Citation: Bashir, A. & Abubakar, M. (2026). Tasirin karin harshen ‘yan gudun hijira a kan Hausar garin Ƙauran Namoda, Jihar Zamfara. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, 5(2), 34-41. www.doi.org/10.36349/tjllc.2026.v05i02.005.
TASIRIN KARIN
HARSHEN ‘YAN GUDUN HIJIRA A KAN HAUSAR GARIN ƘAURAN NAMODA, JIHAR ZAMFARA
Daga
Abdullahi Bashir
Sashen Harsuna da Al’adu
Jami’ar Tarayya Gusau
+234 803 648 1158
abdullahi.bashir@fugusau.edu.ng
Da
Mustapha Abubakar
Ɗalibi a Sashen Harsuna da Al’adu
Jami’ar Tarayya Gusau, Jihar Zamfara
+234 814 111 2741
Tsakure
A ’yan shekarun nan, matsalar tsaro a wasu sassan Arewa maso
Yammacin Nijeriya ta haifar da yawaitar ’yan gudun hijira zuwa garuruwa daban-daban
waɗanda suke zaune lafiya kamar a cikin garin Ƙauran Namoda. Wannan hijira ta zo da sauye-sauye masu yawa,
ciki har da na zamantakewa da tattalin arziƙi da kuma harshe. Wannan bincike ya nazarci tasirin karin
harshen ’yan gudun hijira, musamman waɗanda suka taso daga yankunan ƙasar Shinkafi (Arewacin garin Ƙauran Namoda) da kuma waɗanda suka fito daga yankin ƙasar Zurmi (Arewa Maso-Gabas da garin Ƙauran Namoda) da kuma wani yanki na ƙasar Birnin Magaji (Gabas da garin Ƙauran Namoda). Sai kuma na wasu ƙauyuka da ke kudancin garin na Ƙauran Namoda duk a cikin jihar Zamfara, inda suka shigo da wannan
baƙon karin
harshe zuwa garin Ƙauran
Namoda, a yayin da suke neman mafaka don gudun tsira daga matsalar rashin tsaro
da suka fuskanta a muhallansu na asali. Hakan, ya yi matuƙar shafar wasu kalmomi ta fuskar ma’ana, musamman waɗanda ake amfani da su a Hausar garin ta asali wadda aka san su
da ita, watau Karin harshen Zamfarci, inda ake samun canjin ma’ana . An tattara
bayanai ta hanyar gani da ido, an yi tattaunawa da mazauna gari da ’yan gudun
hijira, tare da yin amfani da littattafan masana. Sakamakon binciken ya nuna
cewa, karin harshen ’yan gudun hijira yana da tasiri mai kyau da kuma ƙalubale ga harshen Hausar Kauran Namoda. Binciken ya bayar
da shawarwari a kan yadda za a ci gajiyar wannan sauyi ba tare da gurɓata harshen asali ba (Zamfarci), wanda ɗaya ne daga cikin kare-karen harsunan ƙasar Hausa.
Fitilun Kalmomi: Harshe, Karin Harshe, Walwalar Harshe, Gudun Hijira, Kauran
Namoda
1.0 Gabatarwa
Harshe wata muhimmiyar hanya ce ta sadarwa da ke haɗa mutane da al’umma. Ta hanyar harshe ne ake bayyana tunani,
al’adu da tsarin rayuwa. Duk wani sauyi da ya faru a cikin al’umma, kamar
hijira ko yaƙi, yakan shafi
harshe kai tsaye. Saboda haka, batun hulɗar
harsuna ya zama muhimmin fanni a nazarin ilimin harshe. A ’yan shekarun nan,
matsalolin tsaro sun tilasta wa mutane da dama barin muhallinsu domin neman
mafaka a wasu garuruwa. Wannan yanayi da ake kira gudun hijira yana haifar da
haɗuwar al’ummomi daban-daban masu harsuna ko karin harsuna
mabanbanta. Lokacin da waɗannan mutane suka zauna a wuri guda, harsunansu sukan yi
mu’amala da juna, wannan dalilin yakan haifar da sauye-sauye a harshen garin.
Garin Kauran Namoda, a Jihar Zamfara, yana daga cikin
garuruwan da suka karɓi ’yan gudun hijira daga wurare mabambanta. Wannan ya haifar
da ƙaruwar kare-karen harshe na Hausa,
wanda hakan yake da tasiri ga Hausar da ake amfani da ita a garin. Wannan
bincike ya mayar da hankali ne a kan nazarin wannan tasiri.
1.1 Karin Harshe
Karin harshe wata hanya ce da ake iya ganin bambanci a cikin
harshe ɗaya. Ana iya samun ‘yan bambance-bambance tsakanin masu
magana da harshe ɗaya. Babban abin burgewa shi ne, bambancin da yake tsakani
bai wuce haifar da rashin fahimta a tsakanin waɗannan
rukunan al’umma ba. Masana sun bayar da gagarumar gudummuwa wajen bayar da
ma’anar karin harshe. Greenbarg (1915) an ce: “karin harshe shi ne wanda ya saɓa wa daidaitaccen harshen da ake rubutawa”. Sai kuma Skinner
(1977) bincike ne da ya ce, za a iya kallon karin harshe “a matsayin wani
nau’in magana a cikin harshe ɗaya wanda ba shi
ne ainihin harshen ba”. Bugu da ƙari, Zarruk da wasu (1990 sh. 9) kuwa an bayyana ma’anar Karin
harshe da cewa, “wasu ‘yan bambance-bambancen lafazi ne da kalmomi da jumloli
tsakanin rukunin al’umma ko shiyyoyin ƙasa mai harshe ɗaya”.
Aikin Bello (2020) ya yi bayani ne a
kan abin da ya shafi karin harshen Hausa, sai dai masanin ya karkata ne ta
fannin furuci, watau yadda akan furta kalmomi a tsakanin kare-karen harsuna maƙwabtan juna musamman a nan ƙasar Hausa waɗanda suka bamabanta ta fuskar muhalli ko wuraren zama. A cikin littafin an
kawo yadda gaɓoɓin furuci sukan yi tasiri ƙwarai da gaske
daga wuri zuwa wuri, inda za ka ji akan furta kalmomi cikin yanayi daban-daban
wanda kuma hakan bai hana kalma ta tsira da ma’anarta ta asali idan aka koma ga daidaitacciyar Hausa.
Galadanci da wasu (1990) an bayyana Karin harshe a matsayin wani “tsari ne na
amfani da harshe, yadda masu magana da harshen suka bambanta da sauran ‘yan
uwansu duk da cewa suna gane tare da fahintar junansu”. Har ila yau, Sani (2009
sh. 2) aiki ne da ya yi ƙoƙarin bayyana Karin harshe da cewa, “wani nau’i ne daga cikin nau’o’in harshe ɗaya wanda akan yi amfani da shi
musamman a wani sashe na al’umma”. Misali a Hausa akwai kare-karen harsuna da
da suka ƙunshi Kananci, Gudduranci, Dauranci,
Katsinanci, Zazzaganci da sauransu.
A nan, masana ilimin harshe sun bayyana cewa, samuwar karin
harshe abu ne na ɗabi’a, domin harshe yana rayuwa ne tare da mutane. Ibrahim
(2009) aikin bincike ne da aka bayyana cewa, duk inda al’umma suka rabu ta
fuskar muhalli ko suka fuskanci canje-canje na zamantakewa, to harshe zai nuna
wannan bambanci. Karin harshe yana taimakawa wajen gano asalin mutum, inda yake
zaune, ko irin al’ummar da ya fito daga cikinta. A wasu lokuta, karin harshe yakan
zama wata alama ta alfahari da asalin al’umma, domin yana ɗauke da tarihin yankin da al’adunsa. Duk da cewa, masana
irin su Crystal (2008 sh. 113) da Finnegan (2008) sun nuna yadda harsuna suke
haɗuwa (Language Convergence) musamman ta fuskar ma’ana
a lokacin isar da saƙo a tsakanin
al’umma.
Kare-karen harshen Hausa sun rabu gida goma sha huɗu (14). Guda bakwai (7) a Nijeriya, sannan kuma guda bakwai
(7) a Jamhuriyar Nijar kamar yadda Sani & Umar (2018 sh. 23) suka bayyana. Ga
su kamar haka:
a. Kananci
b. Katsinanci
c. Sakkwatanci
d. Zazzaganci
e. Dauranci
f.
Bausanci
g. Zamfarci
Sai kuma kare-karen harsuna na Hausa waɗanda suke cikin Jamhuriyar Nijar akwai:
a. Damagaranci
b. Gobiranci
c. Adaranci
d. Arewanci
e. Kurfayanci
f.
Canganci
g. Agadasanci
A wannan bincike na karin harshe yana nufin
bambance-bambancen lafazi, kalmomi da salo na magana da ’yan gudun hijira suka
shigo da su zuwa cikin garin Kauran Namoda, wanda ya bambanta da Hausar mazauna
garin ta asali. Wannan bambanci yana bayyana ne a furuci, zaɓin kalmomi, da kuma tsarin jumla a mu’amalar yau da kullum
ta al’umma.
1.2 Gudun Hijira
Gudun hijira abu ne da yake da daɗaɗɗen tarihi da ya samo asali daga fiyayyan halitta Manzon
Allah (SAW) lokacin da aka addabe shi a mahaifarsa wato Makka, Allah (SWA) Ya
umurce shi da ya bar Makka zuwa birnin Madina. Tun wannan lokacin abin ya samo
asali har zuwa yanzu. Duk lokacin da aka tsangwami mutum a garin, ya samu ya yi
hijira daga wannan gari zuwa wani domin samun aminci da natsuwa.
Gudun hijira yana nufin yanayin da mutum ko al’umma suke
shiga na barin muhallinsu na asali domin tsira daga wata barazana kamar rikici,
tashin hankali, rashin tsaro, bala’o’i ko matsanancin talauci. A cewar
Majalisar Ɗinkin Duniya (U.N,
2018), ’yan
gudun hijira su ne mutanen da aka tilasta wa barin gidajensu amma suke ci gaba
da zama a cikin ƙasarsu. Wannan
hijira ba zaɓi ba ce, illa tilas domin kare rayuka da martaba.
Akwai ƙauyuka da garuruwa
da dama da matsalar tsaro ta addaba har wasu daga cikin al’ummun garuruwan suka yo hijira zuwa
cikin garin Kaura. Wadannan garuruwa sun haɗa da:
a. Magamin Ɗantoro
b. Gabake
c. Moriki
d. Modomawa
e. Dauran
f.
‘Yan
kaba
g. Kungurki
h. Kuromoni
i.
Dogon
kaɗe
j.
Kasuwar
daji
A wannan bincike, gudun hijira na nufin shigowar mutanen da
suka bar ƙauyuka da
garuruwansu sakamakon matsalolin tsaro suka shigo garin Kauran Namoda. Waɗannan mutane sun shigo da karin harshensu da salo na magana,
wanda hakan ya haifar da tasiri kai tsaye ga harshen da ake amfani da shi a
cikin gari.
1.3 Garin Kauran
Namoda
Garin Kauran Namoda ya samo sunansa ne daga Muhammadu Namoda
(Malam Namoda), shahararren Jarumin Yaƙi kuma malamin addinin Musulunci. Garin Kauran Namoda yana
daga cikin manyan garuruwa a Jihar Zamfara, kuma gari ne wanda ya haɗa al’ummomi da dama. Garin ya zama cibiyar noma da
kasuwanci. Hausar da ake amfani da ita a Kauran Namoda tana da tata sigar karin
harshen wadda ta bambanta da ta wasu garuruwan.
A ’yan shekarun nan, sakamakon matsalolin tsaro a wasu
sassan Zamfara da makwabtan jahohi, Kauran Namoda ta zama mafaka ga ’yan gudun
hijira. Wannan ya janyo ƙaruwa a yawan jama’a, tare da shigowar mutane mabambanta
wadanda suke da bambancin asali, al’adu da karin harshe. Yawaitar ‘yan gudun hijirar ta shafi harshen da ake amfani da shi a
Kauran Namoda. Hausar al’umma
daga wurare mabambanta ta yi naso cikin Hausar garin, musamman a kasuwanni,
makarantu, asibitoci da wuraren ba da tallafi da sauransu.
Garin Kauran Namoda gari ne babba wanda yake da gundumomi
(ward) masu yawa wanda jama’a da dama suke rayuwa a cikinsu. Wasu daga cikin
gundumomin sun haɗa da:
- Gabake
- ‘Yankaba
- Saka-jiki
- Kyambarawa
- Banga
- Dogon kaɗe
- Kagara
- Dan-isa
- Kungurki
- Kurya
2.0 Dabarun
Gudanar Da Bincike
Wannan bincike ya yi amfani da hanyoyi mabambanta domin
tattara bayanai masu inganci da za su bayyana ainihin tasirin karin harshen
‘yan gudun hijira a garin Kauran Namoda. Hanyoyin sun haɗa da majiyar farko da ta biyu domin a samu cikakken haske.
An yi amfani da gani da ido a majiyar farko, kamar yadda
Hausawa suka ce gani ya kori ji. Mun ziyarci wuraren da jama’a suke taruwa
akai-akai, irin su kasuwanni, unguwanni, makarantu, da wuraren zama na yau da
kullum. Wannan hanyar ta bamu damar ganin yadda karin harshen ‘yan gudun hijira
ke tasiri a rayuwar yau da kullum ta mazauna garin Ƙauran Namoda. An yi nazari sosai kan yadda ake amfani da
lafuzza mabambanta, kalmomi masu ma’ana biyu ko fiye da biyu (kalmomi masu harshen damo), da
kuma yadda ake magana dasu cikin zantuka na yau da kullum. Har ila yau, an
tattauna da dattawa, matasa, ’yan kasuwa, malamai da ’yan gudun hijira, domin jin yadda Hausar ‘yan gudun hijira
ta yi tasirin a kan Hausar garin. Wannan tattaunawar ta bada damar fahimtar
yadda karin harshe ke canza ko inganta sadarwa a tsakanin al’umma.
Domin tabbatar da sahihancin bayanai da kuma gina binciken
bisa tushen ilimin kimiyya, an yi amfani da majiya ta biyu ta hanyar nazarin
littattafai, da mujallu, da maƙalu,
da kundayen digiri da suka yi nazari kan karin harshe. Wannan ya taimaka wajen
gano abubuwan da masana suka riga suka gano a fannin karin harshe, musamman
yadda yake shafar al’adun
al’umma,
harshe, da zamantakewa. Ta hanyar haɗa
bayanan da aka samo daga majiyar farko da kuma hujjojin da aka samo daga majiya
ta biyu, an samu cikakken haske kan yadda karin harshen ‘yan gudun hijira yake
taka muhimmiyar rawa a garin Kauran Namoda.
3.0 Bitar Ra’i
Bitar ra’i a wannan binciken ta dogara ne a kan Nahawun
Zamantakewa (Sociolinguistics), wato wani fanni na ilimin harshe da ke nazarin
alaƙar da ke tsakanin harshe da al’umma. Wannan fanni yana kallon harshe a
matsayin wani abu mai rai da ke canzawa gwargwadon yanayin zamantakewar al’umma. Sauye-sauye kamar hijira, aure,
kasuwanci, ilimi da hulɗar jama’a kan taka muhimmiyar rawa wajen sauya lafazi,
kalmomi da tsarin magana na harshe.
Fishman (1972) ya bayyana cewa idan al’umma daga yankuna
mabambanta suka haɗu, hulɗar da ke tsakaninsu kan haifar da cakuduwar harshe, inda
kalmomi, lafuzza da salo na magana ke shiga juna. Wannan ra’ayi ya dace ƙwarai da yanayin garin Kauran Namoda, inda ’yan gudun hijira daga sassa mabambanta
suke mu’amala
da mazauna garin a kasuwanni, unguwanni da makarantu. Wannan hulɗa ta yau da kullum tana ba wa harshe damar karɓar sababbin siffofi.
Bugu da ƙari,
Trudgill (2000) ya nuna cewa karin harshe yana sauyawa ne bisa yawan hulɗa da kuma irin karɓuwar
da al’umma ke ba shi. Idan wani salo ko lafazi ya samu karɓuwa daga mutane da dama, to yana da damar ya wanzu na dogon
lokaci. Wannan ra’ayi ya taimaka wajen fahimtar dalilin da ya sa wasu siffofin
karin harshen ’yan gudun hijira ke karɓuwa
cikin sauri a Kauran Namoda, musamman a tsakanin matasa.
4.0 Tasirin Karin
Harshen ’Yan Gudun Hijira a Garin Kauran Namoda
Ɗaya daga cikin manyan tasirin da karin harshen ’yan gudun
hijira ya yi shi ne shigowar sababbin lafuzza da kalmomi cikin Hausar da ake
magana amfani da ita a Kauran Namoda. Wasu kalmomi da lafuzza daga yankunan da
’yan gudun hijira suka fito sun fara zama ruwan dare, musamman a wuraren
taruwar jama’a kamar kasuwa da unguwanni. Wannan sauyi ya fi bayyana a tsakanin
yara da matasa, domin su ne suka fi saurin kwaikwayon bakin abubuwa.
Haka kuma, wannan hulɗa ta
harshe ta taimaka wajen faɗaɗa fahimtar juna tsakanin al’umma. Mazauna gari sun fara
fahimtar karin harsunan baƙi,
haka nan ’yan
gudun hijira ma suna koyon Hausar gargajiyar Kauran Namoda. Wannan yanayi yana ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai
da jituwa tsakanin al’umma, wanda hakan ana iya kallonsa a matsayin tasiri mai
kyau ga zamantakewar garin.
Sai dai duk da waɗannan
fa’idoji, akwai ƙalubale da ke
tattare da wannan sauyi. Wasu siffofi na asalin karin harshen Kauran Namoda ya
fara raguwa, musamman a bakin matasa da yara. Idan aka yi watsi da wannan
matsala, akwai yiwuwar a nan gaba karin harshen asali ya lalace ko ya dusashe,
lamarin da ke nuna buƙatar ɗaukar mataki.
4.1 Misalan Karin
Harshen ‘Yan Gudun Hijira a Garin Kauran Namoda:
|
Lamba |
Kalma/KHGH |
Ma’ana
ta Sarari/ DDH |
Ma’ana ta Ɓoye |
Ajin
Kalma |
Rukuni |
Wuri |
Dalili |
|
1. |
Kansila |
Zaɓaɓɓen ɗan
majalisar ƙaramar hukuma |
Hoce |
Suna |
Maza/Mata |
Taro |
Siyasa |
|
2. |
Kin fi nama |
Nau’in
abinci |
Gala/Awara |
Suna |
Maza/Mata |
Gida |
Yunwa |
|
3. |
Banƙare ciki |
Abinci |
Rogo |
Suna |
Maza/Mata |
Gida |
Yunwa |
|
4. |
Bugun zuciya |
Damuwa |
Tafasa |
Suna |
Maza/Mata |
Gida |
Yunwa |
|
5. |
Kwanan amarci |
Biki |
Wanda ya kwana daji |
Suna |
Maza |
Gida |
Wahala |
|
6. |
Na banza |
Maras amfani |
Tallafin gwamnati |
Suna |
Maza/Mata |
Taro |
Wahala |
|
7. |
Akwai samata |
Zaurance |
Akwai Magana |
Yankin
Jumla |
Maza/Mata |
Gida/waje |
Hira |
|
8. |
Sun taka kwata |
Ƙazanta |
Ɓarayi sun zo ba su yi nasara ba |
Yankin
Jumla |
Maza/Mata |
Gida/waje |
Hira |
|
9. |
Ɗaukar dole |
Tursasawa |
Garkuwa da mutane |
Suna-Aikatau |
Maza/Mata |
Gida/waje |
Hira |
|
10. |
Malam Shehu |
Mutum |
Talaka |
Suna |
Maza/Mata |
Gida/waje |
Wahala |
|
11. |
Tsananna |
Abinci |
Shinkafa |
Suna |
Maza/Mata |
Gida/waje |
Yunwa |
|
12. |
Baƙi da kwat |
Abinci |
Tuwon dawa |
Suna |
Iyaye |
Gida |
Yunwa |
|
13. |
Motar Sayyadi |
Abin hawa |
Mai tafiyar
ƙasa |
Sifa |
Manya/Yara |
Gida/Waje |
Sufuri |
|
14. |
Dongon
baro |
Abin hawa |
Mashin Honda
na ɓarayi |
Suna |
Manya |
Gida/Waje |
Sufuri |
|
15. |
Alaji |
Abinci |
Kunu/koko |
Suna |
Manya/Yara |
Gida |
Yunwa |
|
16. |
Hajiya |
Abinci |
Fura |
Suna |
Manya/Yara |
Gida |
Yunwa |
|
17. |
Gimbiya |
Abinci |
ɓula/tuwon ruwa |
Suna |
Manya/Yara |
Gida |
Yunwa |
|
18. |
Danka |
Abinci |
Dankali |
Suna |
Manya/Yara |
Gida |
Yunwa |
|
19. |
Manka |
Abinci |
Mankani |
Suna |
Manya/Yara |
Gida |
Yunwa |
|
20. |
Ƙanƙamo |
Abin sha |
Ƙanƙara |
Suna |
Manya/Yara |
Gida/Waje |
Ƙishin-ruwa |
|
21. |
Carki |
Tsuntsu |
Mai son banza |
Sifa |
Manya |
Gida/Waje |
Damuwa |
|
22. |
Aku |
Tsuntsu |
Mai sambatu |
Sifa |
Manya |
Gida/Waje |
Damuwa |
5.0 Sakamakon
Bincike
Sakamakon binciken ya nuna cewa karin harshe na ’yan gudun
hijira ya yi tasiri ta fuskoki guda biyu a garin Kauran Namoda. A ɓangare guda, yana ƙara wadata da bunƙasar harshe ta hanyar shigowar sababbin kalmomi da lafuzza,
wanda yake ƙara bunƙasa hanyoyin mu’amalar jama’a. Wannan yana nuna cewa, harshe
abu ne mai rai da yake karɓar canji
gwargwadon zamani da kuma yanayin al’umma, musamman ta fuskar zamantakewa.
A ɓangare guda kuma, binciken ya nuna cewa, wannan sauyi yana
iya rage ƙarfin asalin karin
harshen gari, musamman idan ba a ɗauki
mataki ba. Matasa da yara sun fi karɓar
sabon abu fiye da manya, domin kuwa su manya sun fi yin riƙo da tsohon salo ko tsari na furuci ko magana da suka gada
tun da fari a wurin iyaye da kakanni.
Bugu da ƙari,
an gano cewa, wuraren taruwar jama’a kamar kasuwanni, makarantu da unguwanni su
ne cibiyoyin da aka fi gudanar da mu’amula da baƙin al’ummomi. Wannan ya nuna cewa, mu’amular da akan yi ta yau
da kullum a tsakanin al’umma tana taka muhimmiyar rawa wajen sauya harshe. Har
ila yau, binciken ya yi ƙoƙarin gano ma’anonin wasu kalmomi da jumloli na karin harshen ‘yan gudun
hijira a garin ƙauran Namoda, inda
aka duba ma’anoni na sarari da na ɓoye da
kuma ajin kalma a nahawu, sai muhallin da ake furta irin waɗannan kalmomi da dalilan furta su ta hanyar kallon rukunin
al’umma dangane da su waɗannan ‘yan gudun hijira na garin ƙauran Namoda da ke jihar Zamfara.
Haka kuma a cikin wannan bayani, an yi amfani da Alamar KHGH
a matsayin Karin harshen ‘yan gudun hijira, a yayin da aka saka alamar DDH a
matsayin Daidaitacciyar Hausa. An nuna yadda ake samun canjin ma’ana ta fuskar
kalmomi da kuma yankin jumloli a tsakanin Karin harshen rukuni da kuma na nahiya
duk a cikin harshen Hausa.
Bayani A Kan Wasu Kalmomin Karin Harshen ‘Yan Gudun Hijira a
Garin Ƙauran
Namoda
1. Kansila:
Wannan kalma
tana nufin zaɓaɓɓen ɗan majalisar dokoki ta ƙaramar hukuma. Sai dai a karin harshen
‘yan gudun hijira, kalmar tana ɗaukar ma’anar ‘Hoce’ watau abincin
da ake yi da kwaɓaɓɓen garin masara ko dawa a jihar Zamfara, ta hanyar gasa shi a saman kasako
ko a bayansa.
2. Kin
fi nama: Wannan na nufin Gala (Awara) wadda ake yi da waken suya a
matsayin abinci, ta hanyar dafawa ko soyawa.
3. Banƙare-ciki: Kalmar tana nufin Rogo dafaffe ko
ɗanye a Hausar ‘yan gudun hijira na cikin garin Ƙaura- Namoda.
4. Bugun zuciya: A nan ana nufin Tafasa, watau ganyen da ake zagowa a daji
daga tushensa, inda akan dafa shi domin a ci, ya kasance a matsayin abinci mafi
ƙasƙanci ga marasa galihu ko don yin magani a ƙasar Hausa.
5. Kwanan amarci: ‘Yan gudun hijirar sukan danganta wannan ne ga mutumin da ya
kwana a hannun ɓarayin daji, watau mace ko namiji ta fuskar sauya batun zuwa
baibai.
6. Na banza: A Karin harshen ‘yan gudun hijira, wannan yana nufin kayan
tallafin da gwamnati take bayarwa ga ‘yan gudun hijira, waɗanda suka rabu da muhallansu.
7. Malam Shehu: A nan, ana nufin talaka talak, watau wanda bai da cin yau
balle na gobe.
8. Tsananna: Shinkafa ce da aka dafa kuma ake jira a rarraba ta ga mabuƙata masu jin yunwa.
9. Baƙi da kwat: Tuwon
dawa ke nan, wanda ake raba wa ‘yan gudun hijira matsayin sadaka
10. Motar sayyadi: Watau ƙafa,
ko ktafiyar ƙasa da mutum ya yi
main isa don gudun tsira.
11. Dogon baro: Wani dogon mashin ne (Honda) na ɓarayin daji mai ɗaukar
aƙalla mutum biyar, shi ne suke goya
muatane idan sun ɗauko su domin yin garkuwa da su a daji.
12. Alaji: Wannan yana nufin koko ko kunu, wanda ake rabawa a sansanin
‘yan gudun hijira na garin Ƙaura-Namoda
ta jihar Zamfara.
13. Hajiya: Fura ke nan, wadda ake girkewa domin rabawa ‘yan gudun
hijira a Ƙaura Namoda.
14. Gimbiya: Tuwon-ruwa (ɓula) wanda ake yi
da markaɗaɗɗen gero ko dawa, ta hanyar cura daskararren ƙullu da kuma dafa shi a matsayi abinci a yankin Zamfara da Katsina.
15. Ƙanƙamo: Ƙanƙara ke nan daskararra mai sanyi wadda take da wuyar riƙewa a hannu.
16. Danka: Wannann a nufin Dankali, abinci ne da ake dafawa a ci da ƙuli ko da miya ko gaya.
17. Manka: Ana nufin Mankani, abinci ne da ake dafawa a ci da ƙuli ko da miya ko gaya.
18. Carki: Mai wayau ke nan tare da nuna son abin hannunsa da kuma
nuna halin son banza.
Shawarwari Bincike
Dangane da sakamakon binciken, ana ba da shawarar malamai da
makarantu su ƙara ƙarfafa koyar da harshen Hausa, musamman ta gargajiya a
matakin firamare da sakandare. Wannan zai taimaka wajen gina tubalin harshen
yara tun daga tushe, tare da kare asalin karin harshen garin da suke.
Haka kuma, ya dace a ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin ’yan gudun
hijira da mazauna garin da suka yi sansani don neman mafaka. Domin kuwa, idan
al’umma suna zaune cikin jituwa, harshe zai bunƙasa ba tare da janyo rikici ko rashin fahimta ba.
Masana harshe da ɗalibai
su ƙara gudanar da bincike kan tasirin
karin harshen ‘yan
gudun hijira a harsunan gida, domin samar da hanyoyin kula da sauyin harshe ta
yadda zai ci gaba da bunƙasa ba tare da tauye
asalinsa ba.
6.0 Kammalawa
Wannan bincike ya tabbatar da cewa gudun hijira yana da
tasiri kai tsaye ga harshe, musamman ta fuskar karin harshe. Shigowar ’yan gudun hijira ya sauya yanayin
Hausar Kauran Namoda ta hanyoyi daban-daban, kama daga lafuzza zuwa kalmomi da
salo na magana. Wannan sauyi ba dukkansa ne mummuna ba, domin yana nuna rayuwar
harshe da ci gabansa. Sai dai, idan ba a kula da shi ba, yana iya janyo
gushewar wasu siffofi na asalin karin harshen garin. Saboda haka, wannan
seminar ta zama gudummawa mai muhimmanci wajen fahimtar alaƙar da ke tsakanin gudun hijira da sauyin harshe a al’ummar Hausa, tare da buɗe ƙofa ga ƙarin bincike a nan gaba.
Manazarta
Bello, A. (2020). Daidaitacciyar
Hausa da Kare-Karen Harshen Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Crystal, D. (2008). A Dictionary of Linguistics and Phonetics.
Malden: Blackwell Publishing.
Finnegan, E. (2008). Language: Its Structure and Use. Boston:
Thomson Higher Education.
Fishman, J. A. (1972). The Sociology
of Language. Rowley, MA: Newbury House Publishers.
Galadanci, M. K.
M. da Wasu (1990). Hausa Don Ƙananan Makarantun Sakandare 1. Ikeja, Lagos: Longman Nigeria Plc.
Ibrahim, M. S. (2009). Harshe da
Al’umma: Nazarin Zamantakewar Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Sani, A.-U., & Umar, M. M. (2018).
Global growing impact of Hausa and the need for its documentation. Contemporary
Journal of Language and Literature, 1(1), 16–34.
Sani, M.AZ. (2009). Siffofin
Daidaitacciyar Hausa, Kano: Benchmark Publishers Limited.
Trudgill, P. (2000).
Sociolinguistics: An Introduction to Language and Society. London: Penguin
Books.
United Nations High Commissioner for
Refugees (UNHCR). (2018). Guiding Principles on Internal Displacement. Geneva:
United Nations Publications.
Yakasai, S. A. (2014). Harshe,
Al’adu da Zamantakewa. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Zaria, A. U. (2011). Gudun Hijira da
Tasirinsa ga Al’umma. Kundin Digiri na Biyu, Sashen Ilimin Zamantakewa, Jami’ar
Ahmadu Bello, Zaria.
Zarruk da Wasu (1990). Sabuwar Hanyar
Nazarin Hausa. Ibadan: University Press.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.