Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Mai Zuwa Zance Wandon Shi Ya Jike

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Aslm Dr tambaya nake da shi Dan Allah saurayina ne kullum idan ya xo hira wajena ko ahannuna ya kama ko mukayi Wani Dan hira haka akan junanmu to se ya ji wandonsa ya baci ya yi inzali shi ne yake neman temoko ko akwai Wani mgananin da ze Yana Sha abun ya dena fita Dan Yana damunsa sosai Kuma Yana yawan msa inde munyi hira ko yadan taba hannuna haka pls atemaka masa Yana ganin kaman ba lfy bane nagode Ina jiran amsanka

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu.

Amma dai ina fatan kin sani cewa haramun ne amatsayinki na budurwa ki tsaya kina furta duk wani zancen da zai motsa sha'awa tsakaninki da duk wani saurayi ko ta hanyar waya ko chatting ko zance gaba da gaba, juma koda anyi miki baiko da wannan saurayin, mutukar dai ba'a daura miki aure dashi ba.

Allah maɗaukakin sarki idan ya haramta wani abu yakan haramta dukkan wata hanya komai kankantarta da zata kai zuwa ga aikata wannan abun. Saninmu taɓa jikin mace babbar hanya ce wadda ke motsar da sha’awa zuwa ga aikata zina.

A cikin addinin Musulunci, haramun ne ga mace ko namiji da ba su da aure su taɓa juna ko shiga cikin irin wannan yanayi da zai iya jawo sha’awa ko aikata zina. Wannan yana daga cikin manyan laifuka da ake yi wa mutane gargaɗi sosai a cikin Alƙurani da Hadisai.

وَلَا تَقْرَبُوا الزِّنَا ۖ إِنَّهُ كَانَ فَاحِشَةً وَسَاءَ سَبِيلًا

“Kada ku kusanci zina; lallai ita alfasha ce kuma mummunan hanya.”

(Suratul Isra’i, 17:32)

Kusantar zina yana nufin duk wani abu da zai kai ga aikata zina, ciki har da taɓa juna, kallon sha’awa, ko shiga cikin yanayi na sha’awa.

Hadisin Manzon Allah صلى الله عليه وسلم An karɓo daga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم cewa: “Idan ɗayanku ya taɓa mace da hannunsa, to ya riga ya aikata laifi.” (Tirmidhi da Abu Dawud) ana magana game da wadanda babu aure tsakaninsu ko taɓa matar da haramunne ka taɓa ta.

Hadisi ya tabbata wanda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam Yace: Abuga Narkakkiyar kusar wuta ta bakin karfe akan ɗayanku shi yafi masa alkhairi akan ya shafi jikin macen da bata hallata agareshi ba. Albany yace hadisine ingantacce acikin sahihul jami’ul kabeer (5045).

Abinda ke fita ajikin mace ko namiji ta dalilin motsawar sha'awa ana kiransa Maziyyi ne. Fitarsa bata wajabta wanka, sai dai wajibi ne awankeshi kuma awanke duk abinda ya taɓa. (Misali kamar Underwears).

Akwai dokoki waɗanda idan aka kiyaye su hakan bazata faruba:

1. Shigar da mace zata fito wajen saurayi.

2. Kalaman da za suyi.

3. Samun fuska a wajen mace da saurayi ya ke samu.

4. Idan zatazo zance tazo da muharramanta.

5. Idan za ayi Hirar ayita a sarari, ba'a lungu ba ko kwararo.

Da sauran abubuwa makamantansu.

ALLAH YA SHIRYA MU AMEEN

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

 ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments