Ticker

6/recent/ticker-posts

Lokacin Shiga Da Fita I'tikafi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Yaushe Mai I'itikafi Yakamata Yashiga Ittikafi Yaushene Kuma Yakamata Yafita?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Lokacinda mutum zai fara shiga ittikafi jamhurdin malamai suntafi akan cewa zai shiga kafin faɗuwar ranar daren ashirin da ɗaya daka cikin Malaman akwai malaman mazhabobin nan guda huɗu (Abu hanifa da malik da shafi'i da Ahmad) sun kafa hujjah da dalilai masu yawa daka cikinsu akwai:

1. Ya tabbata daka Annabi sallallahu Alaihi wasallam yana yin i'itikafi agoman karshe na Ramadan. Bukhari/ Muslim. Wannan yana nuna yana i'ikafin dararen ne bawai wuni ba, domin goma tana tan-tance dararene, Allah maɗaukakin sarki ya ce:

وَلَيَالٍ عَشْرٍ

Ina rantsuwa da darare goma (suratul Fajr ayat ta 2)

Goman karshe suna farawane daka daren ashirin da ɗaya. Abisa wannan Mai i'itikafi zai shiga masallaci kafin faɗuwar ranar ashirin da ɗaya na Ramadan.

2. Suka ce: Mafi girman makasudin i'itikafi shine dacewa da lailatul qadri, daren ashirin da ɗaya kuma yana cikin kwanakin wutiri wanda yana iya kasancewa daren lailatul qadri, yakamata yakasance Mai i'itikafi yashiga i'itikafi a cikinsa. Almugni (4/489).

Saidai bukhari da musulim sun ruwaito hadisi daka Ummuna A'isha yardar Allah takara tabbata agareta tace: (Annabi sallallahu Alaihi wasallam yakasance idan ya ɗau niyyar yin i'itikafi yana shiga i'itikafin dazarar an kammala sallar asubahi) Wasu magabata sun kafa hujjah da zahirin wannan hadisin, cewa mutum zai shiga i'itikafinne bayan sallar asuba, kuma wannan itace maganar da malaman lajnatul da'imah suka ɗauka (10/411).

Saidai jamhur ɗin malamai sun amsa musu dangane da wancan hadisin da jawabai guda biyu:

1. Nafarko: Annabi sallallahu Alaihi wasallam yakasance dama yashiga i'itikafin tun kafin faɗuwar rana, amma bai shiga keɓantaccen gurin i'tikafin ba sai bayan sallar asuba.

Imamun nawawi ya ce: Ya kasance (Idan ya yi nufin shiga i'itikafi da ya yi sallar asuba sai ya shiga i'tiikafinsa) Masu cewa mutum zai fara i'itikafine afarkon rana sun kafa hujjah dashi, daka cikinsu akwai, Auza'i da Assauri, da kuma Allaith adaya daka ciki maganganunsa, Malik da Abu hanifa da shafi'i da Ahmad, suka ce: zai shiga kafin faɗuwar rana, idan ya yi niyyar i'itikafin wata guda ko kwana goma, sun fassara wancan hadisin da cewa: Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam dama yariga yashiga i'itikafin, saiya yankeshi, saiya keɓe kansa bayan sallar asuba bawai lokacinne yashiga ba, dama can yana cikin i'itikafi tun kafin magariba azaune a cikin masallaci da ya yi sallar asuba, saiya keɓance kansa.

2. Na biyu: Alqazi Abu ya'ala yana cikin malaman hanabila shine ya amsa ya ce: dama Annabi sallallahu Alaihi wasallam yana haka aranar ashirin ga wata, Assundi ya ce: Wannan jawabin shine zai fa'idantar shi ya fi kuma shine abun dogara sama da sauran.

lokacin fita daka i'itikafi shine: Mutum zai fita akarshen ranar ranakun Ramadan. Yazo afatawar lajnatul da'imah (10/411). I'itikafin kwanaki goman Ramadan yana karewa ne idan Ramadan yakare, Ramadan yana karewa ne da faɗuwar ranar daren idi. Idan mutum ya zaɓi zai zauna har zuwa ayi sallar asuba yafita zuwa sallar idi babu laifi, wasu daka cikin magabata sun so mutum ya yi hakan.

Imamu malik rahimahullah ya ce: yaga wasu daka cikin magabata idan sukayi i'itikafi agoman karshe na Ramadan basa komawa ga iyalansu harsai anyi sallar idin karamar sallah dasu, malik ya ce: bayanin haka yasameni daka ma'abota falalar dasuka gabata, wannan shine abunda ya fi soyuwa agareni cikin abunda naji.

Imamun Nawawi a cikin Almajmu'u(6/323) ya ce: Shafi'i da dalibansa suka ce: Duk wanda yakesan koyi da manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam, awajan i'itikafi agoman karshe na Ramadan, yakamata ya shiga masallaci kafin faɗuwar ranar daren ashirin da ɗaya na Ramadan, dan kada wani abu daka cikinsa ya kubuce masa, ya kuma fita bayan faɗuwar ranar daren idi, duka watan ya yi ko wani yanki na watan, Abunda ya fi shine yazauna daren idi harsai anyi sallar idi dashi, ko yafita daka i'itikafin amma yawuce zuwa sallar idi, idan ba'a masallacin daya yi i'itikafin ake idin ba.

Idan dazarar mutum yafita daka i'itikafi wajan idi zaitafi, Anso ya yi wanka yaci Ado kafin tafiya idin, domin yin hakan yana cikin sunnonin idi.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments