Citation: Pengcheng Li & Nura Lawal (2026). Daga Sasantawa Zuwa Sassautawa: Yunƙurin ECOWAS na Shiga Tsakanin Juyin Mulkin Jamhuriyar Nijar. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, 5(1), 21-34. www.doi.org/10.36349/tjllc.2026.v05i01.003.
DAGA SASANTAWA ZUWA SASSAUTAWA: YUNƘURIN ECOWAS NA SHIGA TSAKANIN JUYIN MULKIN JAMHURIYAR NIJAR
Pengcheng
Li
Academy
of Regional and Global Governance
Beijing
Foreign Studies University
Da
Nura
Lawal
School
of African Studies,
Beijing
Foreign Studies University
Tsakure
Babbar manufar wannan takarda
ita ce fayyace yanayin rawar da Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta taka a Jamhuriyar Nijar bayan juyin mulkin soja a karo na biyar a cikin tarihin ƙasar. Haka kuma,
an amfani da hanyar bibiyar wasu ayyukan da kuma kafofin yaɗa labarai domin tattaro bayanan wannan bincike. A
sakamakon wannan bincike an lura a ci gabanta na
ayyukanta sun faɗaɗa
zuwa kiyaye tsaron yankin kuma
ECOWAS,
ta samu nasarori wajen shiga tsakani game da juyin mulki da rikici da dama da
aka samu a mambobin ƙungiyar. Bayan da juyin mulkin Nijar
karo na biyar ya faru, ECOWAS ta ƙoƙarta
wajen shiga tsakani. Ta tura tawagar diflomasiyya don gudanar da tattaunawa ta
siyasa, kuma ta saka takunkumin tattalin arziki kan Jamhuriyar Nijar. Haka
kuma, tana tattaunawa kan yunƙurin tura sojoji domin daƙile juyin mulkin soja karo na biyar a
tarihin Jamhuriyar Nijar a ƙarƙashin shugabancin shugaban karba-karba
Shugaban Najeriya Ahmed Bola Tinubu. Amma dukkan matakan da aka ɗauka
ba su haifar da sakamako masu kyau ba, kuma ECOWAS ta canja matsayinta daga ƙoƙarin
sasantawa zuwa sassautawa. Gazawar ƙungiyar
ECOWAS don shiga tsakanin juyin mulki na Jamhuriyar Nijar
ta nuna kasawar ƙungiyar ECOWAS
wajen daidaita manyan batutuwan yammacin Afirka da kuma saɓani
a tsakanin mambobinta. A
shekaru nan an samu yawan juyin mulki a yammacin Afirka,
wannan matsala tana kuma dinga ƙaruwa.
Shi ya sa akwai dimbin muhimmanci don a yi bincike mai zurfi kan dalilin
gazawar shiga tsakani ta ECOWAS. A wannan kundi, an yi nazari bisa ra’ayin
kasancewar ɓangarori
daban daban ta hanyar binciken ayyukan manazarta da aka rubuta, da nazarin
tarihi da sauransu, tare da fito da hujjar ƙungiyar
ECOWAS ta yi sassautawa bayan sassantawar juyin juya mulkin Nijar.
Muhimman
Kalmomi: ECOWAS, Shiga Tsakani, Juyin Mulki, Sasantawa
Gabatarwa
A cikin 'yan
shekarun nan, juyin mulkin da aka yi a yammacin Afirka ya jawo hankulan duniya.
Bayan juyin mulki a ƙasar Mali a watan Agustan 2020, juyin mulkin ko yunƙurin juyin
mulki guda goma
suka faru a
cikin ƙasashe mambobin Ƙungiyar Raya
Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) a cikin shekaru huɗu kawai. Wasu ƙwararru sun kira wannan al'amari "dawowar juyin
mulkin" da ba a taɓa ganin irinsa
ba (Sun, 2023). Wannan ba wai kawai ya haifar da babbar barazana ga zaman
lafiya da tsaro a yammacin Afirka ba, har ma ya kawo ƙalubale ga
rawar da ƙungiyar ECOWAS take takawa wajen kiyaye tsaron
shiyya-shiyya. A ranar 26 ga watan Yuli, 2023, an yi juyin mulkin
soja karo na biyar a tarihin jamhuriyar Nijar. Sojoji sun tsare tsohon shugaba
Mohamed Bazoum gami da sanar da cewa za su kafa Kwamitin Tsaron Ƙasa (CNSP).
Bayan kwanaki biyu, Abdourahamane Tchiani, kwamandan rundunar tsaron fadar
shugaban ƙasar ya bayyana kansa a matsayin sabon shugaban ƙasar Nijar a ƙarƙashin mulkin
soja. Ƙasashen yammacin Afirka da ma ƙasashen duniya
sun mai da hankali sosai kan juyin mulkin. A matsayinta ƙasar da take ɗaukar nauyin shugabancin karɓa-karɓa na ECOWAS. Nijeriya ta ɗauki matakai
cikin sauri a ƙarƙashin shugabancin shugaban ƙasar Bola
Tinubu, inda ya yi ƙoƙarin shiga tsakani a juyin mulkin Nijar. Ta hanyoyi
da dama da suka haɗa da
tattaunawa ta siyasa, saka takunkumi da kuma tura sojoji. Sai dai duk da waɗansu tsauraran matakan da ECOWAS ta ɗauka, ba su samar da sakamako mai kyau ba. Gwamnatin
sojoji ba ta farfaɗo da mulki ba
yadda ya kamata, maimakon haka, ECOWAS tana jin matsin lamba na ciki da waje, a
hankali ta yi sassauci ta janye takunkumi, tare da amincewa da mulkin soja na
Nijar.
Tun lokacin da
aka kafa ƙungiyar ECOWAS a shekarar 1975, musamman da taimakon tsohon shugaban Nijeriya Yakubu Gowon da tsohon shugaban Togo
Gnassingbe Eyadema. Kodayaushe tana goyon bayan haɗin guiwa tsakanin duk ƙasashen Afirka
da burin ƙasashen yammacin Afirka su samu cigaba da kansu.
Bayan haka, bisa ga Ƙa’idojin ECOWAS na “wanzar da
zaman lafiya
da kwanciyar
hankali da tsaro a yankin ta hanyar kyautata dangantaka da ƙasashen maƙwabta” (ECOWAS
Commission, n.d.). Ayyukan ƙungiyar ECOWAS sun faɗaɗa daga haɗin guiwar tattalin arziki zuwa kiyaye tsaron yankin. Haka
kuma, ta cim ma nasarar shiga tsakanin juyin mulki na mambobinta
da dama, kamarsu juyin mulki na Guinea-Bissau a 2012 da kuma juyin mulki na
Gambia a 2016. Sai dai kuma, a lokacin juyin mulkin soja karo na biyar a
Jamhuriyar Nijar a shekarar 2023. Kodayake ECOWAS ta ɗauki tsauraran matakan domin shiga tsakani, amma ya
gagara, daga ƙarshe ECOWAS ta yi sassauci ga wannan juyin mulkin.
Wannan ya fallasa saɓabin da yake
cikin mambobinta da tasirin tsoma baki daga ƙasashen waje
da kuma gazawar gudanar da harkokinta, musamman ma harkokin tsaro na yankin.
Wannan halin ni ’yansu ya nuna wasu ƙungiyoyin
sojoji na yammacin Afirka suna yunƙurin samu mulki ta hanyar da ba dimokuraɗiyya ba,
sannan kuma ƙungiyar ECOWAS tana fuskantar ƙalubale sosai
wajen daidaita harkokin ruɗanin siyasa a
yammacin Afirka.
Waiwaye
Wasu masana da
ƙwararrun na ƙasar Sin sun mai da hankali sosai kan juyin mulkin Nijar na
shekarar 2023. Sun Hong
(2023) ta yi bincike
kan taƙaddama tsakanin ƙasashe da
yankuna da juyin mulkin Nijar wadda ta haifar a mahangar siyasa da
diflomasiyya. Bai (2023) ya bayyana yiwuwar yaɗuwar juyin
mulkin soja a yammacin Afirka daga mahangar tsaron yankin. Jiang Xuan ya mai da
hankali a kan yadda ECOWAS take shiga tsakani a juyin mulkin da ke faru a Nijar, ƙarƙashin tsarin
haɗin guiwa na ƙasa da ƙasa (Jiang,
2023). Li Hongfeng da wasu, sun gudanar da bincike a kan yadda ECOWAS take shiga cikin rikice-rikicen siyasa a ƙasashen masu
magana da Faransanci a Afirka bisa tsarin tsaro na ECOWAS, kuma sun bayyana ƙalubalen da
ECOWAS take fuskanta a cikin gida wajen daidaita ra’ayoyin
mambobinta (Li & Li, 2019). Liu Hongwu da wasu sun bayyana cewa, a baya, ta hanyar tura Kwamitin Kula da Tsagaita Wuta, aka
samu nasarar wajen shiga tsakanin juyin mulki a Sierra Leone da Guinea-Bissau,
wanda ya nuna muhimmiyar rawar da ƙungiyoyin ECOWAS take takawa wajen kare zaman lafiya
da kwanciyar hankali a shiyya-shiyya (Liu & Deng, 2014).
Huang Rui ya
yi amfani da misalin juyin mulki na Liberia, inda ECOWAS ta ci nasarar shiga
tsakani sau biyu, don binciken hanyoyin da dabarun da ECOWAS take amfani da su
wajen magance rikice-rikice cikin gida a ƙasashen mambobinta (Huang, 2021). Akwai labaru da
dama a kafofin yaɗa labarai a ƙasashen waje
(Yabi, 2023). Ban da waɗannan kuma,
wasu masana sun yi la’akari sosai da tarihin juyin mulki a Jamhuriyar Nijar.
Lamin ya nuna cewa tsarin tsaro na ECOWAS yana fuskantar matsaloli wajen
magance rikice-rikicen yanki bayan yaƙin cacar baki, don haka ana buƙatar
sauye-sauye cikin gaggawa (Lamin, 2006).
Oluropo da
wasu sun yi imani da cewa yawan juyin mulki a ƙasashen
yammacin Afirka yana ƙaruwa, inda suka nuna cewa manyan ƙasashen yankin
kamar Nijeriya sun gaza cim ma nasarar tattaunawa da
daidaita muradun ɓangarori yayin
juyin mulkin, hakan ya kawo cikas ga sakamakon shiga tsakani (Oluropo et al.,
2024). Sowale da wasu sun ci gaba da nazari daga mahangar siyasa, inda suka
duba yadda lamarin Nijar ya kawo cikas ga ci gaban dimokuraɗiyya a yammacin Afirka (Sowale, 2024). Masanin
siyasa Obasi ya bayyana cewa, takunkuman da ECOWAS ta sanya wa Nijar sun yi
tsauri fiye da yadda ya kamata.
Domin sun fi shafar
jama’a maimakon gwamnatin soja, kuma babu wani ingantaccen tsari na ƙarfafa guiwar mulkin soja domin su maido da gwamnatin dimokuraɗiyya, wanda ya sa shiga tsakanin ECOWAS bai ba da
sakamakon mai kyau ba (Obasi, 2023). Waɗannan ayyuka sun bayar da haske sosai a kan wannan bincike. Haka
kuma, masana daga ƙetare sun fi
mayar da hankali a kan tarihin ci gaban juyin mulki a Nijar, amma ba su taɓo abin da ya
shafi juyin mulkin
da ya faru a shekarar 2023 ba.
Wannan dalili ya bayar da dama gudanar da wannan nazari.
Tarihi na Tsarin Shiga Tsakani na ECOWAS da Manyan
Matakanta
Tsarin shiga
tsakani na ECOWAS shi ne ɗaya daga cikin
muhimman matakan kiyaye tsaron yankin a duniya. Tun daga kafuwarta a shekarar
1975, ayyukan ECOWAS sun faɗaɗa daga haɓaka haɗin guiwar tattalin arziki har zuwa kiyaye tsaron yankin.
Wannan sauyi ba kawai
shi ne sakamakon
tasirin yaƙin cacar baki, kuma yana da alaƙa da ruɗanin siyasa tsakanin ƙasashen
yammacin Afirka da al’adunsu da harshensu.
ECOWAS ta kafu
ne a shekarar 1975 da taimakon ƙasashen
yammacin Afirka kamar Nijeriya da Togo, tare da burin ƙarfafa haɗin guiwar tattalin arziki na yankin. A lokacin da aka
kafa ƙungiyar, an tsara “Dokar Lagos” (Treaty of
Lagos) wadda ta bayyana “ƙarfafa haɗin guiwar tattalin arziki da bunƙasa” a matsayin
babban burin ƙungiyar. Haka kuma, tana mai da hankali a kan gina
kasuwar haɗin guiwar yanki ta hanyar kawar da shingayen haraji a
cikin samar da ingantattun gine-ginen ababen more rayuwa. Wannan sabuwar ƙungiya ta fuskanci barazanar daga cikin gida da
waje, wanda ya tilasta ta faɗaɗa ayyukanta zuwa fannin tsaro (Li & Li, 2019).
A fagen
harkokin ƙasa da ƙasa, ƙalubalen fafatawa tsakanin Amurka da Tarayyar Soviet
ya mayar da
yankin
yammacin Afirka da kewayensa dandalin gwagwarmayar ra’ayin siyasa. A cikin
shekarun 1970, rikice-rikicen da suka faru a Angola da kuma Chad suna haifar da
yiwuwar bazuwar rikice-rikicen zuwa yankin yammacin Afirka. Wanda hakan yake kawo barazana ga zaman lafiyar yankin. Har ila yau, an ba da muhimmanci ƙwarai ga
ECOWAS a matsayi mai ƙarfin wajen yaƙi da mulkin mallaka na ƙasashen
duniya. Saboda haka, muhimmancin ECOWAS wajen kiyaye tsaro a yankin da kuma
daidaita manyan batutuwan yankin ya fito fili. A cikin ƙungiyar, bayan
da Nijeriya ta ƙare Yaƙin Basasa, ta bunƙasa cikin
sauri ta hanyar amfani da tattalin arzikin man fetur don zama babban ƙasa a yanki,
tana ƙoƙarin jagorantar ECOWAS domin faɗaɗa tasirinta a
yankin. A ɓangare guda,
Faransa tare da ƙasashen yammacin Afirka masu amfani da harshen
Faransanci suna ƙoƙarin kawo tsaiko ga cigaban Nijeriya ta hanyar amfani da tsarin tsaro na haɗin guiwa (Sun, 2023).
A cikin wannan
yanayi, ƙasashe mambobin ECOWAS sun sanya hannu kan jerin
yarjejeniyoyin tsaro na haɗin guiwa, waɗanda suka zama ƙa’idojin tsaro a ƙungiyar. Tarihin cigaban tsarin shiga tsakani na
ECOWAS ya rabu zuwa muhimman matakai guda uku bisa lokutan sanya hannu
yarjejeniyoyi guda uku. Wanda kowanne daga cikin waɗannan lokutan yana wakiltar wata barazana ga tsarin
shiga tsakanin ECOWAS. Su ne rikicin Togo da Ghana da juyin mulkin Liberia, da
yaƙin basasa na Sierra Leone. Wannan ya nuna cewa
ECOWAS ta fara gyare-gyare saboda akwai barazana gare ta.
An rattaba
hannu a kan Yarjejeniyar Rashin Kai wa Juna Hari (Protocol
on Non-Aggression) a 1978 ne a cikin yanayin rikicin iyaka tsakanin Togo da
Ghana, wanda ya nuna farkon samuwar tsarin shiga tsakani na ECOWAS a
rikice-rikice. Wannan yarjejeniya ita ce ta farko da ta fayyace ƙa’idar warware
rikice-rikice ta lumana tsakanin ƙasashen ECOWAS. Haka kuma, ta buƙaci a miƙa rikicin da ba a iya warwarewa cikin lumana zuwa
kwamitin ECOWAS domin ta yanke hukunci. Wannan yarjejeniya ba ta ƙunshi
takunkumi ko tsarin shiga tsakani na ƙarfin soja ba, wanda hakan ya bar hatsari a tsarin, wanda shi kuma ne zai kawo matsaloli a gaba.
A farkon
1980s, yaƙin wakilai tsakanin Amurka da Rasha ya ƙaru, juyin
mulki da rikice-rikicen suka dinga faruwa a Afirka ta Yamma. A lokacin juyin
mulkin Liberia na 1980, bisa yarjejeniyar da aka sanya hannu, ECOWAS ba ta da
ikon fiye da yin la’anta
ko Allah-wadai kawai. A
matsayin martani, ƙasashen ECOWAS suka rattaba hannu a kan Yarjejeniyar Taimaka da Kiyaye Tsaron Juna
(Protocol on Mutual Assistance in Defense) a 1981, wadda ta wakilci aka shiga
mataki na biyu na cigaban tsarin shiga tsakani na ECOWAS. Yarjejeniyar ta
bayyana cewa za a taimaki kowace mambar ƙasar da ta fuskanci barazana ko hari, wanda ta
inganta ƙarfin ECOWAS wajen tinkarar matsalolin tsaro a
yankin.
Bayan ƙarewar Yaƙin Cacar Baki
a 1990s, matakan shiga tsakani da ECOWAS take ɗauka suka fara fuskantar tambayoyi kan dalilin
kasancewarta. A 1999, an sanya hannu a kan Yarjejeniyar Rigakafin Rikici, Sarrafawa,
Warware Matsaloli da Kiyaye Tsaro (Protocol Relating to the Mechanism for
Conflict Prevention, Management, Resolution, Peacekeeping and Security). Wadda
ta ƙara sabbabin hukumomi kamar su Kwamitin
Tsaro da Shiga Tsakani (Mediation and Security Council of ECOWAS), da na
Majalisar Dattijai (Council of the Wise), da na Sojojin Standby Force. Da
tsarin gargaɗi, domin tabbatar da cewa ECOWAS na iya yanke
hukunci da sauri a kan yanayin tsaro na ƙasashe
mambobinta bisa doka da yarjejeniya. Wannan mataki ya ba da tabbaci ga matakan
tura sojoji da ECOWAS take ɗauka (Huang,
2021:16),tare da bai wa Kwamitin Tsaro da Shiga Tsakani
ikon shiga tsakani cikin kowanne irin rikici a madadin ECOWAS. Wanda hakan ya
ba ECOWAS irin iya gudanar da ayyukan sojoji ba na wata ƙasa kadai ba, na duk yankin yammacin Afirka (Huang, 2021).
Daga bisani kuma,
ECOWAS ta ƙara da wasu muhimman takardu, ciki har da
Yarjejeniyar Ƙarin Tanadi a kan Dimokuraɗiyya da Kyawawan Shugabanci (Protocol on Democracy
and Good Governance) a 2001. Haka kuma, Tsarin Rigakafin Rikici na ECOWAS
(ECOWAS Conflict Prevention Framework) na 2008, wanda ya nuna canjin tsari daga
shiga tsakanin rikici zuwa rigakafin rikici tun kafin faruwa. Kodayake, an
inganta tsarin shiga tsakani na ECOWAS sau da dama, amma har yanzu tsarin yana
fuskantar manyan ƙalubale a cikin yanayin komowar juyin mulki da yake
afkuwa a yankin Afirka ta Yamma a ’yan shekarun nan. Saboda haka, yana da
muhimmanci a yi bincike a kan manyan matakan da ake amfani da su wajen shiga
tsakani, domin a fahimci yadda tsarin yake aiki da kuma gazawarsa.
Manyan Matakan da ECOWAS Take Amfani da Su Wajen Shiga Tsakani
Idan akwai
rikice-rikice a cikin ƙasashe mambobi, ECOWAS a kan ɗauki matakai uku don shiga tsakani: tattaunawar
siyasa da saka takunkumi da kuma tura sojoji. Wannan ɓangare zai yi bayani a kan kowanne daga cikin waɗannan matakai.
Tattaunawar
Siyasa
ECOWAS tana ɗaukar matakin tattaunawar siyasa a matsayin hanya ta
farko wajen sasanta rikice-rikice. Wannan tsarin yana dogara ne a kan
gudanar da tarurrukan shugabanni da taron ministoci da kuma ƙirƙirar wa ƙungiyoyin aiki
na musamman, domin samar da dandali waɗanda babu son kai ga ɓangarorin da suke rikici. A aikace, tattaunawar
siyasa tana aiki ta hanyoyi uku: shiga tsakani ta taron shugabanni da Majalisar
Dattijai (Council of the Wise), da kuma daidaitawa ta ƙungiyoyin aiki
na musamman.
(1) Taron
Shugabannin Ƙasashe da Gwamnatoci na ECOWAS, wanda hedkwatarsa
take a Abuja, babban birnin Nijeriya, shi ne babban mataki na yanke shawara a
cikin ƙungiyar. Ana gudanar da babban taro sau biyu a
kowace shekara, inda ake bayyana matsaya ta haɗin guiwa ta hanyar fitar da sanarwa tare ko kuma
tura tawaga ta musamman. Alal misali, a cikin juyin mulkin ƙasar Gambiya
na shekarar 2016, taron shugabannin ECOWAS ya yanke hukuncin ƙin amincewa da
gwamnatin Yahya Jammeh (United Nations, 2017), tare da fitar da sanarwar da
take yin Allah wadai da shugaba Jammeh da ya sha kaye amma ya ƙi sauka daga
mulki, wanda hakan ya taimaka sosai wajen warware rikici cikin ruwan sanyi.
(2) A
matsayinta na ginshiƙi mai muhimmanci a tsarin shiga tsakani na ECOWAS, “Majalisar
Dattijai” (Council of the Wise) tun bayan kafuwarta a
hukumance a shekarar 2004, tana taka rawar gani wajen gudanar da “hanyar
diflomasiyya ta biyu”. Wannan tsari yana ƙunshe da
wakilan kowace mambar ƙasa ce, inda ake zaɓar tsoffin shugabannin ƙasa masu
mutunci, shugabannin addini, ko manyan jakadu da suka yi fice, domin su zama
gadoji tsakanin ɓangarorin da suke
rikici. Ta hanyar hanyoyi diflomasiyya ba na hukunce ba. Tsarin wakilcin ya
nuna daidaito na siyasar yankin: Nijeriya ta tura tsofaffin shugabanni ƙasa kamarsu
Olusegun Obasanjo da Muhammadu Buhari a jere har sau uku; ƙasashen da suke
magana da Faransanci kamar Côte d’Ivoire sun tura tsohon firaminista Daniel
Kablan Duncan, yayin da Senegal ta tura babban limamin ƙasar Grand
Mufti Mballo Lo. Haka kuma, shigowar tsohuwar shugabar Liberia, Ellen Johnson
Sirleaf, wadda ta samu lambar yabo ta zaman lafiya ta Nobel a 2011, ta ƙara wa wannan
majalisa ƙima da karɓuwa a idon
duniya. A aikace, lokacin da akwai matsalolin hanyoyin diflomasiyya na hukunci,
Majalisar Dattijai ta yi nasarar shiga tsakani, kamar yadda aka gani a cikin
rikicin Mali na 2013, inda ta taka rawa wajen ƙulla
yarjejeniyar zaman lafiya ta Ouagadougou, wani abin koyi a tsarin tsaron
yankin.
(3) Ƙungiyoyin aiki
na musamman na ECOWAS an kafa su bisa Tsarin Rigakafin Rikici na ECOWAS ta
2008, sashi na 14 game da kafawar Kwamitocin na Musamman. Wato amfanin da ƙungiyoyi na
wucin-gadi da ƙwarewa don cim ma matsaya guda a kan magance
rikice-rikice. A fagen ruɗanin siyasa, ƙungiyar ƙasashe guda uku
zuwa biyar waɗanda suke da
wakilci na yankin za su jagoranci ƙungiyar. Kamar yadda aka samu a lokacin
juyin-juya-halin na Mali a shekarar 2020, wanda ƙungiyar aiki
na musamman ta ƙunshi tawagar Côte d’Ivoire (yanki mai magana da Faransanci), Nijeriya
(yanki mai magana da Ingilishi), da Nijar (wakilin ƙasashen Sahel).
Haka ya taimaka wajen guje wa rikice-rikicen siyasa na yankin. A matakin ƙwararru da
masana, ƙwararrun dokoki da masu bayar da shawara a kan harkokin
tsaro sun taimaka sosai wajen inganta tsarin shiga cikin rikice-rikicen.
Saka
Takunkumin Tattalin Arziki
Saka
takunkumin tattalin arziki wani mataki ne mai ƙarfi da ƙungiyar ECOWAS
ta ɗauka ban da tattaunawar siyasa da shiga tsakani na
soja. Wannan ya ƙunshi takunkumin hada-hadar kuɗi (ciki har da daskare ƙadarorin ƙasashen waje
da dakatar da damar yin amfani da tsarin biyan kuɗi da share fage). Sai kuma, takunkumin kasuwanci
(kamar hana fitarwa da hana shigar da kayayyaki) da rufe iyaka da sauran manyan
matakan takunkumi. Kwamitin Tsaro da Shiga Tsakani ne yake gabatar wa ECOWAS
takunkumi kuma za a iya sanyawa idan aka amince da shawarar kashi biyu bisa uku
(ECOWAS, 1999). Takunkumin tattalin arziki ana gudanar da shi a hankali a
hankali, wato, sannu a hankali yana yin matsin lamba a kan ɓangarorin da suke rikici a cikin tsari na
"gargaɗin saka
takunkumi-takunkumi na wasu fanonni-cikakken takunkumi a duk fannoni" don
tilasta musu komawa kan tattaunawa. Ƙungiyar ECOWAS ta taɓa sanya wa ƙasashe mambobinta takunkumin sau da yawa. Misali,
lokacin da gwamnatin mulkin soja ta Mali ta ƙi gudanar da
zaɓuɓukan da aka tsara a shekarar 2022, ƙungiyar ECOWAS
ta daskarar da ƙadarorin shugabannin sojoji da suka yi juyin mulki
tare da rufe iyakokin ƙasar, da dakatar da kasuwanci da kuma dakatar da haƙƙinsu na ɗaukar kuɗi a babban
bankin ƙasashen yammacin Afirka (China Military Online,
2022).
Amfani
da Ƙarfin Soja
A matsayin
matakin ƙarshe na tsarin shiga tsakani na ECOWAS, shiga
tsakani na soja yana da ma'ana mai kyau da mara kyau. A gefe guda kuma, ta taka
muhimmiyar rawa wajen shiga tsakani rikice-rikice, wanda yake nuna irin ƙimar da take
da shi wajen maido da tsarin mulki cikin ƙanƙanin lokaci. A ɗayan hannun
kuma, ta dogara ga ƙarfin manyan ƙasashen yankin, musamman Nijeriya. Wannan zai
haifar da matsalar rashin daidaiton matsayi a cikin ƙungiyar, ya
yiwu zai kawo saɓani. Ayyukan
shiga tsakani na soja na farko na ECOWAS ya dogara ne a kan ECOMOG da aka kafa
a lokacin yaƙin basasar Liberiya a 1990. ECOMOG ya karɓi tsarin shiga tsakani na wucin gaɗi da ƙa'idar tura sojoji na sa kai. A aikace, Nijeriya ta
tura yawancin sojoji da kuma samar da galibin kasafin kuɗi cikin ayyukan, da kuma ikon sarrafawa kan ECOMOG
sosai (Liu & Deng, 2014). Wannan tsari ya kawo magance rikicin yanki, amma
shugabancin Nijeriya a ciki ya jawo shakku daga dukkan ƙasashen
duniya.
Haka
kuma, domin shawo kan
wannan gazawar, ECOWAS ta kafa sojojin Standby Force a hukumance a shekarar
2005, wanda ake samar da nufin daidaita rabon iko tsakanin ƙasashe
mambobin ƙungiyar ta hanyar tsarin soja na haɗin guiwa na ƙasa da ƙasa. Idan aka kwatanta da ƙa'idar ta
ECOMOG, ana buƙatar ƙasashe mambobin su ƙaddamar da
sojoji da kayan soja a gaba da kuma kafa tsarin umarni na dindindin don rage
lokacin tura sojoji. Duk da haka, ainihin aikinsa har yanzu yana fuskantar matsala.
Kodayake yana jaddada daidaiton haɗin guiwar masu
magana da Faransanci da masu magana da Ingilishi (alal misali, hedkwatarsa tana
Abuja, Nijeriya, amma yawancin kwamandojin su janar-janar na ƙasashe masu
magana da Faransanci ne). Sannu a hankali Nijeriya ta rage tallafin ga ayyukan
Standby Force, saboda taɓarɓarewar tattalin arziki na cikin gida da matsin lamba
na yaƙi da ta'addanci. Haka kuma, rarrabuwar kawuna
tsakanin ƙasashe mambobin ƙungiyar ya sa
abu ne mai wuya a cim ma matsaya guda a kan shawarwarin haɗin guiwa, lamarin ya kawo hatsari ga ƙungiyar ECOWAS
don ta gaza yin ingantaccen tsarin shiga tsakanin soja bayan juyin mulkin da
aka yi a Nijar.
Juyin
Mulkin Soja na Jamhuriyar Nijar Karo na Biyar da Matakan Shiga Tsakani da
ECOWAS Ta Ɗauka
Tsarin shiga tsakani kan rikice-rikice da manyan
matakan da ECOWAS ta ɗauka ya nuna
cewa, tsarin shiga tsakani na ECOWAS ya samu ingantawa sosai bayan shekaru da
dama na cigaba. Sai dai kuma, ingancin wannan tsarin ya dogara matuƙa da haɗin kai tsakanin mambobin ƙasashe da kuma
zaman lafiyar tsarin ruɗanin siyasar
yankin. A cikin yanayin dawowar juyin mulki a yankin Yammacin Afirka tun daga
2020, juyin mulkin soja da ya faru a Nijar a shekarar 2023 ya fallasa
matsalolin cikin gida da na ƙungiya
Yanayin da Cigaban Juyin Mulkin Soja na Jamhuriyar
Nijar Karo na Biyar
Juyin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar shi ne karo na
biyar da aka yi juyin mulki a tarihin ƙasar. A matsayinta na ɗaya daga cikin ƙasashe masu talauci a yankin Sahel, juyin mulkin
Nijar na 2023 ya samo asali ne daga tarihinta, tare da sauye-sauyen tsarin
tsaro a yankin. Yanayin juyin mulkin soja na Jamhuriyar Nijar karo
na biyar Tarihin siyasar ƙasar tun bayan samun ’yancin kai a shekarar 1960 yana
cike da ruɗani. Inda
tasirin rundunar soja, saɓanin ƙabilu da kuma
matsalolin cigaban tattalin arziki suka kawo rashin kwanciyar hankali a siyasa.
A shekarar 2010, Nijar ta ƙaddamar da sabon kundin tsarin mulki ta hanyar kaɗa ƙuri’a, inda aka sauya tsarin mulkin ƙasa daga
tsarin semi-presidential zuwa tsarin presidential tare da kafa majalisar dattawa.
Wanda hakan ya kasance wani cigaba a tafiyar dimokuraɗiyyar ƙasar. A shekarar 2021, Shugaba Mohamed Bazoum ya hau
karagar mulki ta hanyar babban zaɓe, wanda ya
nuna karon farko da aka samu miƙa mulki cikin lumana ta hanyar zaɓe. Sai dai yunƙurinsa na sauya manyan kwamandojin soji yayin
mulkinsa ya jawo gagarumin saɓani tsakanin
gwamnati da sojoji, wanda ya zama asalin dalilin juyin mulki (Sun, 2023).
A fannin tattalin arziki, Nijar na matuƙar dogaro kan
fitar da ma’adinan Uranium, amma yawancin ayyukan haƙar albarkatun ƙasar suna ƙarƙashin ikon
kamfanonin ƙasashen waje, wanda hakan ya janyo zargidaga cikin
gida cewa dokokin gwamnati suke rashin adalci. Bayan haka, matsalar rashin
guraben aikin yi ga matasa sun ƙara haifar da rashin jin daɗi a cikin al’umma. Takunkuman da ECOWAS ta ƙaƙaba wa ƙasashen da
suke maƙwabtaka da Nijar kamar Mali da Burkina Faso sun ƙara haddasa
tangarɗa ga hanyoyin
ciniki a yankin, lamarin da ya tsananta matsin tattalin arziki da ƙasar take
fuskanta.
A fannin tsaro, Nijar na fuskantar barazanar
ta’addanci daga yankin Sahel wanda yake tsananta kullum. Duk da kasancewar
dakarun Faransa da na Amurka a ƙasa na tsawon lokaci, ba su iya kyautata yanayin
tsaron ƙasar yadda ya kamata ba. Maimakon haka, ayyukansu
sun haifar da asarar rayuka da dama na fararen hula. Lamarin da ya jawo rashin
amincewar jama’ar Nijar a kan ƙasashen Turai da Amurka. Haka kuma, jerin juyin
mulki da suka faru a ƙasashen yammacin Afirka daga 2020 zuwa 2023 sun zama
tamkar misalai ga Nijar. Sojoji masu juyin mulki na amfani da adawa da ƙasashen yamma
don samun goyon bayan jama’a. Sannan kuma, suna neman taimakon ƙungiyar Wagner
ta Rasha domin samun kariya. Wannan ya nuna raunin tasirin ECOWAS, kuma ya ƙarfafa zukatan
sojojin Nijar wajen yin juyin mulki.
Ci gaban Juyin Mulkin Soja na Jamhuriyar Nijar Karo na biyar,
wato a ranar 26 ga Yuli, 2023, rundunar tsaron shugaban ƙasar Nijar ta
yi juyin mulki a babban birnin Niamey, cewa “Gazawar yaƙi da ta’addanci” da “Cin amanar
muradun ƙasa” ne dalilin hakan. Shugaban rundunar tsaron shugaban
ƙasa, Abdourahamane Tchiani ya jagoranci sojojinsa
suka mamaye fadar shugaban ƙasa, inda suka tsare shugaban ƙasa, Mohamed
Bazoum, tare da iyalinsa. Sannan kuma, suka sanar da cewa sun hambarar da
gwamnatin da aka zaɓa ta hanyar dimokuraɗiyya, tare da kafa “Majalisar Tsaro ta Ƙasa” (CNSP) domin
karɓar mulki.
Rundunar juyin mulki ta fitar da wata sanarwa a talabijin na ƙasa, inda ta
zargi gwamnatin Bazoum da “yarda da ikon mallakar Faransa wajen ƙwace
albarkatun ƙasa,” tare da yin alƙawarin “maido da tsaron ƙasa.”
A rana ta gaba, sojojin juyin mulki sun ƙulle iyakoki,
suka sanya dokar hana fita, sannan suka katse wasu hanyoyin sadarwa na duniya.
A ranar da abin ya faru, ECOWAS ta fitar da wata sanarwa da kakkausar murya,
inda ta la’anci yunƙurin karɓar mulki ta
hanyar amfani da ƙarfin soji, tare da kiran a saki Shugaba Bazoum ba
tare da wani sharaɗi ba (ECOWAS
Commission, 2023). Ƙungiyar Ƙasashen Duniya (UN), Ƙungiyar
Tarayyar Afirka (AU), da Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) sun bayyana tir da abin
da ya faru. A cikin ’yan kwanaki, yayin da ECOWAS take ci gaba da
tattaunawa da sojojin Nijar ta hanyoyi da dama, ta kuma ƙaddamar da
takunkumi a kan gwamnatin soja ta Nijar.
Sai dai, rundunar sojin ta nuna ƙarfin hali
wajen mayar da martani. Shugaban gwamnatin soja Abdourahamane Tchiani ya zargi
ECOWAS da cewa: “Manufar takunkumin ba wai neman mafita ba ce, sai
dai kunyata mu ne da tilasta mana don miƙa wuya" (Okafor, 2023). Ya kuma yi kira ga ’yan Nijar da
su haɗu don
fuskantar waɗannan takunkumin. Sannan
a ranar 21 ga watan Agusta, gwamnatin sojin ta sanar da wani shirin wucin-gaɗi da zai miƙa mulki ga gwamnati ta dimokuraɗiyya cikin shekaru uku. ECOWAS ta ƙi amincewa da
wannan shiri daga baya. Yayin da shirin ECOWAS na shiga tsakani ta hanyar soja
da takunkumin da aka sanya ba su kawo sakamakon da ake fata ba. Gwamnatin sojin
Nijar ta fara ƙarfafa mulkinta ta hanyar neman goyon baya daga ƙasashen waje.
Rundunar sojin ba wai kawai ta soke yarjejeniyar haɗin guiwa da Faransa ba ne, har ma ta kori jakadun
Faransa daga ƙasar. A watan Satumba na shekarar 2023, tare da haɗin guiwar gwamnatocin soja na Burkina Faso da Mali,
Nijar ta kafa haɗin guiwa mai
suna Ƙungiyar Ƙasashen Sahel (Alliance of Sahel States). Bayan haka
kuma, ECOWAS ta fara sassauta matsayinta, wato, ta rage yawan tsokaci kan juyin
mulkin Nijar, kuma takunkumin da take aiwatarwa ya fara fuskantar suka daga ƙungiyoyin jin ƙai na duniya.
A ƙarƙashin matsin lamba, a ranar 24 ga Fabrairu 2024,
ECOWAS ta gudanar da taron shugabanni inda ta yanke shawarar janye dukkan
takunkumin da aka sanya wa Nijar. Wannan wani mataki ne da yake nuna cewa
tsarin shiga tsakani da aka tsara ya gaza kwata-kwata. A ranar 29 ga Janairu,
2025, bayan dogon lokaci da aka dakatar da su daga matsayin ƙasashe mambobi
na ECOWAS, Nijar, da Burkina Faso da Mali suka fitar da sanarwar haɗin guiwa inda suka bayyana ficewarsu daga ECOWAS
gaba-ɗaya. Wannan
lamari ya sanya ECOWAS cikin babbar matsala mafi tsanani tun kafuwarta ta
rarrabuwar kai, da ayyukansu na daidaita batutuwan yanki sun samu shakku daga ɓangarori da dama.
Matakan da ECOWAS ta Ɗauka
Don Shiga Tsakani a Juyin Mulkin Nijar
A yayin juyin mulkin da ya faru a Nijar a shekarar
2023, ECOWAS ta bi tsarin matakan shiga tsakani ta aiwatar da dabarar kamarsu
gudanar da tattaunawar siyasa, sanya takunkumin tattalin arziki, da shiga
tsakani na ƙarfin soja. Sai dai, wannan tsarin shiga tsakani ya
fara durƙushewa sannu a hankali saboda saɓanin da yake tsakanin ƙasashe mambobi
da tasirin daga ƙasashen waje.
Tattaunawar Siyasa
ECOWAS ta fara aiwatar da tsarin tattaunawa ta
siyasa cikin gaggawa bayan juyin mulki a Nijer, tana ƙoƙarin warware
rikicin ta hanyar amfani da hanyoyin diflomasiyya masu yawa. Don ƙarfafa
tattaunawa, ECOWAS ta tura wata tawaga a ranar 3 ga Agusta 2023 wadda ta ƙunshi tsohon shugaban
mulkin sojan Nijeriya, wato Abdussalam Abubakar da Sarkin Musulmi Sa’adu
Abubakar da shugaban ECOWAS Touré, domin zuwa Niamey don tattaunawa da
gwamnatin soja. Duk da cewa tawagar ta yi doguwar ganawa mai tsawon awanni 5 a
filin jirgin sama da gwamnatin soja, ba a ba su izinin shiga cikin birnin don
tattaunawa a hukumance da shugabannin gwamnati ba (Premium Times, 2023).
Halin Gwamnatin soja na ƙin tattaunawa
ya sa tattaunawar siyasa ta shiga cikin yanayi na gazawa. Kodayake a ranar 9 ga
Agusta 2023, sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi ya yi nasarar gudanar da
tattaunawa tare da gwamnatin soja na Nijar a matsayin shugaban addini na
yankin, amma wannan haɗin kai bai
haifar da babban sakamako ba. Domin gwamnatin soja ba ta yi wani sassauci a kan
muhimman batutuwa kamar lokacin canjin mulki da miƙa mulki ba. A
yanayin wannan gazawar tattaunawar siyasa, ECOWAS ta canza dabarunta cikin
gaggawa, ta fara matsa lamba ta sanya takunkumi na tattalin arziki a kan
gwamnatin sojojin Nijar, da fatan za a tilasta su komawa kan tattaunawa.
Tasirin Takunkumin a Kan Tattalin Arziki
Bayan tattaunawar siyasa ta farko ta ci tura, ECOWAS
ta fara sanya takunkumi a hukumance a kan Nijar a ranar 30 ga Yuli 2023.
Matakan sun haɗa da rufe
iyakokin ƙasa da sama, daskarar da ƙadarorin kuɗi, da katse wutar lantarki (Alake, 2023). Domin
kusan kashi 70 cikin 100 na wutar lantarkin Nijar ya dogara da Nijeriya ne. Wannan
takunkumin ya haifar da mummunan tasiri ga tattalin arziki da rayuwar yau da
kullum a Nijar a farkon aiwatar da shi. A matsayinta Nijar da ba ta iyaka da
teku, dogaronta ga tashar jiragen ruwa na ƙasar Nijeriya da Benin ya sa ba ta da dabara don yaƙi da munanan
sakamakon takunkumi. Farashin kayan masarufi, abinci da man fetur a Nijar ya
tashi ƙwarai.
Har ila yau, munanan tasirin takukumi ga ECOWAS ita kanta ya
fara bayyana ba da jimawa ba. A farin farawa, gwamnatin soja ta Nijar ta yi
amfani da halin rashin kwanciyar hankali na cikin gida don zargi aikin sabon
mulkin mallaka na Faransa take yi. Inda tana ƙoƙarin wayar da kan
jama’a don su yi haɗin guiwa tare
da gwamnati wajen kawar da ‘yan mulkin mallaka. A sakamakon haka, an sha yin
zanga-zangar goyon bayan juyin mulkin soja da adawa da dakarun Faransa a birnin
Niamey da Agadez. Na biyu, gwamnatin mulkin soja ta ɗauki matakai na rage dogaro da tattalin arzikin
ECOWAS. Ta hanyar ƙarfafa haɗin kai da ƙasashen Sahel
kamar Mali da Burkina Faso, da kuma buɗe iyakar ƙasa da
Aljeriya a arewa don ƙirƙirar sabbin hanyoyin kasuwanci. Haka kuma, tana
neman tallafi daga rundunar Wagner ta Rasha domin rage matsin lambar takunkumin
tattalin arziki. A lokaci guda kuma, hauhawar farashin abinci ya sa yawan
mutanen da ke fama da rashin abinci a Nijar ya ƙaru, kuma rufe
iyakoki ya ƙara matsalar ‘yan gudun hijira. Waɗannan matsalolin jinƙai sun ƙara haifar da
rashin jin daɗin jama’a a
kan takunkumin da ECOWAS ta sanya. Wanda hakan ya sa gwamnatin soji ta sami
wani goyon bayan ƙasa da ƙasa. A taƙaice, matsin lamba na tattalin arziki daga ECOWAS ya
nuna gazawarsa saboda ta kasa tinkarar matsalar canjin fasalin tsarin siyasar
yankin. Wanda hakan ya sa ECOWAS tana tunanin ɗaukar matakin tura sojoji a ƙarshe.
Yunƙurin
Tura Sojoji
Saboda kasa cim ma matsaya guda a tattaunawar siyasa
da kuma gazawar takunkumin tattalin arziki, ECOWAS ta gudanar da Taron
Shugabannin Kwamitin Kiyaye Tsaro (Meeting of the ECOWAS Committee of Chiefs of
Defence Staff) da Taron Shugabanni na Musamman a farkon watan Agusta, domin
tattauna shirin shiga tsakani na ƙarfin soja a Nijar. Sun sanya ranar 6 ga watan
Agusta a matsayin lokaci na ƙarshe da sojojin Nijar za su dawo da mulkin dimokuraɗiyya tare da saki Shugaba Bazoum, amma rundunar
sojin ba ta mayar da martani gare ta ba.
ECOWAS ta ci gaba da matsa lamba, a ranar 12 ga
watan Agusta, ƙasashen Côte d’Ivoire da Benin da Senegal da Nijeriya sun tura
dakarun soji cikin hanzari don jiran umurni. Hakazalika, daga baya mambobin ƙasashen ECOWAS
sun fara samun saɓani kan batun
tura sojoji. Nijeriya, wadda take matsayin shugaban ƙungiyar, ta
fara nuna jinkiri saboda al’ummar Hausawa da suke maƙwabtaka da ƙasar Nijar sun
nuna adawa da yunƙurin tsoma bakin soja. A cikin Senegal, ɗan majalisar na adawa Thierno Alassane Sall ya
bayyana a fili yana gargaɗin cewa tsoma
bakin soja na iya tayar da “ɗaya daga cikin
mafi munin yaƙe-yaƙe a yankin” (Le Monde, 2023). Ƙasashen Mali
da Burkina Faso kuwa sun bayyana a fili cewa idan aka yi yaƙi, za su ba da
cikakken goyon baya ga ƙawarsu Nijar.
A wajen ECOWAS ma, akwai matsanciyar adawa da tsoma
bakin sojan. Shugaban ƙasar Aljeriya, Abdelmadjid Tebboune, ya bayyana a
fili cewa duk wani yunƙurin soja da ECOWAS za ta yi a Nijar tamkar barazana
ce kai-tsaye ga ƙasar Aljeriya. Ma’aikatar
harkokin wajen Rasha ma ta fitar da sanarwa tana adawa da wannan yunƙurin tsoma
bakin (BBC News, 2023). A ƙarƙashin matsin lamba daga ciki da waje, shirin tsoma
bakin sojan ECOWAS ya gagara a hankali. Gwamnatin sojan Nijar ta sanar da
tsarin mulki na wucin-gadi na shekaru uku, inda aka ce za a miƙa mulki bayan
shekaru uku, da kuma gwamnatin soja ta fara gudanar da ayyukanta don daidaita
halin cikin gida. Wannan ya nuna cewa shirin tsoma bakin ECOWAS ya ci tura gaba-ɗaya. Wannan ba wai kawai ya fallasa raguwar ƙarfin
jagoranci na ECOWAS ba. Har ma ya bayyana sauyin tsarin siyasar ƙasa da ƙasa na
yammacin Afirka sakamakon tasirin sabbin haɗin guiwar ƙasashen Sahel. Babu shakka, wannan ya kawo ƙalubale a kan
makomar tsaron yammacin Afirka.
Dalilin
Gazawar Shiga Tsakanin ECOWAS
A yayin da ECOWAS take ƙoƙarin shiga
tsakanin a juyin mulkin da ya faru a Nijar, duk da cewa ta yi yunƙurin amfani da
hanyoyi daban-daban, ba su haifar cda sakamako mai kyau ba. Wannan ɓangare ya fito da yadda wasu batutuwan cikin ƙungiyar suka
zama manyan dalilan da suka haifar da gazawa wajen shiga tsakanin kamar haka:
Canzawar Matsayar Manyan Ƙasashe
A matsayinta na ƙasa mai ƙarfi a yanki
kuma shugabar ƙungiyar ECOWAS a wannan lokaci, Nijeriya ya kamata
ta zama jagora kuma hedkwatar yanke shawara a cikin matakin shiga tsakani da
ECOWAS ta ɗauka a kan
juyin mulkin Nijar. Sai dai matsayar Nijeriya ta riƙa canzawa
lokaci zuwa lokaci. Wanda hakan ya haifar da sauyin matsayar ECOWAS gaba-ɗaya. Wannan yana nuna yadda matsalolin cikin gida
suke shafar manufofin diflomasiyyar yanki. Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bayan ya
hau mulki a ƙarshen watan Mayu na shekarar 2023, ya ƙaddamar da
manyan sauye-sauyen tattalin arziki. Manyan daga cikin waɗannan sauye-sauyen sun haɗa da cire tallafin man fetur wanda shekaru da dama
ake amfani da shi, da kuma daidaita tsarin darajar kuɗi da ya kasance da bambance-bambance. Waɗannan matakai biyu sun haifar da gagarumar illa ga
tattalin arzikin cikin gida, inda hauhawar farashin kayayyaki ta haura zuwa
28.92% a ƙarshen shekarar 2023. Wannan ya zama yanayi mafi
muni cikin tsawon shekaru 27 da suka gabata dangane da tashin farashi, wato har
farashin abinci ya tashi da kashi 33.93% (Nigeria National Bureau of
Statistics, 2024).
