Ticker

6/recent/ticker-posts

Ma'anar Sunan Lantana

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam KHAMIS. Allah ya kara lafiya da tsawon kwana malam tambaya ta ita ce mene ne ma'anar sunan LANTANA kuma shin ya halatta sanya wa yariya sunan?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.

Sunan LANTANA ya samo asali ne daga tsagin wata ayar Alƙur'ani mai girma (daga Suratu A'ali Imran, Aya ta 92), inda Allah Ta'ala yake cewa:

لَنْ تَنَالُوا الْبِرَّ حَتَّىٰ تُنْفِقُوا مِمَّا تُحِبُّونَ ۚ وَمَا تُنْفِقُوا مِنْ شَيْءٍ فَإِنَّ اللَّهَ بِهِ عَلِيمٌ

MA'ANA: "Bã zã ku sãmi kyautatãwa ba, sai kun ciyar daga abin da kuke so. Kuma abin da kuka ciyar, kõ mne ne, to, lalle ne Allah, gare shi, Masani ne.

LANTANA Kalmar na nufin "BA ZAKU SAMU BA"

A saboda haka, malamai sun bayyana cewa ba sunan da ya dace a rika amfani da shi wajen radawa 'ya'ya mata ba ne, ba ta da wata kyakkyawar ma'ana ta sunan mutum. Hasali dai an yankoshi ne daga sashen wasu kalmomin wani hizifin Alƙur'ani bisa riwayar Imamu Warshu daga Ƙira'ar Imam Nafi'u dan Abdurrahman Almadaniy (rah). Kuma Babu wata mace mai irin wannan suna a cikin tarihin Musulunci tun daga matayen Annabawa har zuwa Sahabbai ko magabata na kwarai.

Sanya wa yaro sunan wata surar Alƙur'ani ko kan wani hizifi, bidi'ah ce wacce mutane suke yinta ba tare da wani dalili ko hujjah ba. Idan kuma masu yin hakan suna yi ne domin bayyanar da soyayyarsu ga Alƙur'ani, to ai har yanzu bamu kai Sahabbai da magabata tsananin son Alƙur'ani ko aiki da shi ba. Amma ba'a ruwaito cewa wani daga cikinsu ya taɓa sanya wa 'ya'yansa irin waɗannan sunayen ba.

Abinda yafi dacewa ga mutum duk lokacin da zai sanya wa yaro ko yarinyarsa suna, shi ne yayi koyi da wasiyyar Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) wanda yace "Fiyayyen sunaye sune waɗanda aka raɓa zuwa ga Abdu (kamar su ABDULLAHI (bawan Allah) ko ABDURRAHMAN (Bawan Mai Rahama) ko kuma waɗanda aka raɓa da sunayen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) kamar su MUHAMMAD: (Wanda aka yaba kwarai) AHMAD: (Wanda ya fi kowa yabon Allah. MAHMUD: (Abin yabo). " Wannan na daga cikin kyawawan halaye na sanya wa yaro suna a Musulunci.

Wato shi dai kyautata wa yaro sunansa, yana daga cikin hakkokin da yake dasu akan iyayensa. Don haka abinda yafi dacewa shi ne ka jingina sunan yaronka zuwa ga sunan Ubangiji, ko kuma ka jinginashi zuwa ga sauran sunaye daga sunayen Allah ɗin nan guda 99. Ko kuma ka sanya masa irin sunayen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ko sunan wani Annabi daga cikin Annabawa (alaihimus salam) ko irin sunayen Sahabbai (radhiyal-Lahu anhum) ko sunayen wasu daga magabata da salihan bayin Allah.

Idan kuma 'Ya mace ce ka kyautata sunanta ka sanya mata daga sunayen mataye mafiya daraja aduniya. Wato FATIMAH, ko KHADIJAH, ko MARYAM Ko kuma daga sunayen Iyaye ko Matayen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam). Kamar AMINATU, HALIMATU, A'ISHATU, ZAINAB, MAIMUNATU, SAFIYYATU, da sauransu.

A takaice dai ana sanya wa yaro suna ne domin nema masa albarkar ainihin masu irin wannan sunan. Ba wai don birgewa ko alfahari ba. Amma kada ka biye wa son zuciya ka sanya wa yaronka ko yarinyarka wani suna marar ma'ana ko marar tushe. Irin yadda yawancin iyayen zamani sukeyi idan sun samu haihuwa burinsu shi ne su sanya wa yaro wani baƙon suna wanda babu mai irinsa a unguwar ko a danginsu.

Daga karshe, ba a so a sanya wa yariya sunan "LANTANA". Malaman addini sun bayyana cewa sunan ba shi da wata kyakkyawar ma'ana. An ciro shi ne daga wani ɓangare na wata aya a cikin Alƙur'ani, kuma yana nufin "BA ZA KU SAMU BA".

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa. . .

  ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments