Daga
Abu-Ubaida Sani
Jibril Yusuf
Muhammad Sulaiman Abdullahi
Wannan wani nau’in damfara ne da ake gudanarwa a kan intanet. Masu wannan damfara sukan fito wa wanda suke son damfara ta fuskar soyayya. Idan mace za su damfara, za su fito mata a matsayin namiji wanda yake son ta. Idan kuma na miji za a damfara, za a fito masa a matsayin mace ce. A nan za mu bayar da misali da damfarar soyayya da ake yi wa maza.
‘Yan damfara sukan yi amfani da dabarun jan hankali daban-daban da za su sa
a yarda cewa mace ce kyakkyawa take son soyayya da wanda suke shirin damfara.
Ana iya tuntuɓar wanda za a damfara ta imel ko kafafen sada zumunta
kamar Facebook ko WhatsApp, da makamantansu. Za a iya tura masa hotuna waɗanda
aka ɗauka a lokuta daban-daban (hotunan mace) domin dai a ja
hankalinsa ya yarda cewa da mace yake tattaunawa.
Idan an tuntuɓe
shi ne da sunan cewa Baturiya ce daga Turai, ana iya masa ƙaryar cewa matar tana sha’awar baƙaƙen fata ne.
Ana kuma iya masa ƙaryar cewa
matar tana son aure ne daga Afirka domin samun damar kawo ziyara. Wani lokaci
kuma ƙaryar takan kasance cewar matar ta gaji
da soyayya da ‘yan uwanta Turawa saboda mayaudara ne. A wasu lokutan kuma, za a
iya ƙaryar cewa matar tana da kuɗi
ne masu yawa, duk masoyanta suna son ta ne saboda kuɗinta,
wanda hakan ya sa ta nemo wani salihin bawa a kan intanet domin samun soyayyar
gaskiya.
Burin ire-iren waɗannan
‘yan damfarar zai iya kasancewa tatsar bayanai. Idan a nan suka taƙaita, cikin sauƙi
suna iya samun bayanan da suke nema yayin da wanda aka tuntuɓa
ya yaudaru. A ɓangare ɗaya kuwa, za ta iya yiwuwa kuɗi
ake son tatsa daga mutumin.
Wannan littafin ya ci karo da Hausawa
biyu da suka faɗa komar ‘yan damfarar soyayya a kan intanet a shekarar
2024. Ɗaya a jahar Bauchi yake, ɗaya
kuma a jahar Kebbi.[1] Dukkanninsu biyu an tuntuɓe
su ta Facebook da sunan Baturiya ce wadda ta faɗa
soyayya da su. Bayan sun ɗan tattauna da ita, sai ta buƙaci su yi kiran bidiyo da wata manhaja (video call). A
nan suka nuna mata cewa ai ba su da kwamfutar da za su iya yin hakan.
Matar ta jinjina lamarin sannan ta ce
za ta turo musu kwamfuta da babbar waya saboda soyayyar da take tsakaninsu.
Bayan bai fi kwana ɗaya ba, ta ɗauki hoton sabuwar kwamfuta da sabuwar waya ta turo musu,
har ma da bidiyo tana bayanin cewa wannan kyauta ce zuwa gare su. Daga nan kuma
ta nuna cewa ta turo saƙon domin a
kawo musu Nijeriya.
Bayan kamar kwana ɗaya,
sai aka tuntuɓe su da lambar Nijeriya cewa daga filin jirgi ne a Legas.
Saƙonsu ya iso, akwai buƙatar su turo kuɗin rajistar
karɓar saƙo
(clearance fee). An turo musu hoton takardar saƙon kaya ɗauke da sunayensu da bayanansu na tuntuɓa
da adireshi, tamkar dai na gaske. Dukkanninsu biyu an sanar da su kuɗin
da bai fi dubu ashirin ba (₦20,000).
Cikin zumuɗi
suka tura kuɗin da aka buƙata. Bayan
sun tura ne kuma aka dawo musu da saƙon
cewa ai ba abin da ake nufi ba ke nan. Akwai kuɗin
da za su biya wanda ya kai kimanin dubu arba’in da biyar (₦45,000).
A wannan gaɓar ma, ‘yan damfarar sun ɗauki
hoton kwamfutar da waya a cikin kwali domin su tabbatar wa waɗanda
suke son yi wa damfarar cewa zancen gaskiya ne.[2]
Wannan labari yana nuni da yadda ‘yan
damfarar kan intanet suke shirye tsaf domin yaudarar mutane. Wani zai yi
mamakin ta yaya har ita Baturiyar ta yi bayanin cewa ga saƙo ta aiko, kuma a cikin bidiyo? Sannan ta yaya ta turo
musu hotunanta a lokacin da suke tattaunawa a kan Facebook? Wannan abu ne mai
sauƙi. Za su iya ɗauko
bidiyon wata mata a kafafen sada zumunta kamar TikTok ko Facebook da sauransu,
a inda take wannan bayani na tura saƙo.
Suna ma iya yanko wani ɓangare na fim. Daga nan za su gyara bidiyon yadda zai
dace da abin da suke son aiwatarwa. Dangane da hotuna kuwa, za su bi akawun ɗin
matar a Instagram ko wani wurin da ake ɗora hotuna
domin su tattaro hotuna daban-daban waɗanda aka ɗauka
a lokuta mabambanta.
[1] Waɗannan su ne waɗanda aka samu damar tattaunawa
da su. Littafin ya samu labaran Hausawa daban-daban waɗanda aka tunkara da irin wannan
damfarar. Waɗansu sun faɗa tarkon, wasu kuma sun
tsallake.
[2] A
wannan gaɓar ne kuma Allah ya sa
zancen ya kai gare mu, inda muka tabbatar musu da cewa damfara ce.
Manazarta:
Sani, A-U., Yusuf, J. & Abdullahi, M.S. (2025). Damfara a duniyar intanet. SAS Publishers. ISBN: 978-978-695-575-9. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19513307
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.