Takardar da aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Sani na Tsangayar Nazarin Halayyar Ɗan’adam, a kan Kowane Fannin Nazari, wanda aka Yi a Tsangayar Nazarin Halayyar Ɗan’adam, a Zangon Karatu na Farko na Shekarar 2021, a Jami’ar Sule Lamiɗo, Kafin-Hausa, Jihar Jigawa.
Maris,
2021
ANNOBAR
MAGUƊIN NEMAN TAKARDAR SHEDAR ILIMI: NAZARI
A KAN AL’ADAR NEMAN ILIMIN BAHAUSHE
Daga
Dr.
Abdulrahaman Ado
Sashen
Harsunan Nijeriya,
Jami’ar
Umaru Musa Yar’adua, Katsina.
e-mails: ado.abdulrahaman@umyu.edu.ng
Phone Nos:
(+234) 08066177053 (MTN)
Facebook
and WhatsApp No: 09028506956 (AIRTEL/ZAIN)
Tsakure
Ilimi abu
ne mai muhimmancin gaske. Makami ne shi, mai bunƙasa
rayuwar mutum da al’ummar da yake zaune a cikinta. Tun a lokacin da ake zaman
Maguzanci, masu ilimi a fannonin sana’o’i, su ne ke shugabantar mutane a
fannoni daban-daban. Tun a wancan lokaci, duk wani mutumen da ke son ya samu ƙima
da daraja a cikin al’umma, dole ne ya samu ilimin sana’a ko wani abin yi mai
daraja. Da addinin Musulunci ya zo, sai ya sauya madubin ƙyallaro
ƙima da daraja ga masu ilimi. Haka ma, a
lokacin da ilimin boko ya zo, ya bayar da daraja ga masu ilimi. Samun takardar
shedar ilimi, ita ce aka ba fifiko a matsayin shedar samun ilimi. Wannan ya sa
wasu, suka rinƙa bin hanyar da ba ta dace ba, suna yin maguɗi, suna
samun shedar yin ilimin, don su samu ƙimar da
ake ba mai ilimi. Haka kuma, aka samu wasu, waɗanda sun
yi ilimin, amma ba su samu aiki mai ƙima ba.
Wannan ya haifar da annobar walankeluwa da dibilwar yin amfani da ilimin da
suka koya, suka koma aikata ayyukan fanɗarewa,
domin su samar wa kansu sana’a mai ƙima. Kenan,
maguɗin samun
takardar shedar ilimi, ta haddasar da annobar fanɗarewa a
cikin al’ummar Hausawa. An gudanar da wannan bincike bisa manufar jawo hankalin
gwamnatocin Ƙasar Hausa da su yi ƙoƙari
su sauya akalar bayar da ilimi, yadda za ta koma wadda mutum zai samu ƙwarewa,
ba don ya yi wa wata hukuma aiki ba, sai dai wadda zai samar wa kansa sana’ar
da zai dogara da ita. An bi hanyoyi biyar a wajen gudanar da wannan bincike,
watau hanyar lura da abubuwan da ke faruwa a cikin al’umma, da karantawa daga
rubutattun bayanai, da yin hira da wasu mutanen da ke da dangantaka da abin da
ake bincike, da saurare daga kafafen yaɗa labarai.
An ɗora
binciken bisa ra’o’i uku, watau “Ra’in Kwaɗaitarwa”
na rukunin “Ra’in Buƙatun Ɗan’adam,”
da “Ra’in Sauye-Sauye,” da kuma “Ra’in Fanɗarewa.”
Sakamkon binciken ya nuna cewa, sauyin zamani da rashin kulawar gwamnati ya
haddasar da samuwar “Annobar Maguɗin Neman Takardar Shedar Ilimi.”
Muhimman
Kalmomin Bincike: Annoba, maguɗi, samun
ilimi, takardar sheda, fanɗarewa
1.0
Gabatarwa
Rayuwa aba
ce mai sassauyawa, kamar yadda al’adun da ake gudanarwa a cikin al’umma suke
sassauyawa (Alhassan, 1988:64). Wannan ne kan sa a ce al’umma ta sauya daga
halin da aka san ta da shi, ya zuwa wani sabon hali na daban wanda ba a san ta
da shi ba. Haka wannan lamari yake ga al’ummar Hausawa, tun daga jiya, har ya
zuwa yau.
Masana da
manazarta Hausa da Hausawa sun sha bayyana cewa, al’ummar Hausawa tana cikin
al’ummomin da ke fuskantar ƙalubalen
rayuwa na yau da kullum, domin ganin yadda sababbin al’adu suke shigowa cikin
al’ummar, suna kuma kawo mata sauye-saye a cikin halayyar zamantakewarta (Umar,
1987:4; Adamu, 2005). Amfani (2012:6) ya tabbatar da cewa, a yau, Hausa da
Hausawa sun shiga cikin halin “ni-‘yasu”. Abin nufi, sun shiga cikin matsaloli
daban-daban. A irin haka ne, aka lura da cewa, wata sabuwar al’ada, wadda cuta ce,
ta shigo cikin al’ummar Hausawa, ta kawo mata sauye-sauye a cikin harkokin
rayuwarta, ta neman ilimi. Cutar ita ce wadda ke mayar da ilimi, ya koma ba
ilimi ba. Aliyu (2010:66) yana cewa:
Cutar
rashin ilimi tana yin tarke,
Zafinta na
da yawa cikin halakawa.
Cutar
rashin ilimi tana cutarwa,
Mawuyaciyar
cuta, marar warkewa.
(Aliyu,
2010:66)
Shi dai
ilimi, kamar yadda wasu masana da manazarta suke nuna, wani al’amari ne na
ganewa da fahintar lamurran da yake kawo ci-gaban rayuwa da bunƙasar
ƙasa (Jamia’ar Beyero, 2006:205). Shi ne abin da
yake ɗaga
matsayin mutum, tare da ɗaukaka shi a bisa matsayi ingantacce
(Ado, 2009:71; Umar, 2020:16). To, amma, samunsa yana da wuya! Garin neman a
same shi (don a samu kyakkyawan matsayi a cikin al’umma), sai abin ya haifar da
wani ciwo, na ƙarancin samun ilimi, da baddala yadda ya
kamata a same shi. Ita wannan cuta, ita ce wadda ake kira da suna, “Annobar Maguɗin Neman
Takardar Shedar Ilimi” (Diploma Disease).
2.0 Fashin
Baƙi
Annoba ita
ce, yawan mace-mace na mutane, a sanadiyyar wata cuta (Jami’ar Bayero,
2006:18). A fannin wannan nazari, “Annobar Maguɗin Neman
Takardar Shedar Ilimi” (Diploma Disease), wata cuta ce da ke haddasar da
mutuwar ilimi, wadda aka lura da samuwarta, a sanadiyyar sauyin zamani da
sakacin hukumomin. Wasu masana na kiran samuwar irin wannan al’ada a matsayin
kutsen wata baƙuwar al’adar ilimi, zuwa cikin al’adar wasu
mutane, masu al’adunsu na gargajiya (Denis, 1996; 121; Walford, 1998, 405). Wani
Bature, mai suna Ronald Dore, ɗan Ingila, ya fara lura da irin wannan
lamarin, wanda ke faruwa a sanadiyyar kutse na sabuwar al’adar ilimi ta Turawa,
wadda ta wanzu a cikin wasu al’ummomi masu tasowa. Shi Dore (1976), bayan ya yi
bincike, a kan lamarin, sai ya buga littafin bincikensa a shekarar 1976, wanda
ya sa masa suna :“Annobar Maguɗin Neman Takardar Shedar Ilimi”
(Diploma Disease). Wannan littafi nasa, yana ƙunshe da
bayanai a game da “ilimi” da “shedar kammala ilimi” da kuma “ci-gaban Ƙasa.”
Masanin, ya nuna cewa, ilimin da ake bayarwa na Turawa, ya kawo fanɗarewa daga
manufar samun ilimi. Ita manufar neman ilimin Turawa, a cewar Dore (1976), ita
ce, a samun shedar kammala ilimi da ƙwarewa,
wadda ke haddasar da ci-gaba da kuma bunƙasa ga ƙasa
(Denis, 1996; 121; Walford, 1998, 405).
To, amma,
Dore (1976) ya lura da cewa, akwai wasu manufofi na ɓoye, waɗanda suka
wanzu daga baya, a sanadiyyar cusa sabon ilimin da ake yi wa Ƙasashe
masu tasowa, irin su Kyuba da Sri-Lanka da Kenya da Tanzaniya da makamantansu.
Manufofin guda uku ne, watau a samu ilimin karatu da rubutu, domin a inganta
kai, da samun ilimi domin a yi wasu ayyuka na ƙwarewa, da
kuma samun ilimi domin a samu aiki mai ƙima. To,
amma, daga ƙarshe, sai abin ya koma a kan manufa ta uku,
watau, yin ilimi domin a samu aikin yi mai ƙima.
Wannan manufar, ta haddasar da matsala a cikin al’umma, wadda take neman kashe
marowar ilimi ɗungurungum!
Domin, an koma matsayin da mutum ba ya samun aiki a kamfanoni da ma’aikatun
gwamnati da wasu cibiyoyi da hukumomi, sai in yana da “Takardar Shedar Samun
Ilimi.” Wannan muhimmanci da aka ba wa “Takardar Shedar Samun Ilimi”, ya sanya
mutane suka yi ta yin turuwar shiga makarantu, domin a same ta, don a samu
ayyuka masu ƙima a cikin al’umma. Wannan kuma, ya haddasar
da yawan makarantu da ɗalibai, a ƙasashe
masu tasowa (Denis, 1996; 121; Walford, 1998, 405).
Wasu
masana da suka yi nazari a kan aikin Dore (1976), sun yi sharhin cewa, wannan
muhimmanci da ka bayar a kan “Takardar Shedar Ƙwarewa,” ita
ta haifar da matsalar nuna bambanci, a cikin al’umma. Wannan ya ƙara kawo
bambanci a wajen ɗaukar aiki. Abin nufi, ba a ɗaukar mutum aiki sai yana da “kwalin shaidar
samun ilimi.” Wannan ya haddasar da fanɗarewa iri-
iri. Da farko, makarantu suka fara fanɗarewa, suka riƙa
bayar da takardun ƙarya. Haka ma abin ya
shafi malamai, wanda har ta kai ma, wasu malaman makarantun, suka koma
suna bayar da satar jarrabawa a makamantansu. Haka kuma, wasu waɗanda ba su samu aiki ba,
bayan kammala karatu, suka shiga aikata ayyukan fanɗarewa (Walford, 1998:409; Oɗenham, 1980).
To, a irin haka, wasu masana
da manazarta Hausa da al’adun Hausawa, suka lura da cewa, irin wannan “Annobar Maguɗin Neman Samun Takardar Ilimi,”
ta gangaro, ta shigo cikin al’ummar Hausawa (Gusau, 2010:4; Ado, 2019:6;
Sullubawa, 2020:ɓ). Bunza (2002:11) ya nuna cewa, ilimin
addinin Musulunci da na Boko su ne ilimi guda biyu, waɗanda suke
fitattu, da ke da tasiri sosai a wajen asalin ilimi a Ƙasar
Hausa. Kuma, mutum ba ya zama mai ilimi, sai ya iya rubutu da karatun (Bunza,
1998:91; Ado, 2009:71). Don haka, nazarin da aka gudanar a wannan takarda, an ɗora shi bisa
mizanin matakan
guda biyu, na tasirin neman ilimin rubutu da karatu, waɗanda suka shigo ma Hausawa
daga waje, watau na ilimin addinin Musulunci da na Boko.
3.0 Waiwayen Al’adar Ilimi a
Al’ummar Hausawa
Wasu
masana da manazarta al’adun al’ummar Hausawa, sun sha bayyana cewa, tun
asaliyyan, kafin zuwan Larabawa da Turawa Ƙasar
Hausa, Bahaushe yake da al’adunsa, ba ma kamar na ilimin sana’o’insa, waɗanda yake
gudanarwa. Kusan kowa, yana da aikin yi (Sallau, 2013:1; Ɗanmaigoro,
2010:113). Don haka ne ma, wasu masanan suka nuna cewa, riƙo
da sana’a, a wajen ɗan Bahaushe, kamar shiga wani kulob ne
(Alhassan, 1988:38). Abin nufi, akwai sana’o’i barkatai da kowane ɗan
Bahaushe ke kamawa, domin shiga cikin karɓaɓɓiyar
al’adar Hausawa (Umar, 1987:8). Ala-sam-barka! Kafin zuwan Larabawa, kowa yana
da sana’ar yi, yana cikin tarbiyya ta ilimi da alummar Hausa ta koya masa, ba
tare da wata matsala ba (Ado, 2009:65). Kenan, a wancan lokaci, babu maguɗin gudanar
da ilimin sana’o’i.
Kwanfa! An
samu sauyin rayuwa a lokacin Larabawa da Turawa suka shigo cikin Ƙasar
Hausa. Sun shigo da baƙin al’adu,
waɗanda suka
shafi hanyoyin gudanar da rayuwar Hausawa (Jegede, 2013:16). A fayyace, a
lokacin da Larabawa suka zo Ƙasar
Hausa, tun a wajen ƙarni na goma sha ɗaya ( Ƙ.11)
zuwa na goma sha uku (Ƙ.13), sun
zo da wani sabon ilimi, wanda yake gauraye da tarbiyya irin ta addinin
Musulunci (Gusau, 2008:21; Gusau, 2010:4; Galadanci, 2011:35). Wannan zuwa na
Larabawa, ya kawo ingantaccen ilimi wanda ya haifar da sauyin ƙima
da darajar da ake kallon Bahaushe da ita. Alal misali, kafin zuwansu, ƙima
da darajar Bahaushe ta ta’allaƙa da
jaruntakarsa a fagen sana’o’insa, daban-daban da yake gudanarwa. A cikinsu ne
ake nuna halaye na bajinta da ƙwazo da
makamantan hakan, wanda kan sa a samu jagora a cikin kowace sana’a, irin su
Sarkin Noma da Sarkin Ƙira da
Sarkin Dawa da da Sarkin Tsafi da makamantansu ( Galadanci, 2011:32; Umar,
1987:15). Ko a harkar addini, kafin zuwan Larabawa, Bahaushe yana gudanar da
bautarsa ta iskoki da gudanar da tsafinsa, domin girmamawa a garesu ( Gada,
2010:57; Galadanci, 2011:32).
To, amma,
bayan zuwan Larabawa, sai akalar ƙima da
daraja ta juya zuwa ga masana, masu ilimin addinin Musulunci. Mutum, ba shi da ƙima
da daraja a cikin al’ummar Hausawa, sai in yana da ilimin addinin Musulunci.
Kai! Hatta wani aiki mai daraja, mutum ba ya samunsa, sai yana da ilimi (Ado,
2009:64). Ayyuka irin na Alƙali da
Liman da Ladan da Malam da makamantansu, ba a samunsu, sai ana da ilimin
addinin Musulunci (Adamu, 1978:10; Yahaya, 1988:11). Kenan, an bayar da fifiko
ga samuwar ilimi, kafin ka samu ƙima da
ayyuka masu ƙima. Da tafiya ta yi nisa, sai Bahaushe ya
sauya manufar ilimin addinin Musulunci. Ya shigo da wata hanyar maguɗi, wadda
za ta sanya a samu ilimi da takardar shedar ilimi a cikin sauƙi.
Wannan ne ya haifar da matsalar “Annobar Maguɗin Neman
Samun Takardar Shedar Ilimi (Diploma Disease).” Abin nufi, fifiko da aka bayar
na cewa, sai kana da shedar samun ilimin Larabawa kafin ka samu aiki mai ƙima,
irin su malam, ko alƙali ko liman ko magatakarda
da makamantansu. Wannan matsala ce wadda Malamai da ɗalibai
suka haddasar da ita. Ɗalibai na
yin karatun zuƙu, su kuma malamai suna ƙyale
su, su sauka ba tare da samun “nunannen ilimi” ba. Kenan, ɗalibai sai
suka rin samun shedar ilimi, ba tare da yin ingantaccen ilimi ba.
Hakazalika, a karo na biyu, Hausawa sun ƙara
cin karo da matsalar shigowar Turawa. Bincike ya bayyanar da cewa, su Turawa,
sun shigo Ƙasar Hausa tun a wajen ƙarni
na goma sha bakwai (Ƙ.17) zuwa ƙarni
na goma sha takwas (Ƙ.18) (Gusau,
2008:24). Zuwansu ya haifar da samuwar sabon ilimi na boko, a cikinsa Ƙasar
Hausa (Galadanci, 2011:46; Sarɓi,2011:20). Shi ma, kamar ilimin
Larabawa, ya zo da manufa mai kyau, amma sai aka sauya ta, dalilin bayar da
fifiko a kan samun takardar shedar ilimi a matsayin abin da za a ƙimanta
mutum da kuma ba shi aiki mai ƙima. An
mayar da ilimi a matsayin ilimin samun aiki kawai. Don haka, mutum ba ya samun
aikin boko, sai yana da ilimin boko, wadda takardar sheda ke nuna samunsa.
Wannan ne ya ƙara kawo “bugu na biyu,” na samuwar “Annobar
Maguɗin Takardar
Shedar Samun Ilimi.” Kenan, sauyin zamani ya yi wa ilimin Hausawa na gargajiya
“kisan mummuƙe.”
4.0
Matsalar Bincike
Matsalar
da ta haifar da gudanar da wannan bincike, ita ce, an lura da cewa, akasarin ɗalibai,
na wannan zamani, ba su bayar da hankali a wajen nema da samun ingantaccen
ilimi. Ba su nuna kulawa da gudanar da ingantaccen bincike na kundayen digirorinsu,
balle na ayyukan da malamansu suke ba su. Wannan matsala ce da dole ba za a iya
cewa ga abin da ya haddasar da ita ba, sai an gudanar da bincike. Wannan ne ya
sa aka gudanar da wannan bincike.
5.0
Dalilin Bincike
Dalilin
gudanar da wannan bincike shi ne, so a zaƙulo ko a binciko ko a nemo
ko a gano matsalar da ta sanya aka samu sauyin nema da samun ingantaccen ilimi.
So ake a gano matsalar da ta sanya ɗalibai
wannan zamani na ƙarni
21, ba su mayar da hankali a wajen harkar neman ingantacce ko sahihin ilimi.
Abin nufi, so ake a binciko dalilan da suka sanya ɗaliban
wannan zamani na ƙarni
21, ba su mayar da hankali a wajen gudanar da bincike-bincike da
karance-karance na ilimi.
6.0
Manufar Bincike
An gudanar
da wannan bincike bisa manufar wayar da kan al’ummar Hausawa da ta haɗa da
malaman makaranta da ɗalibai da gwamnati da duk wasu
hukumomi masu lura da harkar ilimi, a kan ire-iren illolin da sauyin zamani ya
haddasar, ta fuskar ilimi, a cikin al’ummar Hausawa. Abin nufi, an ƙudiri
aniyar bayar da haske a kan tasirin sauya manufar ilimin addinin Musulunci da
na Boko, a kan Hausawa, da kuma halin da ake ciki a yau, a cikin al’ummar
Hausawa, ba ma kamar a kan abin da ya danganci samar wa ‘yan ƙasa
aikin yi ga waɗanda suka
yi ko suke cikin yin ilimin addinin Musulunci da na boko.
