Ticker

6/recent/ticker-posts

Niyyar Daukar Azumi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Yaya ake niyyar ɗaukar azumi baki ɗaya? Shin niyya ɗaya ta wadatar ko sai an sake niyya a kowace dare?

NIYYAR ƊAUKAR AZUMI

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Ana ɗaukar niyyar azumi kafin fitowar alfijir, idan azumin farilla ne saboda hadisin da Nana Hafsa ta ruwaito daga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: "Wanda bai ɗauki niyyar azumi da dare ba (kafin fitowar alfijir) bashi da azumi." Shaikh Nasiruddīn Albani ya ingan tashi a cikin Sahih Jāmi’us Saghīr.

Ita kuma “Niyya (niyyah) tana nufin yanke hukunci. Yana da mahimmanci a yi niyyar azumi a daren da ya gabata, da sauran darare a cikin Ramadan. (Fatawa al-Lajnah al-Daimah, juzu'i na 10, shafi na 246).

“Wasu malamai sun tafi a kan cewa idan aka yi ibada, to ya wadatar a yi niyya sau ɗaya a karon farko, sai dai idan an katse jerin maimaitawar ibadar, to dole ne a yi wata sabuwar niyya. A kan haka ne idan mutum ya kasance yana da niyyar yin azumin ranar daya ga watan Ramadan, to zai azumci wannan wata gaba ɗaya, to wannan ya isa ya cika watan baki ɗaya da niyya ɗaya, matukar bai samu wani uzuri da ya sa ya sha azumi ba, da haka ne idan mutum ya sha azumi a wani wuni ɗaya, to wancan niyyar ta sa ta karye, sai ya sake sabuwa, kamar matafiyi, idan ya dawo kuma ya so ya ci gaba da azumin sai ya sake yin niyyar azumi. Wannan shi ne mafi ingancin magana, domin dukkan Musulmi idan ka tambaye su, za su ce sun yi niyyar azumtar watan ne daga farkonsa zuwa karshensa. Don haka ko da ba a yi niyya a zahiri ba, tana nan ta hanyar ma’ana, domin ka’ida ta asali ita ce wannan aikin bai tsaya ba. Don haka sai mu ce idan ya karya azumi saboda wasu halaltattun dalilai, to mutum ya tashi dora yin azumi, dole ne ya sabunta niyya. Wannan shi ne ra’ayin da ya fi kawo kwanciyar hankali.”

Niyyar Kowace Ibada Iri Guda ce! Niyya Ana Kudirtawane A Zuciya ba a Faɗin Yin Wani Aiki Na Ibada Da Baki A Matsayin Niyya Kamar Yadda Wasu Keyi Hakan Kuskure Don Bahaka Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam Yakeyin Niyyarsaba, Kudirce Abu A Zuciya Shi ne Niyya (Dazarar Ka Gabato Yin Wata Ibada Saikasa A Ranka Ga Irin Ibadar Dakazoyi Shikenan Niyyarka Tashiga, Dazarar Ka Miki Ko Katafi Zuwa Wata Ibada Shikenan Niyyarka Ta Shiga), Don Haka Niyya Ba Wani Abu ne Me Wahalaba Kamar Yanda Wasu Ke Ɗauka.

ALLAH NE MAFI SANI

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ƘARIN BAYANI

YAYA AKE YIN NIYYAR AZUMIN RAMADAN, KUMA SHIN NIYYA GUDA ƊAYA TA WADATAR GA DUKAN WATAN?

Tambaya:

Mafi yawan musulmi suna fuskantar fargaba game da niyya, wasu suna ganin dole sai sun furta wasu kalmomi na musamman, wasu kuma suna tsoron idan suka manta ba su yi niyya a wani dare ba azuminsu ya ɓaci. Menene matsayar shari'a akan kulla niyya ga azumin farilla?

Amsa:

Hukuncin Niyya Da Yanayin Wadatar Ta Ga Dukan Watan

Niyya ita ce rukunin farko na kowace ibada. Manufarta ita ce rarrabe tsakanin al'ada da kuma ibada. A cikin azumi, niyya tana nufin kudirta ƙudurin barin ci da sha da sauran abubuwan da ke ɓata azumi tun daga ɓallar alfijir har zuwa faɗuwar rana, domin neman yardar Allah.

