Ticker

6/recent/ticker-posts

Mahaifiyana Ta Umurce Ni Na Aske Gemuna

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum wa rahmatulLah. Malam ina da tambaya. Na kasance ina kiyaye bin Sunnah kuma duk wani biyayya ina yi wa mahaifiyar mu, sai dai abu ɗaya tak naki na yi mata biyayya akai, tace min na aske gemuna, nace mata ta yi hakuri ba zan iya askewa ba, wallahi malam buɗewar bakin mamanmu tace min in ban aske ba, ba zan ga da-kyau ba. Ina tsoro kar bakinta ya kama nii. Shin zai iya askewa malam?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikis salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.

A’a, bai halatta ka aske gemu ba koda mahaifiyarka ya umarce ka da yin hakan. Babu biyayya ga halitta cikin saɓon Mahalicci.

A koyarwar Musulunci, barin gemu yana cikin abubuwan da Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya umarci maza su yi, kuma aske shi baki ɗaya haramun ne ko kuma abin kyama mai karfi a gun mafi yawan malamai.

Babu shakka Allah shi ne yayi umurni kuma ya wajabta ma bayinsa muminai yin biyayya da kyautatawa ga mahaifansu. Allah ya ce a cikin Suratul Isra'i:

وَقَضٰى رَبُّكَ اَلَّا تَعۡبُدُوۡۤا اِلَّاۤ اِيَّاهُ وَبِالۡوَالِدَيۡنِ اِحۡسَانًا ؕ اِمَّا يَـبۡلُغَنَّ عِنۡدَكَ الۡكِبَرَ اَحَدُهُمَاۤ اَوۡ كِلٰهُمَا فَلَا تَقُلْ لَّهُمَاۤ اُفٍّ وَّلَا تَنۡهَرۡهُمَا وَقُلْ لَّهُمَا قَوۡلًا كَرِيۡمًا‏

Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi, kum game da mahaifa biyu ku kyautata kyautatawa, ko dai ɗayansu ya kai ga tsũfa a wurinka ko dukansu biyu, to, kada ka ce musu 'tir' kuma kada ka tsãwace su kuma ka faɗa musu magana mai karimci. (Surah: Al-Israa, Aya ta 23).

Kuma Manzon Allah (sallal Lahu 'alaihi wa aalihi wa sallam) ya ce "YARDAR ALLAH TANA CIKIN YARDAR MAHAIFA". Wato duk wanda ke neman yardar Allah, to zai sameta ta cikin samun yardar mahaifansa.

To amma duk wannan biyayyar da kyautatawar da Allah yayi umurni da ayi musu, awani wajen kuma ya ce idan suka kiraka zuwa ga saɓa ma Allah kada ka bisu akan haka. Don haka biyayya garesu tana takaituwa ne akan duk abin da ba Saɓon Allah bane. Shi kuwa aske gemu da gangan Saɓon Allah ne tunda Manzo (sallal Lahu 'alaihi wa aalihi wa sallam) yayi umurni acika gemu a cikin wani hadisi ingantacce wanda Imamul Bukhariy da Imamu Muslim suka ruwaito, ya ce : "KU SAISAYE GASHIN BAKI (WATO KU RAGESHI SAMA-SAMA) AMMA KU CIKA GEMU".

A cikin wani hadisin kuma wanda Imami Muslim ya kebanta da riwayarsa, Manzon Allah (sallal Lahu 'alaihi wa aalihi wa sallam) ya faɗi dalilin umurnin. ya ce : "KU SAISAYE GASHIN BAKI KUMA KU CIKA GEMU DOMIN KU BAMBANTA DA MAJUSAWA (WATO MUSHRIKAI MASU BAUTAR WUTA).

Malamai da yawa sun hakaito Ijma'in Maluman mazhabobin Musulunci baki ɗaya bisa wajibcin kiyaye wannan umurnin da kuma haramcin aske gemu. Misali kamar abin da Ibnul Muflihi ya hakaito daga Imam Ibnu Hazmin Al Andalusiy (rahimahul Lahu). Kuma yardar Allah da Manzonsa ita ce gaba da yardar Iyaye. Don haka bin umurnin iyaye yana wajabta ne idan ya dace da umurnin Allah da Manzonsa. Amma idan aka samu saɓani tsakanin umurnin mahaifa da kuma umurnin Allah da Manzo (sallal Lahu 'alaihi wa aalihi wa sallam), to umurnin Allah ɗin ake bi a kyale umurnin iyayen. Tunda Manzon Allah (sallal Lahu 'alaihi wa aalihi wa sallam) ya ce : "BABU BIYAYYA GA WANI MAHALUKI CIKIN SAƁA WA MAHALICCI".Wato kada kabi umurnin wani (ko waye, koda malamai ko iyaye) mutukar akwai Saɓon Allah a cikin bin umurnin nasu.

Don haka kaci gaba da kyautata wa mahaifiyarku tare da tausasa harshe gareta a cikin duk furucin da zai fito daga bakinsa. Koda kuwa ita ta gaya maka abin da bai maka dadi ba. Domin kuwa Allah ya ce "KA GAYA MUSU ZANCE MAI DADI (CIKIN LADABI DA GIRMAMAWA). Mutukar ka kiyaye da wannan, to in sha Allahu babu wani mummunan abu da zai sameka, sai dai ma alkhairi mai yawa ya biyo baya.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

  ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments