Ticker

6/recent/ticker-posts

Cudanyar Hausawa Da Fulani Da Wanzuwar Sababbin Sunaye

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Asalin Fulani, mutanen Fula ne. A ƙasar Mali da Senegal suke zaune. Akwai Fulanin daji waɗanda ake kira Bararoji, da Fulanin Soro. Fulalanin Soro sun fi yin tasiri ga rayuwar Hausawa, saboda suna zaune a cikin garuruwa ne. Suna karatu da karantarwa. Daga cikin irin waɗannan Fulanin ne aka samu Malam Musa Jakollo kakan Shehu Usmanu Ɗafodiyo, wanda ya zo ƙasar Hausa a cikin ƙarni na 15.

Muhimmiyar cuɗanya a tsakanin al’ummar Hausawa da Fulani ta wanzu ne bayan Shehu Usman Ɗafodiyo ya jagoranci Jahadin ƙasashen Hausa. Wanda jahadin ya kasance sanadin ƙwace mulki daga hannun sarakunan Hausawa ya koma na Fulani. Suka kasance su ne shugabanni a ƙasar Hausa har zuwa farkon ƙarni na 20 (Ibrahim, 1978 p. 104). Irin wannan cuɗanyar ta wanzar da samuwar wasu sababbin sunaye a tsakanin al’ummar Hausawa. Misalai daga cikin irin waɗannan sunaye sun haɗa da:

a. Baffa: Wan uba ko ƙanin uba ko wani da yake da dangantaka ta jini da shi.

b. Dattijo: Mai mutunci da sanin ya kamata da kuma uwa uba yawan shekarun rayuwar duniya.

c. Goggo: Yar uba ko ƙanwar uba ko wadda yake da alaƙar jini da mahaifin.

d. Kawu: Wan uwa ko ƙanin uwa ko wanda yake da dangantaka ta jini da mahaifiyar.

e. Nagge: Saniya (Ibrahim, 1978 p. 105).

Haka kuma, sakamakon auratayya da ta auku a tsakanin Hausawa da Fulani an sami sunayen Fulatanci da suke ishara da jerin haihuwa. Misalansu su ne:

Jad. na 44: Ararrun Sunayen Hausawa Daga Fulani

 

Sunayen Filatanci

Ma’anarsu da Larabci

1.       

Dikko

Auwalu (Lawali)

2.       

Sambo

Sani

3.       

Yaro

Salisu

4.       

Fate

Rabi’u

5.       

Dabo

Hamisu

6.       

Jamo

Sadisu

7.       

Gabindi

Al-a’limu

8.       

Giɗaɗo

Al’Habibu

9.       

Gyano

Al-hayat

10.   

Keranga

Miyassir

11.   

Jalli

Maifara’a

Naɗewa

Duk da bambance-bambance da ake samu tsakanin sunaye al’ummomi daban-daban, akan samu kamance wajen matakan samar da sunayen. Irin wannan misali ya fito a cikin abin da aka nazarta na daga matakan samar da sunayen Barebari da na Fulani kamar yadda aka tattauna a babi na huɗu da na biyar. Kamancen ya shafi samuwar sunaye a gargajiyance da kuma yadda addinin Musulunci ya yi tasiri kan lamarin raɗa su.

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083 

Post a Comment

0 Comments