Citation: Sulaiman, A. (2026). Gurbin Waƙoƙin Yara Mata da ‘Yammata a Rayuwar Hausawa. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, 5(1), 57-66. www.doi.org/10.36349/tjllc.2026.v05i01.006.
GURBIN
WAƘOƘIN YARA MATA DA ‘YAMMATA
A RAYUWAR HAUSAWA
Na
Asma’u
Suleiman
Department of General Studies
College of Liberal Studies
Hassan Usman Katsina Polytechnic, Katsina
Phone:
07038186310
Email:
asmausuleiman2018@gmail.
com
Tsakure
Waƙoƙin yara mata da ‘yammata wani babban rukuni ne a al’adar Hausawa. Waƙoƙi ne da ake yi
domin samun nishaɗi da tarbiyya da ilmantarwa da kuma gargaɗi ga ‘yammata tun suna ƙanana. Waƙoƙin suna ƙunshe da darussa
masu muhimmanci da suka shafi rayuwa da ladabi da tsaftace hulɗa da sauran mutane, ko dogaro da kai ta hanyar sana’o’i. An
ƙudiri aniyar yin wannan bincike ne ganin yadda a yanzu ire-iren waɗannan waƙoƙi masu ƙima suka tafi hanyar ɓacewa kuma waƙoƙin fiyano na ƙoƙarin maye
gurbinsu. Daga cikin manufofin waɗannan waƙoƙi na yara mata akwai koyar da tarbiyya da waɗanda ke ilimantarwa, ga waɗanda ake yi domin tallata sana’o’i, akwai waɗanda ake shiryarwa ga rayuwar aure da kuma waɗanda ake yi domin nishaɗantarwa. Na ɗora wannan bincike a kan ra’in Adabin Gargajiya (Folklore Theory) wanda
William John Thoms ya ƙirƙira a shekarar 1846 daga baya kuma Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo ya kafa ƙa’idojin nazarin
waƙoƙin gargajiya daga 1970 har zuwa lokacin da muke yanzu. Ra’in Adabin
Gargajiya yana nazari a kan abubuwan da al’umma ke gadonsu ta baka. Don haka, waƙoƙin yara mata tubala ne da suka fito daga al’ada waɗanda ake gado daga iyaye zuwa yara cikin sauƙi da nishaɗi, kuma waƙoƙin ba don wasa kawai ake yi ba, al’adu ne waɗanda ke shiryar da ‘yammata a kan yadda za su taso cikin
ladabi da tarbiyya. Hanyoyin da aka bi domin samun sahihan bayanai na wannan
bincike sun haɗa da nazartar littatafai da suka zo hannu masu alaƙa da aikin da
sauraro da naɗar wasu waƙoƙi daga waɗanda abin ya shafa, an yi amfani da wayar hannu domin naɗar waƙoƙin. Haka kuma an samu misalan wasu waƙoƙin daga
marubuciyar. Sakamakon da aka samu bayan gudanar da wannan bincike sun haɗa da duk da sauye-sauyen da aka samu na zamani waƙoƙin yara da ‘yammata
sun ci gaba da zama wata hanya mai tasiri wadda al’umma ke amfani da ita wajen
gina tunanin yara da shirya su domin rayuwar gaba. Wannan ya nuna cewa waƙoƙin ba wai ana yin
su ne kawai don nishaɗi ba, suna taka muhimmiyar rawa wajen tsare al’ada da haɓaka ilimi.
Fitilun Kalmomi: Waƙa, Yara Mata, Waƙoƙin Dandali, Waƙoƙin Gargajiya
1.0.Gabatarwa
Adabin gargajiya wani
muhimmin ɓangare ne na rayuwar Hausawa.
A
cikinsa ne ake tara da adana al’adu. Daga cikin muhimman
rukunan wannan nau’in adabi akwai waƙoƙin yara, musamman waƙoƙin ‘yanmata waɗanda ke taka rawa wajen ilmantarwa da gina halayen yara tun suna ƙanana. Kiɗa da waƙa a ƙasar Hausa wani ginshiƙin abu ne da ake aiwatarwa don
ilimantarwa ko sadarwa ko nishaɗantarwa ko bayar da wata gudummuwa ta musamman, kusan kiɗa da rawa ya yi tsaki ya dulmiya sosai a cikin rayuwar
Bahaushe, musamman rayuwar da ta danganci zamantakewa (Gusau 1987 sh. viii).
Sanin asalin yadda
aka fara waƙar baka abu ne mai wuya. Yawanci akan yi shaci-faɗi a bayyana abin da ya
sauƙaƙa. Masana da
manazarta kuwa kuwa sukan yi ƙoƙarin yin la’akari
da abubuwa daban-daban domin hasashen samuwar waƙar baka. Akwai ra’ayoyin
masana guda huɗu da suka yi bayani a
kan haka. Ra’ayi na farko wanda ake ganin duk ya fi sauran inganci shi ne wanda
ake jin cewa ɗan’adam ya fara yin
waƙa
ne tun lokacin da ya fara samun abinci ta hanyar farauta. Wani ƙaulin kuma shi ne
wanda wasu ke cewa waƙa ta samu ne sakamakon ƙangin bauta na gargajiya
(Gobir da Sani, 2021 sh. 3-6). Mashahuri daga cikin ra’ayoyi dangane da asalin waƙar baka a ƙasar Hausa shi ne
wanda aka danganta faruwarta da Bani Sasana. Ra’ayi na ƙarshe shi ne wanda ake
ganin waƙa ta faro ne daga tsofaffin daulolin Afirka ta Yamma,
Ghana da Mali da Songhay (Yahaya da wasu, 2007 sh. 22).
Wannan bincike ya ƙunshi bayani ne kan waƙoƙi na yara mata musamman waɗanda ke azuzuwan farko na makarantar gaba da firamare. Duk da haka, amfana
da binciken bai taƙaita ga yara kaɗai ba domin kuwa daga yara har manya da masu bincike za su amfana daga abin
da aka samar. Manufar yin binciken shi ne bunƙasa al’adun Hausawa da kuma inganta
burin da ke akwai na ganin yaran Hausawa sun tashi cikin kyakkyawar tarbiyya da
sanin al’adu kyawawa da kuma sauran al’amuran da ke kewaye da mu. Wannan dalili
ne ma ya sa aka yi taka-tsantsan wajen zaɓen kalmomi da gina jumlolin da ke cikin waƙoƙin domin dacewa da tarbiyyar yaran. Aikin ya tattaro wasu
waƙoƙi na yara mata waɗanda suke yi a lokuta
daban-daban.
Akasari yaran suna yin waƙoƙin ne wajen wasanni a dandali ko cikin watannin azumi ko
a makarantu, ko lokacin bukukuwan maulidi, da kuma waɗanda yaran ke yi a
wajen bara da sauransu.
1.2 Ma’anar Waƙa
Da zarar an tambayi mutum
ma’anar waƙa, yawanci al’amuran da suka dangance ta ke fara zo masa
a rai. Ta amfani da waɗannan abubuwan da
suka dangance ta ne waɗanda suka gina ta ake
haɗawa a fito da ma’anar.
Muhimmin abin da kowa ya sani game da waƙa shi ne ana bayyana
ta a rere, ta hanyar amfani da daidaitattun kalmomi da bin sauran ƙa’idoji waɗanda suka haɗa da ɗiya da sautin murya mai
zaƙi,
kuma ana haɗawa da tafi don a
jawo hankalin mai sauraro (Gusau, 1993 sh. 2).
Umar (1988) yana ganin
waƙa
maganganun hikima ne da fasaha da ake rerawa ba faɗa kurum ba cikin zaɓaɓɓun
kalmomi da suka dace da saƙonni waɗanda ke bin ƙayyadajjen
tsari dangane da sautin murya. Ya ƙara da cewa waƙa tana zuwa ne a
sigar gunduwoyin zantuka waɗanda ake kira baitoci ko ɗiyoyi da ake rerawa da wani irin sautin
murya na musamman.
A wurin Yahaya (1984)
kuwa waƙa wata maganar hikima ce da ake rerawa ba faɗa kurum ba wadda ke da
wani saƙo da ke ƙunshe cikin wasu kalmomi zaɓaɓɓu, tsararru kuma zaunannu.
Muhammad (2001) ya bayyana cewa ma’anar da za a iya ba waƙar baka kai-tsaye
ba tare da an haɗa ta da rubutacciya ba
ita ce “waƙa wani zance ne shiryayye cikin hikima da azanci da ke zuwa
gaɓa-gaɓa, bisa ƙa’idojin tsari da
daidaitawa a rere cikin sautin murya da amsa-amon kari da kiɗa da amshi”. Bakura
da Sani (2024 sh. 38) sun tafi kan cewa "waƙa na nufin
tsararriyar magana da ke ƙunshe da fasaha da hikimar sarrafa harshe da ake rerawa
gunduwa-gunduwa, cikin wani amo na musamman."
Ta la’akari da waɗannan bayanai da suka
gabata za a iya cewa waƙar baka wani zance ne da ake bayyanawa a rere wanda ke ƙunshe da wasu muhimman
saƙonni
ba wai don nishaɗantarwa kawai ba, ta
hanyar bin wasu ƙa’idoji ko siffofi irin su rerawa da
manufa da amshi
da sauransu.
1.3
Rabe-Raben
Waƙoƙin Yara
Za a iya raba waƙoƙin yara zuwa gida biyar.
1. Waƙoƙin Tashe: Suna ɗaya daga cikin rabe-raben
waƙoƙin yara mata na gargajiya,
ana gudanar da su sau ɗaya a shekara wato a watan
azumi. Da zarar watan azumi ya kai kwana goma sha ɗaya, ‘yanmata da
samari suke fara wasannin tashe, misalan waƙoƙin tashe sun haɗa da ‘Waƙar Mai Ciki’ da ‘Waƙar Mai Idon Sakaina’
da ‘Waƙar Kura-kura’ da sauransu.
2. Waƙoƙin Bikin Aure: Waƙoƙi ne da ake gabatarwa
a lokacin da ake yin bukukuwan aure, saboda da wuya a yi hidimar biki ba tare
da an rera waƙa ba, wannan ko ya samo asali ne tun kaka da kakanni kuma
har yanzu ana yi. ‘Yammata da ƙawayen amarya ne suke rera waƙoƙin, kuma akan rera su
ne a lokacin gudanar da gudun amarya da wajen kamu da wajen wankan amarya da
kuma wajen buɗar kai.
3. Waƙoƙin Talla: Ana gudanar da waɗannan waƙoƙi lokacin da ake tallar
wani abin sayarwa
a cikin kasuwa ko wuraren da mutane ke taruwa. Kusan kowane abu da ake sayarwa akwai
waƙar
da ake yi don a zuga sana’a ta fito da kwarjininta
ga idon jama’a da kuma yin tuni ga wanda ke da buƙata. Misalan abubuwan
talla da ake rera wa waƙa sun haɗa da ‘Waƙar Tallar Goro’ da ‘Waƙar Tallar
Ɗanwake’ da
‘Waƙar Tallar
tTliya’ da
sauransu.
4. Waƙoƙin Dandali: Waɗannan su ne waƙoƙin da ake gudanarwa a
dandali da daddare bayan an ƙare cin abincin dare, inda yara maza
da mata ke taruwa su yi wasanni. Misalan irin waɗannan waƙoƙi sun haɗa da ‘Waƙar Shalle
Mage’ da
‘Waƙar Doya-
gari- doya- gari’
da sauransu.
5. Waƙoƙin Bara: Waɗannan waƙoƙi ne da yara ke yi da
nufin neman abinci ko wani abin masarufi. A lokacin yin waɗannan waƙoƙi akwai jagora, wato mai
ba da waƙa da ‘yan amshi waɗanda ke ƙara fito da buƙatar da yaran ke da ita
ga waɗanda suke yi wa barar.
Misalan waƙoƙin bara sun haɗa da waƙar yaron malam, da waƙar ‘yar bakara da waƙar mai bara da
sauransu.
2.0 Waƙoƙin Yara Mata
1. Waƙar Sabara
Wannan waƙa ce wadda ‘yammata
ke rerawa a dandali, tana da jagora da ‘yan amshi. Wajen gudanar da ita yaran suna
yin da’ira.
Ga yadda waƙar take:
Badawa: Sabara
Amshi: Sabara
Badawa: Ta yi liya-liya
Amshi: Sabara
Badawa: ‘Yar bakin gulbi
Amshi: Sabara
Badawa: Ku watsa mata ruwa
Amshi: Sabara
Badawa: Shar na ƙoshi
Amshi: Sabara
Sabara wani shahararren
tsiro ne mai muhimmanci a wurin Hausawa wanda ake amfani da shi a ɓangarori da dama na rayuwa.
Ana samun tsiron sabara a yankunan Arewacin Nijeriya, a jeji ko kusa da gidaje musamman
a wuraren da ƙasa ke da ɗan danshi. Ana amfani da ganyen sabara ko
tushenta wajen magance cututtuka da tsarkake jiki da samun kariya daga cututtukan
aljannu. A wannan waƙar ‘yammatan sun bayyana wurin
da sabara ke fitowa
da yadda take yin kyau idan an watsa mata ruwa ta sha ta ƙoshi. A taƙaice amfani da sabara
a cikin waƙa yana nuna zurfin tunani da hikimar adabin baka na Hausawa,
sabara ba tsiro kaɗai ba ce,
ita alama ce ta rayuwa, tana da juriya kuma magani ce sannan kuma an yi amfani
da ita wajen isar da saƙo.
2. Waƙar Carman-Dudu Carman-Duduwa
‘Yammatake
yin wannan waƙa a dandali wajen yin wasanninsu, ana yin da’ira sannan kuma
akwai shugaba da ‘yan amshi. Ga yadda waƙar take:
Badawa: Carman-dudu carma -duduwa
Amshi: Carmande
Badawa: Akwai wani baƙo a gidan Maigari
Amshi: Carmande
Badawa: Ba ya sallah ba ya lazimi
Amshi: Carmande
Badawa: Ba ya neman ‘yanmatan
gari
Amshi: Carmande
Badawa: Ko ya nema ba zai ba
shi ba
Amshi: Carmande
Badawa: Yayata landiyo mana
Amshi: Carmande
Badawa: Ƙanwata landiyo mana
Amshi: Carmande
Waƙar carman- dudu waƙa ce da ke nuna yadda Bahaushe ke karrama baƙo, domin a da can idan baƙo ya je wuri, gidan maigari
za ya sauka. Haka kuma a waƙar an nuna wa yara cewa rashin yin sallah da lazimi na
nuna rashin nagartar mutum, saboda haka babu wanda zai iya ba marar nagarta
auren ɗiyarsa. A waƙar an fito da al’adu
da ɗabi’un Hausawa na karrama
baƙo
da riƙo da addini da kuma yin bincike kafin aure.
3. Waƙar Wankan Amarya
‘Yammata
ne suke yin wannan waƙa lokacin da ake wankar
amarya,
tana da jagora da ‘yan amshi.
Badawa: Ayye!
raye lemu-lemu
Amshi: Ayye
raye lemu-lemu
Badawa: Lemun
Kano, lemun Daura, lemun da ba na sha ne ba
Amshi: Ayye raye lemu-lemu
Wankan amarya na ɗaya daga al’adun da Hausawa ke yi lokacin da ake bikin aure. Wannan waƙar abokan amarya ne
ke rera ta
a lokacin da ake yin wankan. A da can lokacin da addinin musulunci bai karaɗe ko’ina
ba, ana yi wa amaryar wankan ne a fili kowa na kallo, amma a yanzu da ilimin addini
ya yawaita amaryar ce ke yin wankan da kanta.
4. Waƙar Maido Aron Amarya
‘Yammata
suke yin wannan waƙa a lokacin mai da aron (mai da amarya
gidan uban wanka kafin a ɗaura mata aure sannan
a kai ta gidan miji) amarya, ita ma wannan kamar sauran tana da jagora da ‘yan amshi.
Ga waƙar kamar haka:
Badawa: Ayye
ga aro a mai da aro
Amshi: Ayye
ga aro a mai da aro
Badawa: Ga aron da kuka ba
mu yau ga shi mun maido
Amshi: Ga aron da kuka ba
mu yau ga shi mun maido
Badawa: Ta ƙi ci, ta ƙi sha, ta ƙi markaɗen dawa sai ɗan karen kuka
Amshi: Ta ƙi ci, ta ƙi sha, ta ƙi markaɗen dawa sai ɗan karen kuka
Wannan waƙa abokan amarya ke rera ta
a lokacin da za a mayar da aro. Ana mayar da aron amarya kamar saura kwana ɗaya kafin a ɗaura mata aure, za a ɗauke ta daga gidan mahaifinta
a kai ta gidan ɗaya
daga cikin ‘yan’uwansa (wa
ko ƙanensa,
shi ake kira uban wanka), wanda daga gidansa za
a kai amarya gidan miji bayan an ɗaura aure. Haka ‘yammata
za su yi
ta rera waƙa wasu na amsawa har sai an kai ta gidan uban wanka inda daga
nan za a ɗauke ta zuwa gidan miji.
5. Waƙar Samodara
‘Yammata
biyar ko shida ke yin wannan waƙa, ɗaya daga cikinsu za ta yi shiga kamar mai ciki,
za ta sanya ƙoƙo a saman cikinta ta ɗaura zane a bisa, sai ta riƙa turo cikin gaba kamar
mai cikin gaske, ta shiga gaba saura suna biye suna yin waƙar kamar haka:
Badawa: Iya duba
duba
Amshi: Samodara
Badawa: Iya dubi cikina
Amshi: Samodara
Badawa: Baba ne ya saya man
Amshi: Samodara
Badawa: Har ya ce in yi yanga
Amshi: Samodara
Badawa: Ga yangar na yi
Amshi: Samodara
Wannan waƙar ‘yammata
na yin ta ne kawai a matsayin nishaɗi, a yayin yin ta suna misalta yadda yanayin jikin
mata ke sauyawa lokacin suna da ciki. Hakan na nusar da ‘yammatan
su gane cewa duk macen da ta samu ciki ta hanyar aure ba ta jin nauyi idan an
gani, tun da ga shi har yanga take yi, amma idan har cikin ya samu ne ta hanyar
da ba ta dace ba, to abin kunya ne da Allah wadai.
6. Mai Ciki
Wannan waƙa ‘yammata
kamar biyar ke yin ta, sai a ɗaura wa ɗaya daga cikinsu tsummokara a saman ciki ta fito kamar mai
cikin da ta kusa haihuwa, sai ta wuce gaba tana tura cikin gaba tana tafiya babbanƙare sauran suna biye da
ita suna kiran ta
kamar suna tsokanar ta
suna cewa:
‘Yammata: Mai ciki Mai ciki: Iye
ga ni
nan tafe
‘Yammata: Mai ciki Mai ciki: Iye
ga ni
nan tafe
‘Yammata: Mai ciki Mai ciki: Wallahi
ba ni son sunan nan
‘Yammata: Mai ciki
Mai ciki: Wallahi
za ni ɓata da mutum
‘Yammata: Mai ciki
Mai ciki: Wallahi
har gaban alƙali
‘Yammata: Hajiya Mai ciki: Uhm!!
Ga
ni nan ina turawa
Wannan waƙar ta ’mai
ciki'na
nuna yanayin da mata ke shiga idan suna da juna biyu da tarbiyyar da iyaye ke yi
wa ‘ya’yansu mata na kare kansu daga samun ciki ba tare da aure ba, da kuma
yadda Bahaushe
ke ƙimanta
kiran duk wadda ta je aikin hajji da sunan Hajiya.
7. Ke! Ina za ki da Kaya
Wannan waƙa ce da ake yi lokacin
tashe, ‘yammata
kamar su uku ko huɗu ne suke yin waƙar. Ɗaya daga
cikinsu za ta harhaɗa kayayyaki kamar ƙwarya da kwanoni ta ɗaure da zani ta aza bisa
kai, saura suna rera waƙa ita kuma tana rawa ga waƙar:
Badawa: Ke, ina za ki da
kaya?
Amshi: Kishiya ta koro ni har
da kashi tab ba ni,
Har
ta zub da
mani haure.
Wannan waƙa na gwada zamantakewa
irin ta aure, wato irin yanayin zama tsakanin kishiyoyi, an fito da irin tsarin
auratayya ta malam Bahaushe wanda tun kafin zuwan addinin musulunci har bayan
zuwan shi yake da damar auren mace fiye da ɗaya. An fito da yadda mata ke yin yaji daga gidan
mazajensu idan sun samu saɓani.
8. Tsakiyata ta Tsinke
‘Yan yara mata suke
yin wannan waƙa, suna tsugunnawa su yi da’ira su kama hannayen juna suna
lila su gaba da baya suna yin waƙar. Lokacin da suka
zo cewa “shinkafata shaf - shaf” sai su miƙe tsaye su yi ta
tsalle suna juyawa. Ga waƙar:
Tsakiyata
ta tsinke
A ɗakin masoyina
In durƙusa in ɗauka
Abin ne
da kunya
Allah
tsine ‘yar kunama a cikin duhun ciyawa
Shinkafata
shaf–shaf
Shinkafata shaf–shaf.
A waƙar an fito da irin
kunya da girmamawa da ke tsakanin saurayi da budurwa.
9. Waƙar Gajere–Gajere
Ana yin wannan waƙar ne kamar wasan kwaikwayo
a lokacin tashe. ‘Yanmata
kamar su huɗu ko biyar ne suke
yin ta. Yarinya ɗaya daga cikinsu za
ta sanya tufafin maza a matsayin ita ce gajere, sai ɗaya kuma ta ɗauko kayan abinci da
tabarma da matashin kai a yi wa gajeren shimfiɗa ya kwanta, sai ta
riƙa
yi masa fifita tana rera wannan waƙar.
Badawa: Gajere-gajere mai riga
da wando
Amshi: Gajere
Badawa: Amshi tuwonka ka
cinye
Amshi: Gajere ya ce ba ya
ci nai
Badawa: Amshi ruwanka ka
shanye
Amshi: Gajere ya ce ba ya shan
su
Badawa: Na rantse tsakanina
da Allah gobe gidanmu za ni
Amshi: Gajere
Da ta ce haka sai ta ruga da gudu, shi kuma gajere sai ya bi ta da gudu ya
kamo ta ya yi ta ba ta haƙuri.
Wannan waƙa na nusar da al’adar Hausawa ta ƙyamatar haɗuwar mata da maza a wuri ɗaya, (ɗaya daga cikin ‘yammatan ke shiga
irin ta maza), tana koyar da rayuwar aure da yadda aka umurci mata su yi wa
maza biyayya, yin yaji da mata ke yi daga gidan mazajensu idan an samu saɓani da kuma yadda maza ke yin bikon matansu.
10. Waƙar ‘Yar Fulanin Jeji
Wannan waƙar ta ‘yammata ce suna durƙusawa bisa guiwoyinsu su yi ta rera waƙar suna amshi, idan aka
zo ƙarshen waƙar inda ake cewa “a dungura ƙwas - ƙwas” sai dukansu su dungura goshinsu a ƙasa, amma idan aka zo
inda ake cewa“a dungura na ƙi” duk wadda ta dungura sai a bi ta da duka. Ga waƙar:
Badawa: ‘Yar Fulanin jeji
Amshi: Amariɗo
Badawa: Ta yi ɓarin nono
Amshi: Amariɗo
Badawa: Ta ce in tanɗe
Amshi: Amariɗo
Badawa: Ba na uwata ba
Amshi: Amariɗo
Badawa: Ba na ubana ba
Amshi: Amariɗo
Badawa: Da na uwata ne
Amshi: Amariɗo
Badawa: Da na tattanɗe
Amshi: Amariɗo
Badawa: Har bayan ƙwarya
Amshi: Amariɗo
Badawa: Iye ayye a dungura ƙwas – ƙwas
Amshi: Iye ayye
a dungura na ƙi.
A waƙar an fito da yadda
yaran Hausawa
ke yin biyayya da nuna soyayya ga iyayensu, komi idan dai ya danganci iyaye, to
mutum zai yi biyayya iyakar ƙarfinsa, sai inda ƙarfinsa ya ƙare. Wannan ya nuna
yadda ake koya wa yara yin biyayya da girmama iyayensu a al’adance ta amfani da
waƙoƙi. Sa’annan kuma
akwai bin biyayya ga ƙa’idojin da aka
gindaya.
11. Waƙar A-sha-Ruwa
‘Yammata
suke yin wannan waƙar a lokacin azumi bayan an sha ruwa, ‘yammata
kamar biyar zuwa bakwai za su yi shiga gida-gida suna rera waƙar sauran na amsawa. Ga
waƙa:
Badawa: A sha
ruwa malam a sha ruwa
Amshi: A sha ruwa
Badawa: Matar Malam
a sha ruwa lafiya
Amshi: A sha ruwa
Badawa: Masu gidan nan barci
kuke ko sallah
Amshi: A sha ruwa
Badawa: Idan sallah ce ku yi
ta domin Allah
Amshi: A
sha ruwa
Badawa: Idan barci ne ku tashi
domin Allah
Amshi: A sha ruwa
Badawa: Watan
azumi ne watan ibadar Allah
Amshi: A sha ruwa
Badawa: Na yi mafarki Baba
yana aljannah
Amshi: A sha ruwa
Badawa: Na yi mafarki Inna tana
aljanna
Amshi: A sha ruwa
Badawa: Duk suna aljanna a
kan kujerar ƙarfe, ga kuma gadon zinare.
Wannan waƙa ce wadda kalaman da
ke cikinta suka nuna irin hidimomi da ayyuka da ake gudanarwa a cikin watan azumi,
an nuna yadda duk wanda ke son tsira ranar gobe ƙiyama zai
tsayu wurin
yin ibada. Da zarar watan azumi ya tsaya, musulmi suna dakatar da aikata alfasha
da ayyuka marasa kyau, a waƙar ‘yammatan
suna jawo hankalin jama’a ga yin ibada ga Allah kuma domin Allah. Wannan waƙar tana koyar da yara
lallai lokacin watan azumi lokaci ne na yin ibada domin samun tsira a ranar lahira
wanda yin haka zai kai
su ga shiga aljanna.
12. Waƙar Ina Jan–je, Ina
Jan-je
Wannan waƙar yara mata ne suke
yin ta, suna zaunawa a ƙasa cikin layi su mimmiƙe ƙafafunsu, sai ɗaya daga cikinsu ta rinƙa daddafa guiwoyinsu
tana rera wannan waƙar
Ina
jan-je ina jan-je,
Na
jan-je ni gidan gwauro,
Gwauro
ya ba ni tuwon dusa,
Ban
karɓa ba ina tsoro,
Tsoron
me?
Tsoron
wani abu jan baki,
Jan
baki sari ƙoto,
Ƙoton gidan baraje,
Barajen
da wa yake,
Miƙo hannu mu je mu,
Mu
je mu wace rana,
Ranar
yaƙin
busasshe,
Busasshen
karin shanshaye,
Ƙwaryar tasa ta fashe
a bayan ɗaki tangaram.
Waƙar ina jan-je na nuni ga al’adar Bahaushe ta nuna ƙyama ga namiji wanda ke zama ba tare
da aure ba (gwauro), bisa wannan dalilin ne a cikin watan azumi har wasan kamun
gwauraye ake yi. Wannan
al’ada ce mai kyau domin tana faɗakar da yaran Hausawa cewa zama babu aure idan
dai ba tare da wani ƙwaƙƙwaran dalili ba, ɗabi’a ce mara kyau.
13. Waƙar Ta-Zama
Wannan waƙa ce wadda ‘yammata
ke gudanar da ita a lokacin kai amarya ɗakinta, ga yadda waƙar take:
Ta zama
ta zama,
Ta
zama ɗauko riga,
Ta
zama ɗauko wando,
Ta
zama ɗauko hula,
Ta
zama ɗauko buta,
Ta
zama ɗauko kwano,
Ta
zama matar aure,
Ta
zama matar lalle.
A wannan waƙar ana koya wa ‘yammata irin rayuwa ta zaman aure da za su samu kansu a
ciki. Yin hakan zai sa su dage su san cewa idan an yi aure, girma na haye wa mutum
kuma lokaci ya yi da za su gwada da fito da duk irin tarbiyyar da iyayensu suka
ba su a baya. Sani da Gobir (2021 sh. 244)
14. Waƙar Tallar
Goro
Wannan waƙa ce wadda ‘yammata
ke rerawa a wajen tallar goro. Waƙar ba ta da amshi sai
dai badawa kaɗai. Ga waƙar:
Goro,
goriya goro sabo
Ga goro
mai kyau
Mallam in
kana son goro
Kawo
sule ko sisi in ba ka goro.
Goro abu ne mai muhimmanci
da ƙima
a rayuwar Hausawa, duk wani biki na al’ada kama daga ɗaurin aure ko bikin suna
duk ana yin amfani da goro wajen aiwatar da su.
Wannan
dalilin ne ya sa akwai maza da mata masu sana’ar sayar da goro a ƙasar Hausa. Wannan waƙar ‘yammata
masu sana’ar sayar da goro ke yin ta a lokacin da suke talla domin su jawo hankalin
masu saye.
15. Waƙar Tallar
Gyaɗa
Wannan waƙa ‘yammata
suke rera ta a wajen tallar gyaɗa, ita ma ba ta da amshi. Ga yadda waƙar take:
Gyaɗa mai sihiri
A ɓara a ga biyu
A murza
a ga huɗu
A tauna
a ji garɗi
Jama’a ga
kirarin gyaɗa nan ba don kin yawa
ba sai ‘yan sarki
Gyaɗa amaro!!!.
‘Yanmata
masu tallar gyaɗa ke rera wannan waƙa a lokacin da suke tallar
tadomin su jawo hankalin masu saye.
16. Waƙar Tallar
Tuwo
‘Yammata
ke rera wannan waƙa wajen tallar tuwo, ita ma ba ta da
amshi sai dai kawai mai rerawa, ga waƙar:
A zo
a sai tuwo
A zo da
kuɗi da kwanon tuwo
Tuwon Zariya
miyar Kaduna
Albasar bakin gulbi.
‘Yammata
ke rera wannan waƙar a lokacin da suke tallar tuwo, duk mai saye sai ya taho
da kwanonsa da kuɗin saye, idan ba haka
ba, sai dai a saka a leda, idan babu kuɗi kuma labari
sai ya sauya
domin Bahaushe na cewa “ko sallah don lada ake yin ta”.
Ambaton “a zo da kuɗi da kwanon tuwo”, ya
tabbatar da cewa Bahaushe ya san ƙimar sana’a kuma faɗar hakan na koya wa yara
wani darasi, wato kada su ba wani tuwo sai ya biya.
17. Waƙar Tallar
Ɗanwake
‘Yanmata
ke rera ta a wajen tallar ɗanwake, ba ta da ‘yan amshi.
Ɗan
wake sharaf da mai da yaji ɗanwake
Ɗanwaken wake ɗan wakiye.
‘Yammata
masu tallar ɗanwake ke rera ta
domin su jawo hankalin masu saye.
18. Waƙar Tallar
Taliya
Ita ma wannan waƙar ‘yammata
ke rera ta a lokacin da suke tallar taliyar Hausa ta kaɗi, ba ta da amshi sai
rerawa kaɗai.
A zo a
sai tali –tali a zo a sai taliya
A zo a
sai ‘yar gidan alaramma mai rangwaɗa
Bakinsa na ƙamshi-ƙamshi saboda ya ci
taliya mai albasa.
‘Yammata
masu sayar da taliyar Hausa ko taliyar kaɗi ke rera waƙar a wurin talla. Ana
kaɗa taliyar ne da garin
alkama ko garin fulawa.
Tana daga cikin abincin Hausawa na gargajiya.
3.0 Muhimmancin Waƙoƙin Yara Mata
Waƙoƙin yara mata suna da
babban matsayi a tsarin al’adun gargajiya na Hausawa yaran suna gudanar da waɗannan waƙoƙin ne a a dandali ko
a gidajen amare. Akasari waƙoƙin suna tafiya tare
da wasanni, saboda haka suna taka muhimmiyar rawa wajen inganta lafiyar jiki ta
hanyar motsa jiki da kawar da gajiya sannan kuma suna koyon juriya da jaruntaka
da kiyaye umurni, a cikin waƙoƙin ana samun umurnin
da idan yaro bai bi ba akwai horon da ake yi masa.
Saboda
haka don guje wa horo
yaran na
ƙoƙarin bin ƙa’idojin da aka
gindaya masu.
Kamar yadda Sani
(2025 sh. 15) ya bayyana, wasannin suna taimakawa wajen ƙulla zumunta a
tsakanin yara suna zama abokai su yi ta zumunci tsakaninsu.
Wasannin da waƙoƙin suna sanya nishaɗi ga yara,
zuciyarsu
ta sami hutu daga duk wani tunani. Wasannin na sanya nishaɗi da ban sha’awa ga
masu kallo ko mai sauraro. Bugu da ƙari,
waƙoƙin na ƙara inganta harshen
Hausa saboda sun zama taska ta adana kalmomin Hausa sannan kuma yaran suna ƙara fahimtar harshen
da kuma
yin magana da harshen. Wasu wasannin da waƙoƙin na yara mata na ƙunshe da tarbiyya ta
samartaka da zaman aure da koya tarbiyya a tsakanin ‘yammata.
Waƙoƙin na koyar da shugabanci
da bin na gaba saboda ko a halin bada waƙoƙin akwai mai ba da waƙa wadda ita ce jagora
sai kuma ‘yan amshi.
Waƙoƙin suna taimakawa wajen
adana da raya al’adun Hausawa saboda suna hana yara yawon banza da yin waƙoƙin banza waɗanda ba su kamata ba.
Waƙoƙin talla kuma suna taimakawa
matuƙa wajen jawo hankalin jama’a su sayi kayan da ake tallata
masu. Yara na koyon dabaru na yin aiki tare da girmama manya da shiryawa ga
nauyin da zai zo masu a gaba a matsayinsu na mata a cikin al’umma, da kuma fahimtar
muhallin da suke ciki.
4.0 Sakamakon Bincike
Wannan nazari mai suna
Waƙoƙin Yara Mata da ‘Yanmata
da Muhimmancinsu a Rayuwar Hausawa ya tabbatar da waɗannan sakamako:
Waƙoƙin yara mata da ‘yammata wani muhimmin ɓangare ne a adabin gargajiya, suna da dogon tarihi kuma suna
nishaɗantarwa tare da koyar da tarbiyya da
gina ilimi da tunani kuma su makamin koyarwa ne.
Waƙoƙin yara mata da ‘yammata suna ɗauke da darussa na tarbiyyantar da mata, ta hanyar koya masu ladabi da
biyayya da tsabta da kulawa da gida da kishin kai da kamun kai da koyon ayyukan
gida na yau da kullum. An
fahimci cewa zubi da salo da tsarin waƙoƙin mata sun sha bambam
da na maza.
Waƙoƙin yara mata da ‘yammata suna ɗauke da tarihi da al’adun Hausawa. Waƙoƙin suna taimakawa wajen ci gaba da wayewar kai ta hanyar inganta harshe da
magana da koyon lissafi mai sauƙi. Daga ƙarshe binciken ya gano cewa waƙoƙin suna raguwa matuƙa a wannan zamani saboda
amfani da wayar hannu da yanar gizo, raguwar zama da yin wasanni a dandali da
tasirin fina-finan gida da na waje da kuma mawaƙa da kaɗe-kaɗen zamani.
5.0 Kammalawa
A taƙaice, waƙoƙin yara da ‘yammata Hausawa na ɗaya daga cikin muhimman abubuwa da suka gina rayuwar yara a fannin al’ada
da tarbiyya da ilmantarwa da tallata kaya da nishaɗi. Ta hanyar waƙoƙin, yara na koyon darussa masu muhimmanci da suka shafi ladabi da tsafta da
biyayya da mutunci da yadda za su zama ‘ya’ya nagari ga iyaye da sauran al’umma.
Bugu da ƙari, waƙoƙin na taimakawa wajen ƙarfafa harshen Hausa da adana al’adu da ɗabi’u da suka gada tun kaka da kakanni. Duk da
sauye-sauyen da aka samu na zamani, waƙoƙin yara ‘yammata sun ci gaba da zama wata hanya wadda al’umma ke amfani da
ita wajen gina tunanin yara da shirya su don rayuwa ta gaba, wannan ya nuna ke nan,
waƙoƙin ba wai don nishaɗi kaɗai ake yin su ba, suna taka
muhimmiyar rawa wajen tsare al’adu da haɓaka ilimi a wurin yara musamman mata, kuma duk da yadda zamani ya sauya,
akwai buƙatar a ci gaba da sarrafa waɗannan waƙoƙi domin su ci gaba da tallafa wa tarbiyya da adabin gargajiya.
Manazarta
Ado,
A. (2019). Ra’o’in Bincike kan Al’adun Hausawa. Katsina: Maɗaba’a Government Printing Press, Nigeria.
Ahmad,
M. K. (1990) Adabin Hausa na Baka. Zaria: N. N. P. C.
Bakura,
A. R., & Sani, A.-U. (2024). Gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a Sikelin Manazartan Ƙarni Na 21. Four
Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on
the Life and Songs of Makaɗa Sa’idu Faru, 3(3), 37–49.
https://doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.005
Ɗangambo, A. (1984). Jagoran Nazarin Waƙa. Ibadan: University Press.
Dunfawa,
A. (1982) “Waƙoƙin Yara a Al’adar Hausa”. Harsunan Nijeriya, 8, 55-78.
Gobir,
Y.A. & Sani, A-U. (2021). Waƙoƙin Hausa Na
Gargajiya. Kaduna: Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. ISBN:
978-978-54888-6-9.
Gusau,
S. M. (1987) Makaɗa da Mawaƙan Hausa. Littafi na ɗaya. Kano: Al-Amin
Publishing Company.
Gusau,
S. M. (1993) Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark Publishers
Limited.
Gusau,
S. M. (2008). Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa. Kano:
Benchmark Publishers Limited.
Jawondo,
A. D. (1998) “Waƙar Baka ta Hausawa da Siffofinta”. Dalhousie Journal of
Hausa Studies, 2 (1), 33-54.
Koko,
S. A. (2008). “Nazarin Wasannin ‘Yan Mata a Al’adar Hausa”. IJLL Journal, 6 (3)
144-159.
Muhammad,
Y. M. (2001). Adabin Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Rufa’i,
A. (2004). Waƙoƙin Yara na Hausa. Kano: Triumph Publishing Company.
Sani,
A-U. & Gobir, Y.A. (2021). Wasanni a Ƙasar Hausa. Kaduna:
Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. ISBN: 978-978-59094-1-8.
Sani,
A-U. (2025). Raujin Hikima: Gurbin Waƙoƙin Gargajiya a
Rayuwar Hausawa. Njinga & Sepé: Revista
Internacional de Culturas, Línguas Africanas e
Brasileiras. São Francisco do Conde (BA), UNILAB, Brazil, 5
(Especial I), 11-23.
https://revistas.unilab.edu.br/index.php/njingaesape/article/view/2340
Umar,
M. B. (1980) Wasannin Tashe. Zaria: N. N. P. C.
Yahaya,
I. Y da Saura (2007). Darussan Hausa Don Manyan Makarantun Sakandare. Littafi
na Ɗaya.
Ibadan: University Press.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.