Abin sani
shi ne, kowace Ƙwandala ta kwabo,
tana da fuskoki guda biyu, ta “kan sarki” da ta “ɗamara.” A
fayyace, kowane lissafi yana da “cika” da “mara.” Watau dai, kowace rayuwa tana
da fuskoki biyu, ta “zuma” da “maɗi.” Don haka ne ma, kowane abu yana da
fuskar inganci na al’amari a game da shi, da kuma akasin hakan, a game da shi.
To, haka ma sauyin zamani a Ƙasar
Hausa, yana da fuskoki biyu na alfanu da rashin alfanunsa. Don haka, duk da
cewa, zuwan baƙi yana da alfanu ga Hausawa da al’adunsu,
amma kuma, akwai wasu ɓata-gari sun sauya shi ya koma, ya
zama ƙalubale ga Hausawa da al’adunsu. Wannan ƙalubale,
shi ne ya samar da “Annobar Maguɗin Neman Takardar Shaidar Ilimi.”
7.0
Hasashen Bincike
Duba
da aka yi na matsalar da ɗaliban
wannan zamani suke da ita, a kan harkar ilimi, sai ake hasashen cewa, abin da
ya samu “Doma” ne, yake samuwa ga “Awai.’ Abin nufi, ana hasashen cewa, annobar
tasirin samuwar ɓata
garin malamai da rashin kula na hukumomin makarantu da sakacin gwamnati su suka
kawo wa ƙasar
Hausa wannan matsala. Haka kuma, ana zato ko tsammanin cewa, bayar da fifiko ga
samun “kwalin shedar ilimi,” a matsayin shedar samun ilimi tana ɗaya
daga cikin abin da ya kawo wannan matsala. Tsarin da gwamnati ta yi, ta cewa
sai mutum yana da “kwalin shedar samun ilimi,” sannan a ba mutum aiki ko wani
muƙami,
shi ya haddasar da matsalolin fanɗarewa
daga turbar neman ilimi, da aikata ayyukan walankeluwa da dibilwa a cikin
al’ummar Hausawa. A yau, a bisa hasashen wannan bincike, ɗalibai
so suke a ce, sun ci jarabawa, sun amshi “kwalin dipuloma,” ba tare da yin wata
wahalar neman ilimin ba ko yin ingantaccen karatu ba.
8.0
Hanyoyin Gudanar da Bincike
Wannan
bincike ne irin na “Halin Da Ake Ciki.” Shi irin wannan bincike, shi ne wanda
ake gudanar da shi a kan wani abu da ke wanzuwa a yau, na halayyar wasu mutane,
a sanadiyyar cuɗanya da wasu baƙin mutane
na daban (Ado, 2019; Ado, 2020:31). Don haka, an bi hanyoyi biyar kawai, a
wajen tattaro bayanai a game da shi. Da farko, an bi hanyar lura da idon, na
ire-iren abubuwan da ke faruwa a cikin al’ummar Hausawa, a game da harkar
ilimi. Hanya ta biyu, ita ce wadda aka karanta daga rubutattun bayanai, irin su
bugaggun litattafai, da mujallu, da kundayen bincike, da wasu takardun ƙara
wa juna sani da aka gabatar a jami’o’i. Hanya ta uku, ita ce wadda aka gana da
wasu mutane, aka tattauna a game da illolin da zuwan baƙi ya
haifar a game da ilimin Hausawa. Hanya ta huɗu, ita ce
wadda aka samo wasu bayanai daga yanar gizo, a kan yadda shigowar ilimin baƙi
ya shafi wasu al’ummomi, ba ma kamar irin na Afirka. Daga ƙarshe,
an saurai ra’ayoyi na zantukan wasu mutane a cikin kafar yaɗa labarai
ta rediyo, a wasu filaye masu bayar da labaran halayen da ake ciki a yau, irin
su “Kwandon Koli” na Rediyon Bisham FM.
9.0
Ra’o’in Bincike.
A cikin
Ado (2019: iii), an kawo zancen Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau, wanda ya bayyana
ra’i a matsayin wani mizani da ake auna madosa ko mahangar aiki da aka rubuta
na bincike na ilimi. Kazalika, a cikin Ado, (2019:26) an sake kawo bayanan
Miller (1993:1) da Oɗford (1998:490) da Longman (2003:693) da
Collins (2012:1), waɗanda suka bayyana ma’anar ra’i a matsayin wani
tunani (falsafa) na ilimi, wanda ke zama a matsayin wani makami na ilimi wanda
ke bayar da bayani ko haske, na gaskiya, a kan wata matsala da ake iya gani
kuma ake iya tantance ta.
Don haka,
an ɗora wannan
bincike bisa ra’o’i guda uku. Da farko, an ɗora
binciken kan “Ra’in Ƙwaɗaitarwa”
(Motiɓation
Theory). Ra’in Kwaɗaitarwa, ra’i ne wanda ya yi bayani a kan
halayyar Ɗan’adam, a kan neman biya wa kansa buƙatun
rayuwa. Ra’in ya fi raja’a a kan abubuwan da kan jawo hankalin mutum, har ya
kai ga aikata wasu ɗabi’un da yake aikatawa cikin al’ummarsu
(Ado, 2019:98). Wannan ra’in ne wanda Mamman (2012:34) ya ba shi suna “Ra’in Ja
Ni-Mu je” (Stimulus-Response Theory), domin ganin yadda buƙatun
mutum ke jan sa har ya kai ga aikata wani aiki bisa kwaɗayin wani
abu. Don haka ne ma, madosar ra’in ta bayyan cewa, buƙatun
mutum, su ne ke kwaɗaitar da shi (ke jan shi) har ya kai ga
aikata wasu halayen da yake aikatawa. To, shi “Ra’in Kwaɗaitarwa,”
yana da rukunnan madosai masu yawa. Don haka, a cikin rukunnan Ra’o’in Kwaɗaitarwa,
an zaɓi a ɗora
binciken kan Ra’in Buƙatun Ɗan’adam”
(Theory of Human Needs). Shi wannan ra’in, wani Bature ɗan Ƙasar
Amurka, manazarcin mutumtakar Ɗan’adam,
mai suna Abraham Harold Maslow (1908-1970), ya assasa shi. Ya fara bayyana shi,
a lokacin da ya wallafa wata takarda tasa, mai taken “Ra’in Kwaɗaitarwar Ɗan’adam,”
wadda ya gabatar da ita a shekarar 1943 (Aliyu, 2015:76; Ado, 2019:108). Wasu
magoya bayan Maslow, sun haɗa da John Bruton da Iɓan Paɓloɓ
(1848-1936) da B.F Skinner (1904-1990) da Edward Lee Thorndike (1874-1949), waɗanda, su
ma, suka gudanar da bincike-bincikensu kan ƙawar da ke
kwaɗaita Ɗan’adam,
ya aikata wasu halaye (Aliyu, 2015:77; Ado, 2019:169).
Abin da
wannan ra’i yake bayani, a matsayin manufarsa, ita ce, cewa, dukkan Ɗan’adam
Allah ya halicce shi da wata “ƙawa” wadda
ke zaburar da shi ya aikata wani abu, domin ya biya wa kansa buƙatar
wasu abubuwa na rayuwa, waɗanda za su gamsar da shi da jikinsa
(Ado, 2019:16). Wasu daga cikin buƙatun da
Maslow (1908-1970) ya zayyana, a jaddawalin tsarin hawa-hawa na dala, ya
bayyana cewa, buƙatar daraja da ɗaukaka da
kulawa ita ce ke kan gaba, a cikin buƙatun Ɗan’adam.
Abin nufi, dukkan Ɗan’adam yana buƙatar
ɗaukaka da
daraja da ƙima. A cikin al’umma, waɗannan buƙatu
akan same su, idan aka samu ilimi (Aliyu, 2015:22). Saboda haka, ilimi na cikin
buƙatun Ɗan’adam,
waɗanda idan
ya same shi, to, zai samu girma da ɗaukaka da daraja da
kulawa a cikin al’umma.
Manufar
wannan ra’i, ta yi daidai da abin da Dore (1976) ya faɗa cewa,
wannan lamari na ƙimanta samun ilimi,
ya faru a ƙasashen masu tasowa. Kenan, Turawa, sun kawo
ilimi, amma sai sauyin zamani da gwamnatoci suka mayar da shi mai daraja da ɗaukaka, waɗanda buƙatu
ne da Ɗan’adam ke son samu. A duk lokacin da Ɗan’adam
ya samu ilimi, akan ba shi aiki mai daraja, wanda ke sanya shi samun ɗaukaka,
wadda ke biya masa buƙata. Wannan
kan sanya Ɗan’adam ya samu gansuwa da kwanciyar hankali
da zaman lafiya. Amma, a duk lokacin da Ɗan’adam ya
yi ilimi, bai samu aiki ba, wannan kan sanya shi cikin damuwa da rashin
kwanciyar hankali, domin bai samu biyan buƙata ba.
Daga nan kuma, sai abin ya jawo fanɗarewa daga dokokin
al’umma.
Wannan
lamarin biyan buƙata ta ilimi, irinsa
ne ya samu al’ummar Hausawa a lokacin da suka sauya manufar zuwan Larabawa da
Turawa. Abin nufi, a lokacin da Larabawa suka kawo wa Hausawa ilimin Addinin
Musulunci, sun mayar da shi abu mai daraja da ƙima da ɗaukaka. A
lokacin, waɗanda suka
same shi, suna samun ayyuka masu ƙima, irin
su limanci da ladanci da alƙalanci da
malanta da makamantansu. To, daga nan kuma, sai aka samu wasu, waɗanda suka
yi ilimin, amma ba su samu aiki ba, kila don ba su yi shi daidai yadda ake yi
ba. Wannan ya haddasar ƙirƙirar
wasu ayyuka na fanɗarewa, domin su (ɗaliban),
su cimma burinsu (buƙatunsu) na samun
daraja da ƙima da ɗaukaka.
Haka lamarin yake a lokacin da Turawa suka zo Ƙasar
Hausa. Sun kawo ilimin boko, wanda takardar sheda ke nuna samunsa. Wannan ya
haifar da da sauyin hanyar samunsa. Abin nufi, sai aka rinƙa
bin munanan hanyoyi wajen samun takardar ko kuma, bayan an sameta, aka faɗa hanyoyin
fanɗarewa domin
a samu ayyuka masu ƙima.
Ra’i na
biyu da aka ɗora wannan
bincike a bisa, shi ne “Ra’in Sauye-Sauyen Al’adu” (Theory of Cultural Change).
Wannan ra’i ne wanda Gusau (2015:51) ya bayyana shi a matsayin wanda ya fito
daga “Mazhabar Sauyin Al’adu.” Wannan ra’i ne da ya samo asalin faruwarsa daga
wani Bature, masanin halittu masu rai, mai suna Charles Robbert Darwin
(1809-1882) ɗan Ƙasar
Biritaniya. Zancen ra’in ya wanzu ne a lokacin da ya gabatar da wata takarda
tasa, a shekarar 1958 (wasu suka ce 1959), mai taken “Asalin Halittu ta Hanyar
Zaɓi,” wadda
a cikinta ya bayana yadda halittu kan sami sauye-sauyen rayuwa, daga sassauƙan
mataki (ƙaramin matsayi) zuwa ga sarƙaƙƙen
mataki (babban matsayi) (Langacker, 1973:18; Otite, 1981:13) .
Abin da
wannan ra’i ke magan a kai, shi ne, cewa, akan samu halitta, wadda ke zaune a
muhallinta, ta samu sauyi na halayyarta ko halittarta a bisa wasu dalilai na
kutsen wani abu sabo daga waje ko daga cikin muhallinta (Ado, 2019: 70).
Wasu
masana, sun bayyana cewa, sauye-sauyen al’ada, shi ne duk wani sauyi da ake
samu a cikin al’adun al’umma (ta zahiri ko ta baɗini), ta
hanyar samun ƙaruwa ko raguwar ko baddala wani abu da ake
aikatawa. Sauyi na al’ada na iya zuwa daga kowane irin mafari, amma, an fi samu
a sanadiyyar cuɗanya da wata al’umma da ke ɗauke da
wata al’ada, mai kyau da ƙima da
daraja (Sallau, 2013:32). Ganin darajar da al’adar take da ita, shi ne kan
haddasar da ɗauka ko aron
baƙuwar al’adar da aka samu cuɗanya da
ita (Horgan, 2006:102; El-Tabie, 2012:82). Gusau (2015:51) ya ƙara
da cewa, ra’in yana yin bayani a kan yadda tasirin baƙin al’adu
na zamani yake yin ƙoƙarin
mamaye al’adun gida na gargajiya.
To, ta
fannin wannan bincike, al’ummar Hausawa ta samu sauyi a cikin al’adunta, a
lokacin da suka samun cuɗanya da Larabawa da Turawa, wadda
hakan ta haddasar da aro ko ɗaukar al’adun kyawawa, irin gudanar da
harkar ilimi, na Larabawa da Turawa (Sallau, 2013:35; Yahaya, 1988:8). To,
amma, daga baya, sai aka sauya waɗannan manufofi, suka koma a matsayin
abun da ake samu, domin a samu damar kaiwa ga samun madafan iko, masu bayar da
damar wawusar kayan gwamnati.
Kazalika,
Hausawa sun ari tsarin ilimi irin na Larabawa da Turawa, da zummar su samu
ayyuka masu ƙima da daraja, irin su alƙalanci
da malanta da makamantansu (Ado, 2009:71). Wannan ya haddasar da matsaloli da
yawa, kamar irin su, yin sauri a gama karatu (karatun zuƙu),
da samun takardun shedar ilimi, ba tare da samun ingantaccen ilimi ba, da
makamantansu. Da ɗalibai masu takardun shedar samun ilimi suka
yi yawa, sai, al’umma ta gaza ba su ayyukan yi. Wannan ma ya haifar da fanɗarewa
iri-iri, wadda ta haddasar da wasu sabbabin matsaloli ga al’ummar Hausawa.
Ra’i na
uku da aka ɗora wannan
bincike a kai, shi ne “Ra’in Fanɗarewa” (Deɓiance Theory). A fannin nazarin
al’adun al’umma, mutane biyu ne suka yi fice a wajen assasa wannan ra’i. Da
farko, akwai wani Bature ɗan Ƙasar Faransa mai suna Emile
Durkheim (1858-1917), wanda ya yi bayanin fanɗarewa a cikin littafinsa mai
taken “Kashe-Kai”. Akwai kuma, wanda ya goya masa baya, watau Robbert K.
Merton, wanda shi ɗan Ƙasar Amurka ne (Otite,
1981:217).
Bayanan wannan ra’i su ne,
kowace al’umma tana da dokokinta da ta tsara waɗanda take son dukkan mutanen
da ke cikinta su kasance suna bin su. To, idan mutum ya kauce wa aikata
abubuwan da al’umma ta tsara, to, an ɗauke shi a matsayin wanda ya
fanɗare daga dokokin al’umma
(Radda, 2014:151; Ado, 2019:117).
Ta fannin wannan nazari,
binciken ya yi daidai da manufar ra’in. Domin kuwa, tun kafin zuwan baƙi, watau
Larabawa da Turawa, al’ummar Hausawa tana da tsarinta da dokokinta da
hanyoyinta na gargajiya, na samun ilimi da ƙimanta masu ilimi. A lokacin,
kowa yana da sana’arsa, wadda ƙwarewa a cikin sana’o’i ke
bayar da daraja da ƙima. To, amma, bayan zuwan baƙi, sai abin
ya sauya. Sai gwamnatoci suka rinƙa bayar da daraja ga samun “kwali”
ko “takardar sheda” a matsayin abin da ke nuna samuwar ilimi, ba tare da lura
da ƙwarewa ba. Wannan ya haifar da fanɗarewa masu tarin yawa a cikin
al’ummar Hausawa.
10.0
Annobar Neman Samun Takardun Shedar Samun Ilimi
Tasirin
samuwar sauye-sauye a cikin al’adar ilimin da Larabawa da Turawa suka kawo,
tasiri ne mai fuskoki biyu, na alfanu da na fanɗarewar
al’ummar Hausawa daga halayya ta ƙwarai ya
zuwa wasu halayen da ba a san su ba. Ilimi abu ne mai matuƙar
muhimmanci, wanda yake da manufa ta ƙwarai, to,
amma, son zuciya, na neman biya wa kai buƙatu, ya
sanya aka sami sauye-sauyen da suka jirkita al’ummar Hausawa, kamar yadda
bayanai suka biyo nan gaba.
10.1 Neman
Samun Takardun Shedar Ilimin Addinin Musulunci
Shi ilimin
addinin Musulunci, ilimi ne da Larabawa suka kawo a Ƙasar
Hausa. Ilimi ne mai daraja da ɗaukaka wanda ya kawo wa Hausawa
sauye-sauyen rayuwa ta addini da wayewar kai, a cikin wasu harkokinsu na
rayuwa. Sabon ilimin ya samar wa Hausawa wasu sababbin sana’o’i waɗanda masu
yin su, ake ɗaukarsu a
matsayin mutane masu ƙima da
daraja. Samuwar addinin Musulunci ya sanya kowa ya fantsama ga neman ilimin
addinin Musulunci. A nan, kowa so yake ya zama malam, domin ganin cewa, malanta
sana’a ce da ta fi ci (Ado, 2009:71). Ɗantumbushi
(2009:159) ya bayyana cewa, an kai lokacin da, idan aka kira mutum da sunan
Malam, a Ƙasar Hausa, to, ana nufin mutum mai mutunci
da martaba. Mutum ba ya zama malam, sai ya yi ilimin karatu da rubutu na
addinin Muslunci (Bunza, 1998:91; Bunza, 2004:17). Wannan sauyi na rayuwa, duk
da alfanunsa, amma kuma, ya kawo wasu ƙalubaloli
masu tarin yawa a cikin al’ummar Hausawa, kamar haka:
Da farko, fifita
samun takardar sheda, fiye da samun ƙwarewa, ya
haddasar da “Annobar Maguɗin Neman Samun Takardun Shedar Ilimin
Islama.” Abin nufi a nan, a bisa lura da aka yi, na ƙimar da
samun ilimin addinin Musulunci yake da shi, wanda sai an same shi ake samun
aiki a gwamnati ko wata hukuma, ya sanya ɗalibai
suka yi ta yin rigyangyaton tafiya Ƙasashen
“Gabas”, watau Barno, da ƙasashen da
ke kewaye da ita, don neman ilimi. Wasu kuma, suka yi ta fitowa daga
garuruwansu, zuwa duk inda aka ji labarin ɓullar wani
malami mai koyar da irin wannan ilimi, ana zuwa ana koyo.Wannan al’ada ta
tafiya neman ilimin addinin Musulunci, ta bunƙasa sosai
a lokacin Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo
(Umar, 2020:17). Tsarin tafiya zuwa neman wannan ilimi, yana da wuya. Hasalima,
matakan samun ilimin kan ɗauki lokaci, wanda mutum kan fara tun
daga “Molo” ya zuwa “Ƙolo”, sai
“Ɓalla”, sai “Titiɓiri”, sai “Gardi”,
sai “Alaramma”, sai “Gwani”, sai kuma “Gangaram” maƙarar ilimi
(Barkum, 1990:23; Ado, 2009:190).
