𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam khamis barka da yamma, da fatan ka wuni lafiya. Allah Ya saka maka da mafificin alkahiri. Mene ne ma'anar sunan Rahmah ko Rahmatullah da Rahima ko Rahimatullah. Na gode
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
A cikin Alƙur'ani mai girma, kalmomin
RAHMAH da RAHIMAH ba su zo a matsayin sunayen mata na mutane ba. Maimakon haka,
sun fito ne a matsayin siffofi na Ubangiji (Allah) da kuma ma'anonin jinkai da
tausayi.
Sunan RAHIMATULLAH da
RAHMATULLAH sunayen sun samo asali daga harshen Larabci, kuma suna nufin
"RAHAMAR ALLAH" ko kuma "ALHERIN ALLAH". Sunayen sun kunshi
kalmomi guda biyu ne da aka haɗa su wuri guda: RAHIMAH da RAHMAH, idan aka haɗa da ALLAH, yana zama
"RAHMATULLAH ko "RAHIMATULLAH".
Kalmar
"RAHMAH" na ɗaya daga cikin
kyawawan siffofin Allah, kuma tana nuna tsananin tausayi, jinƙai, da falalar
Ubangiji ga bayinsa. Kalmar Larabci ce ta "RAHMAH" tana nufin Rahama
ko Jinkai ko Tausayi. RAHMATULLAH Tana nufin "RAHAMAR ALLAH".
RAHIMATULLAH: Wannan
kuma ya samo asali ne daga kalmar "RAHIMAH" wacce take nufin mai
yawan rahama. Kalmar ta samo asali ne daga AR-RAHIM wanda yana ɗaya daga cikin
kyawawan Sunayen Allah 99 (ASMA'UL HUSNA) wanda ke nufin "MAI JINKAI NA
MUSAMMAN".
RAHIMATULLAH da
RAHMATULLAH akwai bambanci tsakanin sunayen biyu. Duk da cewa sun fito daga
asali ɗaya na Larabci mai
ma'anar Rahama ko Jinƙai, amma kowanne yana da nasa tsarin da kuma ma'anar.
RAHMAH Kalma ce ta
asali a cikin harshen Larabci da ke nufin "Jinƙai". RAHĪMAH
Wannan kuma siffa ce ko kuma sunan da aka dafa shi daga kalmar RAHMAH (wato
nau'in Ism Fā'il). Ma'anarsa ita ce "Mai Jinƙai" ko "Mai
Tausayi". A taƙaice, RAHMAH tana nufin jinƙai da kanta, yayin da
RAHIMAH ke nufin wacce take da jinƙai ko wacce take
tausayawa.
An fi amfani da sunan
a matsayin ABDUR-RAHMAN (Bawan Mai Rahama) ko ATIYATULLAH (Kyautar Allah). Sai
dai a matsayin RAHIMAHULLAH, a kan yi amfani da shi wajen yin addu'a ga
magabata na kwarai, idan aka ambaci sunansu sai ace: RAHIMAHULLAH wanda ke
nufin: Allah ya yi masa rahama. Sunan ya shahara a matsayin lakabi ko kirari ga
mutane masu matsayi, kamar yadda tarihi ya nuna a cikin littattafan Musulunci. Hakanan,
"ABDUR-RAHMAN" (Bawan Mai Rahama) na daga cikin shahararrun sunaye
tun zamanin Sahabbai.
Kalmar RAHMAN da
RAHIM da kuma RAHMAH (wadanda suke tushen sunan RAHMATULLAH) sun zo a cikin Alƙur'ani sau 114. Duk
da cewa babu wani abu mai suna "RAHMATULLAH" a matsayin mutum a cikin
Alƙur'ani,
kalmar tana nufin Rahamar Allah. Sunan RAHMAH da RAHIMAH sun zo a cikin ayoyi
da dama na Alƙur'ani don bayyana fadin jinkan Allah ga bayinsa:
بِسْمِ
اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
"Da sũnan Allah,
Mai rahama, Mai jin ƙai. "
A cikin BISMILLAH:
Wannan suna yana fitowa a farkon kowace surah ta Alƙur'ani (in ban da
Suratut Tawbah).
Kalmar tana yawan
zuwa tare da gafara, misali a cikin Suratul Baƙarah Aya ta 163:
هُوَ
الرَّحْمَٰنُ الرَّحِيمُ
"Shi ne Mai
rahama, Mai jin ƙai".
ۖ وَرَحْمَتِي وَسِعَتْ كُلَّ
شَيْءٍ ۚ
"Rahamata ta
yalwaci dukkan komai. " (Suratul A'raf Aya ta 156).
Ana kiran Annabi
Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) da siffar rahma ga talikai:
وَمَا
أَرْسَلْنَاكَ إِلَّا رَحْمَةً لِلْعَالَمِينَ
"Kuma ba Mu aike
ka ba fãce dõmin wata rahama ga talikai. " (Suratul Anbiya Aya ta 107).
A al'adar Hausawa da
ma duniya baki ɗaya, ana raɗawa yara mata waɗannan sunaye (RAHMAH
ko RAHIMAH) domin yin kyakkyawan fatan samun jinkai da albarkar Ubangiji a
rayuwarsu. Addinin Musulunci ya ba da damar amfani da kalmar "RAHIM"
ko "RAHIMA" ga ɗan adam saboda
sifface ta tausayi da mutum ma zai iya siffantuwa da ita (kamar yadda Allah ya
siffanta Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) da cewa shi mai tausayi ne da
jinkai "RA'UFUR RAHIM" a Suratut Tawbah).
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa. . .
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.