Na taho yima barka da zuwa Hausa,
Naji labarin
Jagora /Y/amshi:
Wada kaw wa maza kamak kwanakki,
Madogara na Malan,
Iro uban Bawa maigida Shinkahi
Jagora:
Riƙa da gaskiya Ibrafin,
Mai taimakonka Allah na nan
Jagora /Y/amshi:
Zan kawa maza gurnani,
Madogara na Malan,
Iro uban Bawa maigida Shinkahi
Jagora:
Mai kamak ka Ibrafin,
Kaga ya sha hura da nono kundum,
Yaci tuwo da nama,
Ga sutura gashi had da doki ɗamre,
Yab biye mutanen zamani sun ka
kai shi hanyaɓ ɓanna
Jagora /Y/amshi:
Ga iggiyar ruwa sun ka bash shi,
Yau gashi nan da ragga cinjim,
Dole sai ya sha rummaye,
Madogara na Malan,
Iro uban Bawa maigida Shinkahi.
An samo waɗannan batutuwa ne☝️☝️daga
cikin waƙar
Makaɗa Alh. (Dr.)
Ibrahim Narambaɗa
Tubali wadda ya yiwa Marigayi mai girma Dagacin Shinkafi wato Magajin Shinkafi
Ibrahim II (wanda yake kira da Ibrahimu na Guraguri) mai amshi "Madogara
na Malan, Iro uban Bawa mai gida Shinkahi".
Ya yi masa wannan waƙa a ƙarshe ƙarshen
1950s (Ibrahim II ya yi sarauta daga shekarar 1950 zuwa rasuwarsa a shekarar
1990).
Wato wata waƙi'a ce
ta faru a lokacin, aka kai ƙarar Magaji Ibrahim II a Isa inda Uban Ƙasa/Hakimin Gundumar dake
duba Shinkafi da zummar a cire shi. Wasa-wasa magana tayi tsauri har zuwa
majalisar mai alfarma Sarkin Musulmi a Sakkwato. Bayan dogon bincike aka wanke
Magaji Ibrahim II ya dawo ya ci gaba da mulkinsa.
"Na taho yi ma barka da zuwa
Hausa, naji labarin wada kaw wa maza kamak kwanakki" inji Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali. Wato tunda an
wanke shi kuma ya dawo gida lafiya daga Sakkwato ( ita yake kira Hausa) inda
aka kai shi ƙara
to ya zo ya yi masa barka da zuwa. A cikin wannan ɗiyan waƙa ya nuna ba wannan ne karo na farko da
ake ƙullawa
Ibrahim II irin wannan makirci ba kuma a kowane lokaci sai Allah ya kuɓutar dashi, " Naji
labarin wada kaw wa maza kamak kwanakki" kenan ko a wasu kwanuka a can
baya an yi masa irin wannan ƙullalliya amma ya fito lafiya.
A cikin waƙar dai ya ci gaba da
bayyana yadda zamantakewar fada da mutanen fada da kuma mu'amalar jama'a take.
Masu biyayya ga Sarki suna cikin ni'ima da wadata da kwanciyar hankali, daga
baya sai wasu masu neman tayar da zaune tsaye su shiga su fita saboda su haddasa
husuma a tsakanin Sarki da yan uwansa da sauran jama'arsa.
Shi ne Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali ke cewa "Mai
kamak Ibrafin kaga ya sha hura da nono kundum, ya ci tuwo da nama ga sutura,
gashi had doki ɗamre,
yab biye mutanen zamani sun ka kai shi hanyaɓ
ɓanna.. Kenan ya na
nufin jagoran wannan lamari zuwa Isa da Sakkwato a can baya yana biye da Magaji
Ibrahim II kai da ƙafa, bai kuma rasa komai ba sai shukara amma daga baya ya fara
ɗaukar shawarwari daga
mutanen da basu ƙaunar a zauna lafiya. Bayan ya ɗauki
maganganunsu to bai samu nasara akan Magaji ba, "Ga iggiyar ruwa sun ka
bash shi, yau ga shi nan da ragga cinjim dole sai ya sha rummaye" inji
Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali. Sun iza shi sun
gaza fitar dashi, ya janyowa kansa matsala, babu sutura babu kwanciyar hankali
babu abinci mai kyau sai dafaffen ganyen tafasa ko zogale a cikin gumbar hatsi
/gero (shi ne rummaye /rummace) tare da tsumma/tsummokara a matsayin suturarsa
(sune yake kira ragga).
Ya nunawa Magaji Ibrahim II
muhimmanci zama namijin tsaye a sha'anin mulki da kuma gaskata Allah SWT
"Riƙa
da gaskiya Ibrafin mai taimakonka Allah na nan, zan kawa maza gurnani"
(gurnani shi ne irin wada Zaki ko Damisa ko Kura ke furta wasu alamomi daga
bakunansu saboda su tsorata sauran dabbobi).
Makaɗan baka na Hausa musamman na fada/sarauta suna
da hanyoyi masu dama dasu ake amfani dasu wajen taskace wasu muhimamman abubuwa
da suka faru a cikin al'umma, wani lokaci su bayyana su ƙarara a cikin waƙoƙinsu a
wasu lokuta kuma su sakaya. Ala kulli halin dai suna biye /suna sane da faruwar
manya da ƙananan
al'amurra a fadoji/masarautun da suke mu'amala dasu kamar dai yadda a waɗannan ɗiyan waƙa Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali ya taskace muna
wannan waƙi'a.
Magaji Ibrahim II shi ne Dagacin
Shinkafi na 10 tun daga maƙirƙirin gidan sarautar na farko wato Muhammadun Badarawa da ya yi
mulki daga 1751 zuwa 1821 da hedikwata a Badarawa.
Ibrahim II ɗan Magaji Dango ne wanda
shi ne Dagaci na 8 daga 1919 - 1939. Shi kuma ɗan
Malam Abubakar ne shi kuma ɗan
Magaji Umaru ne Dagaci na 5 da ya yi sarauta daga shekarar 1883-1890, shi kuma ɗan Magaji Muhammadu Sanusi
ne wato Dagaci na 3 da ya yi mulki daga shekarar 1884 zuwa 1852, shi kuma ɗan Malam Muhammadun
Badarawa ne wato ma'assasin gidan da ya yi mulki daga 1751 zuwa 1821.
Bayan wafatinsa a shekarar 1821 ɗansa (ɗan uwa Magaji Muhammadu
Sanusi) da ake kira Malam Muhamman Bello ne ya gaje/gade shi har zuwa 1844.
Turawan mulkin mallaka ne suka ƙarfafa
dawowar hedikwatar mulki daga Badarawa zuwa Shinkafi a lokacin mulkin Magaji
Ahmadu Lamiɗo Dagaci
na 9 da ya yi sarauta daga shekarar 1939 zuwa 1950.
Shinkafi ta ci gaba da kasancewa
garin Dagaci a ƙarƙashin gundumar Isa, Jihar Sakkwato har zuwa ƙirƙiro
Jihar Zamfara daga Tsohuwar Jihar Sakkwato a shekarar 1996 lokacin da aka ciro
ta daga gundumar Isa, Jihar Sakkwato zuwa Jihar Zamfara aka ɗaukaka darajar ta zuwa
gunduma da kuma hedikwatar Ƙaramar Hukumar Mulkin Shinkafi a Jihar Zamfara. A halin yanzu
Shinkafi masarauta ce da Sarki mai daraja ta biyu a Jihar Zamfara da laƙabin
Sarkin Gabas.
Mai martaba Alh. Muhammad
Makwashi Isah ne ke rike da wannan sarauta ta Sarkin Gabas Shinkafi daga gidan
sarauta na Malam Muhamman Bello ɗan
Malam Muhammadun Badarawa. Allah ya ƙarawa mai martaba Sarki lafiya da nisan
kwana mai albarka, amin.
Wannan hoto marigayi mai girma
Dagacin Shinkafi na 10 ne, wato Alhaji Ibrahim II wanda a cikin waƙar da
Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali ya yi masa ne muka
ciro batutuwan da muka yi sharhi akan su.
Allah SWT ya jaddadawa dukan
magabatanmu rahama ya sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani Alfarmar
Fiyayyen Halitta Rasulallahi Sallallahu Alaihim Wasallam, amin ya rabbal
alamin.
Daga alƙalamin:
Hon. Dr. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin
Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.
25/07/2026.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.