To,
matsalar a nan, ita ce, saboda ɗaukar lokaci da samun ilimin addinin
Musulunci yake da shi, sai abin ya zamanto, ba dukkan ɗalibai ke
kammala karatunsu ba, har su zo su samu aikin yi. Akasari, daga matakin sauka na
“Gardi”, bayan ɗalibi ya samu “Allon Zayyana na Shedar
Kammala Karatu,” mai nuna samun ilimin addinin Musulunci, ɗalibai kan
yanke karatunsu, domin su rugo, su samu aikin yi (Ado, 2014:93). Wasunsu,
“Karatun Zuƙu” suke yi, wanda ba cikakken karatu ne ba,
wanda zai bayar da damar samun ingantaccen aiki. Daga haka ne, wasu kan shiga
sana’ar “tsibbu” (Ado, 2014:93). Hausawa na cewa; “Ƙaramin
sani ƙuƙumi ne” (Madauci
1982: 92). Don haka, wannan ne ya haddasar da wasu matsaloli a cikin al’ummar
Hausawa, kamar yadda bayanai za su biyo nan gaba.
Da farko, domin neman samun aikin yi, sai ɗaliban
ilimin addinin Musulunci, (akasari, waɗanda suka yi karatun
zuƙu), suka koma gudanar da “Sana’ar Tsibbu.” Sana’ar
tsibbu, sana’a ce ta hautsina magungunan Maguzanci da na Musulunci (Bunza,
2004:2; Bunza, 2000:44). Barkum (1990:42) ya bayyana cewa, akasarin ɗaliban
ilimin addinin Musulunci, sukan yi ɗan karatun allo,
amma, ko da ba su yi nisa ba, sai su koma hanyar tsibbu. Abin nufi, bayan wasu ɗalibai sun
samu taimakon da ake nuna masu, daga cikin Alƙur’ani,
sai kuma su haɗa da wau
dabaru na sukulle, su samar da magungunan da za su bayar ga masu buƙata
(Bunza, 2001:92; Bunza, 2004:15; Nasarawa, 1997:10). Galadanci (2011:75) ya
nuna cewa, a lokacin da addinin Musulunci ya zo Ƙasar
Hausa, ya yi hani da bautar iskoki da tsafi da camfi da makamantansu, to, an
samu kusan duk Hausawa Musulmai sun bari. To, sai daga baya, aka sami wasu suka
“koma ruwa” a sanadiyyar rashin aikin yi, bayan sun yi ilimi.Wannan matsala ce
da ya kamata gwamnati ta tsawata a kansa. Amma, gwmnati na kallonsu ba tare da
twasatawa ba. Wannan matsala ce babba! Abin nufi, annoba ce, a harkar ilimin Islama,
a al’ummar Hausawa.
Bayan
haka, waɗannan ɗalibai, da
ba su iya kai wa ga samun ilimin zama “Gwani” ko “Gangaram” ba, da zarar sun
samu ɗan abinda
suka samu, akasari a matakin “Gardi”, sai kawai su ruga su zama “Gardawa.” Abin
nufi, sai su koma su samar wa kansu sana’o’i daban-daban na siddabaru.
Da farko,
wasu kan yi sana’a “Gardin Wando.” Gardin Wando, shi ne gardin karatun allo,
mai yin shiga irin ta “maza-mata”, wanda ya ɗauki
sana’ar yi wa mata hidima. Abin nufi, yakan tafi gidaje mata, ya rinƙa
kula da su, ta hanyar ba su magunguna na kariya daga wasu larurori da ke
damunsu. Kazalika, sukan nishaɗantar da mata da kwanzarta su, ta
hanyar kiɗa da rawa
da wasannin siddabaru, irin su tafiya cin kasuwar sama, su yo masu sayayya da dabon
Ɗandaƙoƙa
da na hawan mashi da shuka duma ya fito, ya yi yaɗo da dakan
turmi da taɓarya da
makanatansu (Ado, 2009: 232; Nasarawa, 1997:14; Alhassan, 1988:87; ‘Yartsakuwa,
2000:17). Wannan matsala ce da ƙaramin
sani ya jawo ma ƙasar Hausa.
Haka kuma,
an samu wasu ɗaliban
ilimin Isilama, suka waske, “suka raɓe da guzuma, suna
harbi karsana.” Abin nufi, suka shiga yin wasa da wasu dabbobi, a matsayin
“Gardawan Dabbobi”, waɗanda suka mallake su ta hanyar amfani
da ilimin Isilama. Asalin sana’ar kama da wasa da dabbobi masu haɗari, irin
su kura da biri da maciji da kunama da makamantansu, sun samo asali daga sana’ar
gargajiya ta farauta, a Ƙasar Hausa
(Ado, 2009:76). Illa iyaka, a lokacin da ɗaliban
ilimin Isilama, suka ga cewa, ba su sami isasshen ilimi ba, amma, sun sami na
laƙunna da asirai, sai suka gwama ilimin
gargajiya da na Isilama, domin su samar wa kansu sana’ar yi (Abubakar, 2002:43;
Bunza, 2004:7). A irin haka ne suka ƙirƙiri
yin amfani da asirai da siddabaru, don nuna bajinta. Suna kama ire-iren waɗannan
dabbobi, masu haɗari ga mutane, suna wasa da su, da sunan yin
amfani da ilimin addinin Musulunci(Ango, 2000:21; Ado, 2009:150).
Kazalika,
a wajen harkar sana’ar kiɗa da waƙa, ɗaliban
ilimin Isilama, ba a bar su a baya ba. Wasu, sun ɗauki
sana’ar yi wa Malamai kiɗa da waƙa, suka kira
kansu da sunan “Gardawan-a-Daki-Buzu” (Ɗangambo,
1984:30). Su ba su yi wa wani kiɗa da waƙa, idan ba
malami ba ne (Ado, 2009:215). Kazalika, baya ga Gardawan Wando, kusan duk wani
makaɗi da mawaƙi
na Ƙasar Hausa, za a iske gardi ne, wanda ya fanɗare wa
hanyar “sambel,” ta yin amfani da ilimin da ya koya. Shi ya sa, a duk lokcin da
aka ji tarihin wani mawaƙi, sai ka
ji ya ce, daga almajiranci ya zarce zuwa yin kiɗa da waƙa
(Gusau, 2013:106). Alal misal, akasari makaɗan
Gambara, irin su Na-Birdigau mai Gambara da Sale Gambara, duk sun bayar da
bayanai na rayuwarsu, a cikin hirarrakinsu na gidajen rediyo, cewa, daga
almajiranci suka ɓige ga yin kiɗa da waƙar
Gambara. Haka ma, wasu makaɗa da mawaƙa, irin su
Alhaji Mai Daji Sabon Birni da Alhaji Sani Sabilu na Kanoma duk daga
almajiranci, suka bige zuwa sana’a kiɗa da waƙa
(Ado, 2009:74). Kenan, wasu makaɗa da mawaƙan Hausa
almajiri ne, waɗanda ke son aiki yi mai ƙima,
amma, ba su iya samun ilimin da zai iya kai su ga samun ba, sai kawai suka faɗa kiɗa da waƙa.
Kenan, akasarin mawaƙa da makaɗan Hausa,
“Annobar Maguɗin Neman
Takardar Shedar Ilimi” ta kai su ga wannan sana’a.
Daga ƙarshe,
kamar yadda aka saurara a kafafen yaɗa labarai, kamar irin
Taskar Labarai ta Bisham FM, an samu bayanin cewa, a yau, wasu Hausawan da suka
gaza samun “Takardar Shedar Kammala Karatu,” sun koma ga harkarsu ta ilimin
gargajiya, ta bayar da magungunan waraka daga cututtukan jama’a. Alal misali,
wasu masu iƙirarin cewa malamai ne, sun koma harkar
bokanci. Sun faɗa, gadan-gadan a wajen bautar iskoki ta
hanyar yi masu biyayya, da gudanar hidimomi na yanke-yanken dabbobi da mutane,
domin a samu biyan buƙata. To,
amma, sukan raɓe da
guzuma, su harbi karsana. Abin nufi, sukan nuna cewa, magunguna ne na Musulunci.
Da gani an san da cewa, neman aikin yi, don a samu kuɗi, suka
haddasar da sauya manufar ilimin Isilama.
10.2 Neman
Samun Takardun Shedar Samun Ilimin Boko
Ilimin
boko, wani sabon ilimi ne da masana da manazarta suka tabbatar da cewa, Turawa
ne suka shigo da shi cikin Ƙasar
Hausa, tun a wajen ƙarni na 19 zuwa 20.
Abin ya wanzu sosai a Ƙasar
Hausa, a lokacin mulkin Gwamna Lugga, wanda shi ne ya ba Sir Hans Ɓischer,
watau Ɗan Hausa, izinin kafa makarantar boko ta
farko a Kano (Yahaya, 1988:90; Galadanci, 2011:46; Malumfashi, 2009: ɗɓii). Wasu masana suna
bayar da bayanai, na mahangarsu a kan ilimin Turawa na boko. Wasu suna kallonsa
a matsayin ilimin littafi, watau “Book”, wanda ba wahayinsa aka yi ba, wanda
daga wannan suna ne ya samu sunansa na “boko” (Bunza,2 002:24; Bagari, 1986:91;
Ɗangambo,1984:10; Ɗantumbushi,
2009:157; Yahaya, 1988:74). Amma, wasu manazarta na kallonsa a matsayin ilimi
na “shakku” ko na “yaudara” ko na “zalunci” ko na “ƙarya” ko
na “zamani” da makamantansu (Ado, 2010:139).
Duk da
cewa, ilimin boko na Turawa, a cewar Galadanci (2011:46) ya zo da wasu abubuwa
masu amfani. To, amma fifiko da ya bayar a kan bayar da aikin gwamnati ga masu
“Takardar Shedar Ilimi,” ita ce ta haifar da matsaloli. Abin nufi, Turawa sun ƙarfafa
cewa, idan an same shi, to, za a samu ayyuka kyawawa, masu gwabin biya, a duk ƙarshen
wata. Kenan, an girmama samun kuɗi da muƙami, ga
duk wanda yake da “Kwalin Ilimi,” ba tare da fifita ƙwarewa ba.
Don haka, aka yi ta rububin shiga makarantun boko don samun ilimin Turawa. Lura
da aka yi, na yadda aka fifita samun ilimi, shi ne ya sanya wasu mawaƙa,
irin su Alhaji Aƙilu Aliyu ya hujjanta
manufar da ilimin boko ya zo da ita, kamar haka:
Shi ne
Kadaura, ilmu babbar gayya,
Inuwa mayalwaciya,
wajen hutawa.
(Aliyu,
2010)
To,
matsalar a nan, ita ce, Turawa sun kawo ilimi bisa manufa mai kyau, sun fifita
samun takardar sheda, kafin a ba mutum aiki, don jawo ra’ayin Hausawa, a kwaɗaitar da
su karɓi ilimin.
To, amma sai ba a fahimci manufar ba. Wannan laifi ne na hukumar ilimi ta ƙasar
Hausa. Wasu sun ɗauka da cewa, Turawa sun nuna bambanci, mai
nuna cewa, iliminsu ya fi na Hausa, watau na gargajiya da na Musulunci (Ɗantumbishi,
2009:165). Duk wata hikima, a cewar Mu’azu (2014:3), sai dai ka ji an yi fi
bayar da fifikon ta a harshen Turanci, amma shi harshen Hausa an mayar da shi
harshen hira da wasan yara. Masanin ya sake tabbatar da cewa:
Tun farkon zuwan Turawa, ƙoƙarin da
aka yi ta yi shi ne,
kafa
Turanci cikin harkokinmu, yadda duk yadda muka yi
ba za mu
yi tasiri ba, sai ta hanyar Turanci da al’adun Turawa.
(Mu’azu,
2014:3)
Bature ba
ya aikin banza! Abin da Turawa suka shuka na fifikon ilimi ya jawo ma Bahaushe
matsala a cikin al’ummarsa. Ƙimar da
Turawa suka bayar ga iliminsu, ya kawo sauye-sauye a wajen nema da samun ilimi
a Ƙasar Hausa (Ɗantumbishi,
2011:164). Bunza (2019:16) ya tabbatar da wannan zance, da ya ce:
Hasarar da
Ingilishi ya kawo muna,
ta fi ta
yaƙin basasa da muka yi.
(Bunza,
2019:16)
Kenan, sauya
akalar ilimin da Turawa suka kawo, ya sanya Hausawa sun bar sana’o’insu na
Hausa, sannan kuma, ba a ba su wasu masu ƙima da
daraja ba, dole sai sun samu takardar shedar yin sa. Abin nufi, an shiga boko,
an zubar da sana’o’in gargajiya, kuma ba a samu aikin Turawa ba, sai ana da
kwalin shedar samun ilimin. Wannan ya kawo sanadiyyar gurɓata ilimin
boko. To, daman, masana irin su Gusau (2010:4) da Galadanci (2011:46) sun nuna
cewa,Turawa sun shigo Ƙasar
Hausa, bisa wasu manufofi nasu. Kenan, ana ganin kamar sun shigo ne su haddasar
da matsaloli, kamar haka:
Da farko,
jingina “Takardar Shedar Samun Ilimi”, a matsayin shadar da za a gani a ba
mutum aiki, ya sa ɗalibai ba su “damuwa” a cikin harkar yin
karatun. Damuwa kuwa, ciwo ce. Dalilin wannan damuwa ta sanya ɗalibai suka
fi himmatuwa ga samun takardar shedar ilimin boko, ta kowace hanya. Wannan
matsala ce, wadda wasu masana da manazarta Hausa da Hausawa, suka nuna cewa,
wannan matsalar watsar da samun sahihin ilimi, wata alama ce mai nuni da cewa,
alummar Hausawa tana neman shiga “Shekarun Duhun Kai na Ilimin Hausawa” (Dark
Age of Hausa Studies). Abin nufi, an shiga “Annobar Maguɗin Neman
Samun Takardar Shedar Kammala Karatu” (Diploma Disease), a maimakon neman samun
ingantaccen ilimi, a zahirance (Sullubawa, 2020: ɓ; Ado, 2019:6). Wannan jawo
hankali da aka yi, an yi ne bisa kyakkyawar manufa, domin Hausawa su mayar da
hankalinsu, su samu ingantaccen ilimi. To, amma, sai son zuciyar ɗalibai da malamai suka gurɓata lamarin. Su kuma hukumomi
da gwamnatoci suka yi biris a kan matsalar.
Ciwon damuwa na biyu, shi ne
wanda wasu iyaye suka jawo, a harkar ilimin ‘ya’yansu. Wannan kuwa shi ne, wasu
iyaye kan sanya a yi wa ‘ya’yansu tsallaken aji, domin su yi sauri, su kammala
karatunsu, su samu “Kwalin Shedar Kammala Ilimi,” domin a samar masu aiki da
wuri. Ke nan, ba ilimin aka damu ɗalibi ya samu ba, “kwalin” kawai ake so ya
samu. Wannan babbar annoba ce a cikin ilimin Hausawa na boko
(Abdulrahman, 2007). A irin haka ne, a manyan makarantu, wasu ɗaliban kan
so su bayar da kuɗi domin a ba su maki, domin su ci jarbawa.
Kazalika, wasu ɗalibai mata, kan so su bayar da jikinsu,
domin a ba su maki, don su ci jarabawa, su samu kwalin shedar sun samu ilimi,
domin su je su samu aiki mai ƙima.
Wannan babban ciwo ne, a harkar ilimin boko na Hausawa.
Kazalika,
harkar neman samun “Takardar Samun Ilimin Boko”, ta sanya ɗalibai ba
su damuwa, su san ilimin, sai dai yin satar jarabawa. Da yawa daga cikin ɗalibai,
akan sami wasu masu rubuta amsoshin jarrabawa a jikin hannuwansu da rigunansu
da kan teburin da suke rubutu, domin su yi satar jarabawa (Abdulrahman, 2007).
A wata hira da aka yi da wani ɗalibi, ya bayyana cewa, akwai wani
gurgu da yakan rubuta satar amsa, ya ɓoye ta a cikin kafar
(kussuwar) sandarsa da yake dogarawa. Idan ya fakaici idon malamai, sai ya yi
ta fito da takardun, yana rubuta amsar jarrabawarsa, kuma yana ba sauran ɗalibai su
juya. Wannan babbar masifa ce a harkar neman ilimi a Ƙasar
Hausa. Lallai hukumomin ilimi sun yi sakaci, suka bar fifikon samun ilimi a kan
“takarda” a maimakon ƙwarewa.
Bugu da ƙari,
a yau, a harkar neman ilimin Boko, ɗalibai ba su son yin
karatu, don haka, ba ma su iya gudanar da bincike-bincike (Ado, 2018:13). Abin
nufi, a yau kusan babu wasu ɗalibai da za su iya tsayawa, bisa
gaskiya, su rubuta aikin gida da malamai kan ba su. Sukan duƙufa
a wajen juyar aikin juna, su kai wa malami, a matsayin aikin da suka yi (Ado,
20120:24). Ba su iya gudanar da bincike, balle su rubuta ingantaccen kundin
digiri na kammala iliminsu. Ɗalibi kan
tashi daga wata jami’a, zuwa wata, domin ya juyo aikin wani, ya gabatar da shi
a wata jami’a, a matsayin kundin digirinsa (Abdullahi, 2007:23; Ado, 2019:2).
Yanzu ma, ɗalibai sun
ɗauki salon
ƙin rubuta kundin digirinsu, don sun san za a
yafe masu, ko kuma a karɓi duk abinda suka juyo (kwafo) suka
kawo, idan lokaci ya ƙure na
kammala karatunsu na digiri. Wannan masifa ce ta ilimi. Ba wai suna koyon
ilimi, domin bunƙasa kansu da ƙasa
ya dame su ba, su dai suna yi ne domin su sami “kwalin shedar sun yi ilimi.”
Masana, irin su Bunza (2019:16), ya nuna damuwarsa a kan irin wannan masifa ta
“Annobar Maguɗin Neman
Samun Shedar Ilimi,” a inda ya ce:
“Malami ya
karanto ya yi shifta,
ɗalibai su
hardace matani,
ba tare da
sanin ma’ana ba,
har a
kammala digiri, ɗalibi bai san ma’anar
sunan
darasin da ya karɓi digiri a kansa ba.”
(Bunza,
2019:16)
Wa Iyazu
bil Lahi! Ba komai ya kawo wannan matsala ba illa maguɗin da ɗalibai ke
yi a wajen neman ilimi, da sakacin da malamai ke yi a wajen rashin lura da
yadda ake bayarawa da karɓar ilimi, da kuma rashin sauya
manhajar karatu, wadda za ta fifita ƙwarewa
bisa " ƙwalin sheadr samun ilimi” Ba karatun, ko
samun ilimin ke gaban ɗalibai ba. So suake su samu “Kwalin
Digirin,” domin a sami aikin gwamnati.
Daga ƙarshe,
ana iya cewa, sauye-sauyen manufa cikin harkar ilimi, baya ga ɗimbin
alfanun da aka samu, sun haddasar samuwar “Annobar Maguɗin Neman
Samun Shedar Ilimi.” Abin nufi, zuwan baƙi, ya ƙara
kawo wayau ga Hausawa, a wajen harkar ilimi. Bambancin da aka nuna, na cewa,
sai mai takardar shedar samun takardar shedar samun ilimi, ke iya samun aiki, sai
kawai Bahaushe ya ci gaba da gudanar da walankeluwa da dibilwar zamani ta 149,
a cikin harkar samu da neman samun ilimin boko. Tsananin riƙon
al’adar da yake da shi, ya sanya bai bar gudanar da wasu al’adunsa ba
(Alhassan, 1988:6)
11.0
Sakamakon Bincike
Kamar
yadda bincike ya nuna, cewar, tun kafin zuwan baƙi Ƙasar
Hausa, Hausawa suke da al’adunsu na gargajiya da suke amfani da su a wajen biya
wa kansu buƙatun rayuwarsu ta kowane fanni, irin su
siyasa, da addini, da tsaro, da kiwon lafiya, da makamantansu. Don haka, wannan
bincike ya gano cewa:
Da farko, zuwan
Larabawa da Turawa sun bunƙasa Ƙasar
Hausa da Hausawa ta hanyar kawo masu sababbin ilimi na addinin Musulunci da na
Boko.
Haka kuma,
Larabawa da Turawa, sun fifita samun “Takardar Shedar Ilimi,” domin su zaburar
da ƙawar Hausawa, shiga makarantu, su samu
ingantaccen ilimi, amma sai Hausawa suka sauya abin ya koma a matsayin lasisin
da sai kana da shi ake ba ka aikin yi ko naɗa ka wani
muƙami.
Fifikon da
aka bayar ga nema da samu “kwalin ilimi” ya haɓaka sosai,
a lokacin da Hausawa suka karɓi ragamar bayar da ilimi a Ƙasar
Hausa, kafin a samu aikin yi. A garin neman biya wa kai buƙatar
samun aikin yi, ya sanya ɗalibai suka shiga hanyar maguɗi ta
“Annobar Maguɗin Neman
Samun Takardar Shedar Ilimi.” Abin nufi, kamar hirar da aka yi da wasu, sun
tabbatar da cewa, akwai ‘ya’yan da akan ajiye masu aiki, a ƙi
ba wani, har sai sun samo “kwalin” shedar sun sami ilimin kujerar da aka ajiye
masu. Wannan shi ya sa, ba su kula, ko mayar da hankali, a kan abin da ake
koyar da su. Suna so ne kawai su samu “kwalin” shedar samun ilimi domin an riga
an ajiye masu aikin gwamnati da za su yi. Kazalika, ta fannin ilimin addinin
Musulunci, akwai iyayen da ke son ‘ya’yansu su gaje su, a harkar ilimi. Duk da
cewa ‘ya’yan ba su samu isasshen ilimi ba, sai a ɓoye, a
kwarzanta ɗalibin, a
ce ya je “Barno” ko ya je “Masar” ko ya je “Sudan” karatu. Zuwa wata Ƙasa
karatu da samun karatun, ba ɗaya suke ba.
Daga ƙarshe,
binciken ya lura da cewa, son zuciyar ɗalibai, sakacin
malamai da hukumomi, shi ya haddasar da matsalolin da Hausawa suke ciki a yau.
Dalili kuwa shi ne, tarin yawan ilimin da Hausawa suka samu daga baƙi,
guda biyun da suka shigo masu, sun sanya su ƙarin samun
dabaru na gwama al’dunsu da na baƙin. Wanna
ya sanya suka samar wa kansu “hautsunannun al’adu, irin su “tsibbu” da “al’adun
kasuwar Kano”na ƙarya da yaudara da
walankeluwa. Kusan duk wata cuta da masu ƙaramin
sani suke yi, a cikin al’ummar Hausawa, sukan danganta shi da ilimin addinin
musulunci ko na boko. Alal misali, bokanci irin na yau da tsafi irin na yau,
akan danganta shi da ilimin addinin Musulunci. Kazalika, nau’in yaudara na 419
da ta Yanar-Gizo duk an ɗauka da cewa’yan boko ne ke yi
12.0
Shawarwari
Tunda dai,
masana da manazarta, sun tabbatar da cewa, Hausawa suna da tsananin riƙo
da al’adunsu na gargajiya. To, Kenan, “komai ka yi da aura, sai ya ci kara.”
Abin nufi, komai aka kawo wa Hausawa, sai sun sauya shi, cusa al’adunsu a ciki.
Don haka, ana shawartar masu hannu a cikin harkar Hausa da Hausawa. da cewa, su
sake duba harkar ilimi, ta hanayar tsintsintar ilimin addinin Musulunci da na
Turawa, wanda zai kawo ko sanya mutum ya koyi wata sana’ar da zai iya dogara da
ita, domin ɗaukar ɗawainiyar
kansa da iyalansa. A daina kawo ilimin da za a rinƙa kwaɗaita ma ɗalibai
cewa, idan suka gama za su samu aiki “kaza.”
Kazalika,
kamar yadda Anne (2019:171), ya nuna cewa, a rinƙa sanya
harkar ilimin gargajiya a cikin harkoki na ci-gaba, to, ya kamata gwamnatocin Ƙasar
Hausa, su rinƙa yin hakan. Abin nufi, a bunƙasa
al’dun Hausawa na gargajiya, ta yadda za su rinƙa samar da
bunsaƙa a cikin ƙasa.
Gwamnati ta farfaɗo tare da bunƙasa
sana’o’in gargajiaya, ta hanyar sanya su a cikin manhajar ilimi, da kuma
tabbatar da aikata su, a aikace. Ana ganin, wannan zai kawo raguwar ko ma kawar
da matsalolin da ake fama da su a cikin al’ummar Hausawa.
Bayan
haka, ana shawartar Hausawa da su ba gwamnati goyon baya a bisa
shirye-shiryenta na gwama ilimi addinin Musulunci da na boko, domin samar da
maslahar rayuwa. Kamar yadda Umar (2020:18) ya bayyana cewa, hukumar UNICEF ta
shiga cikin harkar mayar da makarantun allo zuwa na zamani, ta hanyar gwamutsa
ilimin addinin Musulunci da na Boko, to, a bayar da goyon baya domin a samu
wata sabuwar hanyar samun ingantaccen ilimi.
Wata
shawarar ita ce, malamai fa ya kamata su rinƙa zage
damtse, a wajen duba ayyukan ɗalibai da kyau. Malami ya dage ga
sanin ilimin ɓangaren da
ya koya, kuma yake koyar da shi. Bayan ɗalibi ya
kammala karatunsa, ya fa san abin da Malami ya yi masa na mugunta, ta ƙin
koyar da shi da kyau, da kuma rashin duba aikinsa da kyau. Abin nufi, ɗalibi fa
ya san aikin wani ya ɗauko, amma, malamin bai hankalta ba
(ya lura), har ya nuna ɗalibin ya yi aiki mai kyau. Ya sanya
masa hannu a kundin digirin da ya juyo (ya kwafo) daga wata jami’a ko na wani ɗalibi da
ya kammala. A lura fa! Ɗaliban kan
faɗi halayyar
“Annobar Rashin Duba su,” da wasu Malamai ke yi, bayan sun kammala karatunsu.
Daga ƙarshe,
ana shawartar Malaman Hausa da su rinƙa bayar da
ilimi wanda daga ƙarshe, ɗalibi zai
dogara da kansa. Malamai masu koyar da darasin al’ada da adabi da harshe, suna
da babbar dama sosai, ta yadda za su iya ɗora ɗalibai a
kan harkokin da suka danganci sana’o’i na gargajiya da na zamani. Wannan
shawara tana daidai da irin wadda Salawu (2000:50) ya bayar cewa, ana son ɗalibi ya
tashi tsaye ya samu ilimin da sana’ar yi, domin dogaro da kansa. Kenan, tun
farko, da ilimin da ake ba ɗalibai, irin wanda zai nusar da su ne,
a kan yadda za su sami sana’o’in da za su dogara da kansu, da ba a samu wannan
annoba ba. Da man dai, sana’o’i na gargajiya, gado ne na Bahaushe. Ashe, don ka
ce gyara kayanka, ai ba zai zama sauke mu raba ba. Abin nufi, don ka ba Bahushe
ilimin da zai inganta sana’o’insa, ai ba zai taɓa samun
matsala ba da duk wani sabon ilimin da zai shigo masa.
13.0
Kammalawa
Hausawa na
cewa, “zama da maɗaukin kanwa, shi ke kawo farin kai.” Abin
nufi, bincike ne wanda aka gudanar a kan illolin sauya manufar ilimin da
Larabawa da Turawa suka kawo a ƙasar
Hausa. Binciken yana ƙunshe da
matsalar da ta haifar da shi da dalilansa da manufarsa da hasashensa. An bi
hanyoyi biyar a wajen tattaro bayanan da suka bayar da sakamakon binciken. An
dora binciken kan ra’o’i uku na ‘Ra’in Kwaɗaitarwa”na
“Buƙatun Ɗan’adam” da
“Ra’in Sauye-Sauyen Al’adu da kuma “Ra’in Fanɗarewa.”
Sakamkon binciken ya yi daidai da hasashensa cewa, sauya manufar ilimin da baƙi
suka kawo matsalar samuwar “Annobar Maguɗin Neman
Samun Takardar Shedar Ilimi.” Abin nufi, wannan ne ya haddasar da matsalolin da
ake samu a harkar neman ilimi da samunsa a al’ummar Hausawa.
Manazarta
Abdullahi, I. (2007). "Harshen Hausa Zai Mutu!
Ina Mafita?" Makarantar Hausa (Makaranta Ga Mai Neman Ilimi). Mujallar
Harshe da Adabi da Al'ada na Hausa. Fitowa ta 3. Sokoto: Ubandoma Road (Sabon
Titi).
Abdulrahman, A. (2007). "Parental
Over-Protectiveness and Over-Indulgence on their Children and Rate of
Indiscipline in Schools: A Case Study of F.G.C. Sokoto," The Zodiac. A
Publication of Federal Government College, Sokoto. Vol. V, 2007. Sokoto:
Federal Government College.
Adamu, M. (1987). The Hausa Factor in West African
History. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Ado, A. (2020). Dabarun Gudanar Da Bincike Na Ilimi A
Kan Hausa. Katsina: Government Printing Department.
Ado, A. (2019). Ra'o'in Bincike Kan Al'adun Hausawa.
Katsina: Bugu na Biyu. Government Printing Press.
Ado, A. (2019). "Muhimmancin Nazarin 'Ra'o'in
Bincike ga Ɗalibai Masu Nazarin Al'adun
Hausawa." Takardar da aka gabatar a taron Makon Hausa wanda Ƙungiyar Hausa ta Sashen Nazarin Harsunan Afirka, suka Shirya
daga Ranar 3-6 ga watan Oktoba, Jami'ar Alƙalam,
Katsina.
Ado, A. (2019). Bincike Na Kimiyya A Hausa: Yadda
Yake Da Yadda Ake Gudanar Da Shi. A Draft Book on Research Methodology in
Hausa, which is not yet published. The Draft was made by Katsina: Government
Printing Press.
Ado, A. (2018). "Muhimmancin Nazarin 'Ra'o'in
Bincike' ga Ɗalibai Masu Nazarin Al'adun
Hausawa," Al'adunmu: Journal of Current Research in African Studies.
Vol.1, No.1, Maiden Edition. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.
Ado, A. (2014). Sana'ar Gardancin Hausawa: Asalinta
da Yadda Take da Yadda Ake Yin Ta a Ƙasar Hausa.
Alƙahira: Maktabatul Adab.
Ado, A. (2009). "Gardancin Hausawa Jiya Da
Yau." A Dissertation Submitted to the Postgraduate School in Partial
Fulfillment of the Requirements for the Award of the Degree of Master of Arts
(Hausa Culture), Department of Nigerian Languages, Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo University.
Ado, A. (2010). "Boko: A Ma'aunin Manazarta da
Masana Addini", Himma Journal of Contemporary Hausa Studies. Department of
Nigerian Languages, Katsina; Umaru Musa Yar'adua University.
Alhassan, H. da Wasu (1988). Zaman Hausawa. Lagos:
Islamic Publication Bureau.
Aliyu, A. A. (2010). "Kadaura Babbar
Inuwa", Fasaha Aƙiliya.
Zaria: Northern Nigeria Publishing Company.
Aliyu, U. D. (2015). Introduction to Psychology of
Learning. 2nd Edition. Kano: Baba Isa Printing Press.
Amfani, A. H. (2012). "Hausa da Hausawa: Jiya da
Yau da Gobe," Champion of Hausa Cikin Hausa: A Festschrift in Honour of Ɗalhatu Muhammad. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.
Anne, O. E. (2019). "Rethinking Traditional
Knowledge in Rural Development," Danmarna International Journal of
Multi-Disciplinary Studies. Vol. 10. No. 1. Katsina: Umaru Musa Yar'adua
University.
Bagarim, D. M. (1986). Bayanin Hausa: Jagora ga Mai
Koyon Ilimin Bayanin Harshe. Maroc: Imprimerie El-Maarif Al Jadida.
Barkum, I. M. (1990). "Malanta A Matsayin Sana'a
A Birnin Kano." Kundin Digiri Na Farko, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Kano: Jami'ar Bayero.
Bunza, A. M. (2019). "Hausa da Hausawa a Duniyar
Ƙarni na Ashirin da Ɗaya (Amsa Kiran Majalisar Ɗinkin
Duniya (UN) ga Ranar Hausa ta Duniya-Litinin 26 Agusta, 2019)," Takardar
da aka Gabatar a Bikin Hausa ta Duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya ta Keɓe a Ranar Litinin 26 ga Agusta, 2019 An Gudanar da Taron a
Jami'ar Bayero, Kano.
Bunza, A. M. (2004). "Ilimin Tsibbu a Wasar
Hausa: Jiya da Yau." Takardar da aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Sani na Musamman a Ɓangaren Nazarin Al'ada da Addini. Cibiyar Nazarin Harsunan
Nijeriya, Kano, Jami'ar Bayero.
Bunza, A. M. (2002). Rubutun Hausa: Yadda Yake Da
Yadda Ake Yin Sa Don Masu Koyo Da Koyarwa. Lagos: Ibrash Islamic Publications
Centre LTD.
Bunza, A. M. (2001). "Kamanci da Kwatanci cikin
Asirran Tsibbu," Hausa Studies: Readings in Hausa Language, Literature and
Culture. Vol. III, no. 3. Department of Nigerian Languages, Kano: Bayero
University.
Bunza, A. M. (2000). "Naƙali a Tsibbace: Nazarin Naƙalin
Sarrafa Ayoyin Alƙur'ani a Tsibbace,"
"Malam": Journal of Languages and Linguistics. Department of Arabic,
Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo University.
Bunza, A. M. (1998). "Malam: Nazarin Siffofi da
Kamalar Malami a Idon Bahaushe," Al-Nahadah: A Journal Islamic Heritage.
Centre for Islamic Studies, Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo University.
Ɗangambo, A. (1984). Rabe-Raben
Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Sashen Harsunan Nijeria.
Kano: Jami'ar Bayero.
Ɗanmaigoro, A. (2010).
"Sana'o'in Hausawa Da Fulani", Al'adu da Ɗabi'un Hausawa da Fulani. Kaduna: El-Abbas Printers and Media
Concepts.
Ɗantumbushi, A. M. (2009).
"Matasyin Ilimi da Tarbiyya a Rayuwar Bahaushe Jiya da Yau." Himma
Journal of Contemporary Studies. Vol. 1, No.1. Department of Nigerian
Languages, Katsina: Umaru Musa Yar'adua University.
Denis, P. (1996). Economic and Humanism: from
Communitarian Utopia to Struggle on Behalf of the Third World. Paris: Les
Editions du Cerf.
Gada, A. M. (2010). A Short History of Early Islamic
Scholarship in Hausaland. Department of Islamic Studies, Sokoto: Usmanu
Danfodiyo University.
Galadanci, M.K.M da Wasu (2011). Hausa Don Ƙananan Makarantun Sakandare Bugu na Biyu. Ikeja: Longman Nigeria
Plc.
Gusau, S. M. (2015). Mazhabobin Ra'i da Tarke a Adabi
da Al'adun Hausawa. Kano-Nigeria: Century Research and Publishing Limited.
Gusau, S. M. (2010). "Al'adun Hausawa a Taƙaice," Al'adu da Dabi'un Hausawa da Fulani. Kaduna:
El-Abbas Printer and Media Concepts.
Gusau, S. M. (2008). Dabarun Nazarin Adabin Hausa.
Kano-Nigeria: Benchmark Publishers Limited.
Gusau, G. U. (2013). "Nazarin a Kan Rayuwar Sani
Sabulu na Kanoma da Waƙoƙinsa," Zauren Waƙa Journal
of Hausa Poetry Studies. Vol. 1, No.1, September, 2013. Department of Nigerian
Languages, Sokoto: Usmanu Danfodiyo University.
Horgan, M.O. (2006). Dictionary of Sociology. New
Delhi: Academic (India) Publishers.
Jami'ar Bayero (2006). Ƙamusun Hausa. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Kano: Jami'ar
Bayero.
Jegede, A. et al (2013). Macmillan Brilliant Primary
Social Studies 6. Lagos: Macmillan Nigeria Publishers Ltd.
Langacker, R.W. (1973). Language and Its Structure:
Some Fundamental Linguistic Concepts. Second Edition. New York: Harcourt Brace
Jovanovich.
Madauci, I. et al (1982). Hausa Customs. Zaria:
Northern Nigerian Publishing Company.
Malumfashi, I. (2009). Adabin Abubakar Imam. Sokoto:
Garkuwa Media Services Ltd.
Mamman, M. (2012). "Bahaushe Mai Ban
Sha'awa," Champion of Hausa Cikin Hausa: A Festschrift in Honour of Ɗalhatu Muhammad. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.
Nasarawa, S. H. (1997). "Gardanci." Kundin
Bincike Don Neman Digiri Na Farko, Sashen Harsunan Nijeriya, Sakkwato: Jami'ar
Usmanu Ɗanfodiyo.
Mu'azu, A. (2014). "Ceto Hausa a Ƙasar Hausa," Garkuwan Adabin Hausa: A Festschrift in
Tribute to Abdulƙadir Ɗangambo. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.
Otite, O et al (1981). An Introduction to
Sociological Studies. Ibadan-Nigeria: Heinemann Educational Books (Nig) Ltd.
Odenham, J. (1980). "The Diploma Disease
Revisited: Ronald Dore", IDS Bulletin 11.2. Vol.11, No. 2. Institute of
Development Studies.
c/users/user1/downloads/nlh%202018%result/dore11.2final.pdf
Radda, S. I. (2014). "Gambu and Categorization
of Crimes in his Songs," Garkuwan Adabin Hausa" A Festschrift in
Tribute to Abdulƙadir Ɗangambo. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Salawu, A. A. (2000). "Introduction to Guidance
and Counselling." Readings in Education. Vol.1. Sokoto: The Path Sokoto
State Newspaper Company.
Sallau, B. A. (2013). Wanzanci da Sauye-Sauyen
Zamani. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Sarɓi, S. A. (2011). "Yaɗuwa da Muhimmancin Harshen Hausa a Duniya," Himma Journal
of Contemporary Hausa Studies, Vol.3, October, 2011. Zaria: Ahmadu Bello
University Press Limited.
Umar, A. (2020). "Perceptual Disposition of
Parents, Teachers and Students on the Integration of Qur'anic System in Gombe
State, Nigeria: Implications for Curriculum Planning," Danmarna
International Journal of Multi-Disciplinary Studies. Katsina: Umaru Musa
Yar'adua University.
Umar, M. B. (1987). Dangantakar Adabin Baka da
Al'adun Gargajiya. Kano: Kamfanin Triumph.
Walford, G. (1998). "The Diploma Disease:
Education, Qualification and Development by Ronald Dore", Assessment in
Education: Principles, Policy and Practice. Vol. 4, no. 1. Oxford Review of
Education: Taylor and Francis Ltd. https:www.jstor.org/stable/1050987.
Yahaya, I. Y. (1988). Hausa a Rubuce: Tarihin
Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zariya: Kamfanin Buga Littattafai na Nijeriya ta
Arewa.
'Yartsakuwa, S. D. da wani (2000). "Nazari a kan
Sana'ar Damfara a Sakkwato." Sashen Hausa, Sakkwato: Kwalejin Ilimi ta
Shehu Shagari.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.