1. Niyya A Zuciya Take (Ba A Furta Ta)

Kuskure ne babba wanda wasu suke yi na furta niyya da baki (kamar cewa: "Na yi niyyar azumin gobe..."). Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) bai taba furta niyyar azumi ba, haka ma sahabbansa. Niyya aiki ne na zuciya.

Misali: Tashi da ka yi don yin suhur (sahur), wannan shi kansa niyya ce, domin ba za ka tashi cin abinci a wannan lokacin ba sai don kana nufin yin azumi.

Ka'ida: Duk wanda ya sani a ransa cewa gobe azumi ne kuma ya yi niyyar yi, to ya yi niyya.

2. Lokacin Yin Niyya (Azumin Farilla)

Ga azumin Ramadan ko duk wani azumin farilla (kamar ramako ko kaffara), dole ne mutum ya ƙulla niyyarsa kafin alfijir ya keto. Idan alfijir ya keto mutum bai yi niyya ba, to azuminsa bai inganta ba.

Daga Nana Hafsa (R.A), Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya ce:

مَنْ لَمْ يُجْمِعِ الصِّيَامَ قَبْلَ الْفَجْرِ فَلَا صِيَامَ لَهُ

Wanda bai ƙulla niyyar azumi ba kafin alfijir, to ba shi da azumi.” (Sunan Abu Dawud da Tirmidhi).

3. Shin Niyya Guda Ɗaya Ta Wadatar Ga Dukan Watan?

Wannan ita ce gabar da aka samu saɓani tsakanin malamai, kuma maganganun sun kasu kashi biyu:

A. Maganar Mafi Yawan Malamai (Jumhur):

Malaman mazhabar Shafi'iyyah, Hanbaliyyah, da Hanfiyyah suna ganin cewa kowace rana ibada ce mai zaman kanta. Saboda haka, wajibi ne a sabunta niyya a kowane dare na Ramadan. Idan mutum ya yi niyyar dukan watan a daren farko, hakan bai wadatar masa ba ga sauran kwanakin; dole ne ya rika kudirta niyya a kowane dare.

B. Maganar Mazhabar Malikiyyah (Da Wasu Malaman Tahkiƙi):

Malaman Malikiyyah suna ganin cewa azumin Ramadan ibada ce guda ɗaya wadda aka haɗa ta (Integrated Worship). Saboda haka, niyya guda ɗaya da mutum zai yi a daren farko na Ramadan cewa zai azumci daukacin watan, ta wadatar masa har zuwa ƙarshen watan.

Wannan zance shi ne mafi sauƙi da kuma kawo kwanciyar hankali, domin yana kare mutum daga waswasi ko kuma mantuwa. Sai dai akwai sharaɗi guda ɗaya:

Sharaɗi: Idan mutum ya samu wani uzuri da ya sa ya katse azumin (kamar rashin lafiya, tafiya, ko jinin haila ga mata), to idan zai sake ci gaba, dole ne ya sabunta sabuwar niyya. Domin wancan jeri na azumi da ya yi niyya a farko ya riga ya katse.

4. Fa'idar Niyya Guda Ɗaya

Daga cikin manyan fa'idojin bin maganar Malikiyyah akan niyya guda ɗaya shi ne: Idan mutum ya yi niyya a daren farko, sai ya kasance a wani dare ya yi barci bai tashi ba sai bayan alfijir ya riga ya keto, to azuminsa na wannan ranar ya inganta, domin wancan niyyar ta farko tana nan tana aiki a kansa.

5. Ta Ina Niyya Take Karyewa?

Niyyar azumi tana karyewa ne idan:

Mutum ya yi niyyar daina azumi (ko da bai ci komai ba).

Mutum ya samu uzurin da ya sa ya sha azumi (rashin lafiya, tafiya, haila).

Watan ya ƙare.

Kammalawa

Mafi ingancin bayani shi ne musulmi ya kudirta a zuciyarsa a daren farko na Ramadan cewa zai azumci daukacin watan. Bayan hakan, duk tashi da zai rika yi don suhur, ko shirin da zai rika yi don gobe azumi ne, duk wannan yana ƙara ƙarfafa niyyarsa ne. Shari'ar Musulunci mai sauƙi ce, ba ta buƙatar takura wa kai wajen neman kalmomin da za a furta.

Allah ya karɓi azuminmu da sauran ayyukanmu na kwarai.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments