci.
Jarumai ne masu juriya da ɗa’a
a fagen fama. ƙwararru
ne a sha’anin sana’o’i da sauran ayyukan ƙwadago.
Hausawa haɗuwar ƙabilu
ne daban-daban da suka zo daga sassan duniya mabambanta, suka cuɗanya
da juna, suka kasance masu magana
da harshe ɗaya
da ake kira Hausa, wanda ya zama
harshen sadarwa da addini a tsakaninsu, kamar yadda Adamu (2011 p. 6) da Adamu (1997 p. 48) suka ayyana.
Mafi yawan haifaffun
‘yan ƙasar
Hausa sukan bayyana nau’in ƙabilar
da suka fito. Wasu sukan ce su Larabawa
ne, wasu Fulani, wasu Barebari,
wasu kuma Buzaye. Kodayake wasu ba su san
ko zo–in–kashe–ka ba na wancan harshen, sai dai da’awar ce kawai.
Misali, Malam Adamu Nama’aji mai ɗinkin takalmi na Unguwar
Alfindiƙi da ke cikin birnin Kano, iyayensa Larabawa
ne mutanen Ghadamus (Libiya). Sun zo Kano ne suka yi auratayya da Hausawa, suka
zama Hausawa, kamar yadda Adamu (2011 p. 15) ya bayyana.
Haka kuma waɗanda suke riƙe da sarautar
Sarkin Sharfai na Kano, zuriyar Shehu Magili ce, wanda ya zo Kano daga Madina
tun a zamanin mulkin Sarkin Kano Muhammadu Rumfa, domin ya ƙarfafa addinin Musulunci. Da zai koma, sai ya
bar ɗansa
Malam Isa da ake kira Sidi Fari, kamar yadda Dokaji, (1978 p. 21) ya nuna.
Su ma sun yi auratayya da Hausawa, suka zamanto sun saje da su. Haka Shehu Usmanu Ɗanfodiyo
da ƙaninsa Shehu Abdullahin Gwandu, Fulani
ne daga ƙabilar Toroɓɓe, kamar yadda Talata Mafara, (1999
p. 1) ya nuna. Sun jaddada addinin Musulunci a farfajiyar ƙasar Hausa, zuri’o’insu sun yi auratayya da Hausawa, sun
hayayyafa, sun koma abu ɗaya, ta hanyar riƙon al’adunsu na gargajiya,
waɗanda suka haɗa da: Tufafi, da abinci, da lamurran da suka danganci aure
da haihuwa da mutuwa da sha’anin mu’amala tsakanin dangi da abokai da shugabanni
da neman ilimi da sana’o’i da sauransu, kamar yadda Gusau (2021 p. 49), da
Adamu (1997 p. 49) suka ayyana.
Yayin da muka dubi gidan sarautar Kano, za a ga cewa Sarkin Kano Malam
Ibrahim Dabo Bafillatani ne. Kamar yadda Sufi (1993 p. 106) ya nuna, amma zari’arsu sun zama Hausawa a bisa dalilan
da aka bayyana a baya.
Idan aka karkata a
Masarautar Zazzau da take da magada har gida huɗu. Za a ga cewa, gidan sarautar Katsinawa ne kaɗai ya kasance na jinsin Hausawa. Sauran ukun kuwa sun fito ne daga jinsuna daban-daban kamar haka: Mallawa, waɗanda
Malam Musa ne farkon wanda ya hau karagar sarautar Zazzau ɗin, ya kasance ɗan asalin ƙasar Mali ne, kamar yadda Fagaci, (2014 p. sh 15) ya nuna. Shi kuwa Malam Yamusa, wanda shi
ne ya kafa gidan sarautar Barebari
a Zazzau, ya fito ne daga jinsin Larabawa daga ƙasar Bagdada,
kamar yadda Fagachi, (2014 p. 18) ya nuna.
Shi kuma Malam Abdulsalam wanda ya kafa gidan Sarautar Sulluɓawa
a Zazzau, dangi ne na ƙabilar Fulani da ake yi wa Laƙabi
da Iba, kamar yadda Fagachi, (2014 p. 23) ya nuna.
Idan aka natsu za a tarar cewa, duk zari’o’insu
sun rikiɗa
sun zama Hausawa. Sakamakon auratayya da karɓar al’adu da ɗabi’o’insu har ma da harshen Hausa, wanda ya kasance ya zamar
musu harshen farko (harshen uwa).
Bisa ga waɗannan bayanai za a iya cewa, Hausawa haɗuwa ce ta taron al’ummomi daban-daban da suka fito daga wurare mabambanta, suka zauna a farfajiyar ƙasar Hausa; tare da rungumar al’adu da ɗabi’u da yanayin rayuwar al’ummar Hausawa da uwa-uba harshen Hausa a matsayin harshen farko.
Manazarta
Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.