Ticker

6/recent/ticker-posts

Bunkasar Sunayen Al’ummar Kanuri (Barebari) Da Samar Da Suna Ta Amfani Da Sunayen Allah Kyawawa

Daga

Adamu Rabi’u Bakura, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Bunƙasar Sunaye a Al’ummar Kanuri

An sami bunƙasar sunaye a tsakanin al’ummar Kanuri (Barebari) sakamakon bayyanar addinin Musulunci da yadda suka karɓe shi, tun a zamanin rayuwar Sayyidina Abubakar Siddiƙu. Rungumar addinin Musuluncin da sarakunan al’ummar suka yi. Ya kawo sauyin rayuwa da zamantakewar al’umma da wayewar kai tare da kafuwar makarantun addinin Musulunci da bunƙasar su a faɗin masarautar. Sakamakon haka ne ya haifar da wanzuwar shigar wasu nau’o’in sunayen Musulunci a tsakanin al’ummar. Irin waɗannan sunaye sun haɗa da:

(i) Sunayen Allah MasuTsarki.

(ii) Sunayen Mala’ikun Allah.

(iii) Sunayen Annabawan Allah.

Irin waɗannan sunayen an cirato su ne daga cikin Alƙur’ani mai tsarki ko hadisan Annabi S. A. W. ko kuma daga cikin littattafan tauhidi.

Samar da Suna ta Amfani da Sunayen Allah Kyawawa

Al’ummar Kanuri kan yi amfani da sunayen Allah kyawawa wajen raɗa wa ‘ya’yansu suna. Sukan yi haka ne ta hanyar yi wa sunayen ɗafa-goshin ƙwayar ma’anar. Misali, “Abdu” a farkon kalmar sunanyen Allah Kyawawa. Wasu daga cikin irin waɗannan sunaye da suka tusgo daga cikin Alƙur’ani mai tsarki sun haɗa da:

Allah, wanda aka ambata sau 2699.

Ar-Rahmaan, wanda aka ambata sau 57.

Ar-Rahim, wanda aka ambata sau 123.

Al-Ƙuddus, wanda aka ambata sau 2.

As-Salam, wanda aka ambata sau 1.

Al-Mu’min, wanda aka ambata sau 1.

Al-Malik, wanda aka ambata sau 5.

Al-Ƙaadir, wanda aka ambata sau 12, da sauransu.

Keɓaɓɓun sunayen da Kanuri suka fi shahara da su wajen raɗa wa ‘ya’yansu tare da ɗafa-goshi na Abdu mai ɗauke da ma’anar “bawan” sun haɗa da:

Jad. na 27: Sunayen Kanuri Daga Sunayen Allah

 

Asalin Suna

Ma’ana

Taƙaitawa

Tsokaci

1.       

Abdullahi

Bawan Allah

Abdu ko Dala ko Dallai ko Buji

Kalmomin Dala, da Dallai da Buji duk na harshen Kanuri ne da suke kiran mai wannan sunan, kamar yadda Hausawa da Fulani suke kiran mai sunan “Maiboɗinga” ko “Maikano” ko “Maigwandu”

2.       

Abdur-Rahman

Bawan Mai-Rahama

Ramanu

Sukan kira mai sunan da “Darman”.

 

3.       

Abdul-Ƙudus

Bawan Mai-Tsarki

Gudus

Ɗaiɗaikun mutane ne ke amfani da shi.

4.       

Abdus-Salam

Bawan Mai-Aminci

 

 

5.       

Abdul-Muminu

Bawan Mai-Amintarwa

Mumin

 

6.       

Abdul-Ƙadir

Bawan Mai-Iko

Ƙadi ko Kadar

 

Tushen Bayani: Waziri, (2000 p. 17)

Sunayen Hausawa

Manazarta

Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2024). Sunayen Hausawa (Bunƙasar Sunayen Hausawa da Maƙwabtansu). WT Press. ISBN: 978-978-782-932-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19512083

Post a Comment

0 Comments