Wannan ya kawo babbar matsin lamba ga tattalin
arziki da kasafin kuɗi, kuma ƙarancin kuɗaɗe daga ƙasashen waje
ya sa Nijeriya cikin jinkiri wajen yanke shawarar tura sojoji don kwantar da
juyin mulkin Nijar. Wani muhimmin abu da yake hana Nijeriya ɗaukar matakin sanya cikakken takunkumi da ma tura
sojoji shi ne batun dangantakar al’ummar Hausa da suke tsakanin Nijeriya da
Nijar. Hausawa su ne al’umma mafi girma a Nijar, yawansu ya fi rabin yawan
jama’ar ƙasar. Haka kuma, Hausawa suna ɗaya daga cikin manyan ƙabilu uku a Nijeriya.
Cikin tsawon shekaru da dama, Nijeriya da Nijar sun gina tsarin kasuwanci da
hulɗa tsakanin
mutane bisa tushen ƙasar Hausa (Hausaland), wanda yake da matuƙar muhimmanci
ga tattalin arziki da zamantakewa. Binciken da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya
gudanar ya nuna cewa kusan kashi 75% daga cikin kayayyakin Nijeriya take
fitarwa ta hanyar kasuwancin da ba a hukumance ba suna shiga cikin Nijar ne (Africa
Defense Forum, 2023). Takunkumin da ECOWAS ta sanya wa Nijar ya haifar da tsaikon
kayayyaki da yawa a kan iyaka, inda ’yan kasuwa Hausawa da dama suka shiga
cikin halin kunci. Hakan ya haddasa rashin jin daɗi daga ɓangaren
Hausawa. Bayan sanarwar kashedin ECOWAS na tura sojoji ta fitar, a ranar 12 ga
Agusta, jama’a a Kano, birni mafi girma a Arewacin Nijeriya, sun fito kan titi
domin yin zanga-zanga, suna nuna adawa da takunkumi, tare da nema a kare
‘yan’uwansu Hausawa da suke a Nijar.
Bayan haka, gargaɗin da ya fito daga ƙasashe irin su
Rasha da Aljeriya da Mali, da kuma Burkina Faso ya haifar da tsoron cewa tura
sojoji zai haifar da yaƙe-yaƙe da rikice-rikicen siyasa da ba a son su faru. Har
ila yau, a lokacin da Shugaba Tinubu ya hau mulki, manyan sauye-sauyen tattalin
arziki da ya ƙaddamar, suna cikin matakin farko, kuma yawancin
matsalolin cikin gida ba su samu mafita ba. Duk da cewa ya yi kira ECOWAS ta ɗauki tsauraran matakan a kan gwamnatin soja ta
Nijar, amma saboda matsin lamba daga gida da ƙetare, sai ya
zaɓi yin sassauci
a kan matsalar Nijar. Sauye-sauyen matsayin Nijeriya ya yi tasiri a kan yadda
ECOWAS take yanke hukunci a matsayin ƙungiya, kuma a ƙarshe, ECOWAS ta yanke shawarar janye takunkumin da
aka sanya wa gwamnatin soja ta Nijar, a sakamakon shawarar shugaba Tinubu a
cikin taron.
Takunkumi ko Haɗin Guiwar Tattalin Arziki
Ɗaya daga cikin
manyan manufofin da ECOWAS ta kafa kanta da su tun asali shi ne ƙarfafa hanyar ’yancin
kasuwanci a tsakanin ƙasashe da kuma haɗin guiwar tattalin arziki, don samar da ingantaccen tsarin
kasuwaunci kayayyaki da jari da kuma tabbatar da ‘yan kasuwa da ma’aikata daga ƙasashe daban
za su iya tsallaka iyakar ƙasashe cikin sauƙi. Amma yayin
da juyin mulki ya faru a Nijar, matakan takunkumi na tattalin arziki da na kuɗi da ECOWAS ta ɗauka sun
haifar da babban tasiri a cikin gajeren lokaci ga wannan tsarin haɗin guiwar. Musamman ma ga ƙasashen da ba
su iyaka da teku na yankin Sahel, wato Burkina Faso da Mali da Nijar,
kasuwancinsu ya dogara matuƙa a kan haɗin kai da ƙasashen da
suke dab da teku.
Hakazalika, wannan takunkumi bai haifar da sakamako
mai kyau, haka ta sa ƙasashen uku suka yanke shawara don fice daga ECOWAS
da kuma fara neman hanyoyin fitar da kayayyaki zuwa Arewacin Afirka, damar haɗin guiwar tattalin arzikin ƙasashen
yammacin Afirka za ta ragu matuƙa. Har ila yau, idan waɗannan ƙasashe uku suka fice daga ECOWAS gaba-ɗaya, babu shakka ƙasashen
yammacin Afirka za su fuskanci ƙarin shingayen haraji da hauhawar farashin
kayayyaki. Wannan zai lalata tsarin haɗin guiwar
tattalin arziki da ECOWAS ta gina tsawon shekaru. Idan tsarin takunkumi ya ci
gaba da lalata tushen amincewa da juna tsakanin ƙasashe
mambobi, ECOWAS za ta fuskanci haɗarin
tarwatsewar tattalin arziki da kuma ƙalubalen halascinta (legitimacy crisis) a matsayin
wakilci na yankin.
Bayan haka, ƙasashen uku sun daɗe suna dogara ga Ƙungiyar
Tattalin Arziki da Kuɗi ta Yammacin
Afirka (UEMOA) wajen aiwatar da manufofin kuɗi da haɗin guiwar
tattalin arziki. Wannan ƙungiya na amfani da CFA Franc na Yammacin Afirka da
kuma tsarin da Babban Bankin Ƙasashen Yammacin Afirka (BCEAO) yake jagoranta domin
samun wani mataki na haɗin kai a
fannin tattalin arziki. Duk da cewa Ƙungiyar Ƙasashen Sahel da ƙasashen uku
suka kafa ta sanar da ficewarta daga ECOWAS, ba ta fice kai-tsaye daga UEMOA
ba. Sai dai kuma, shugaban gwamnatin sojan Nijar, Abdourahamane Tchiani, ya
ambaci yiwuwar ƙasashen ukun ƙaddamar da sabon kuɗi na bai ɗaya a cikin
wani jawabi a talabijin, inda ya bayyana cewa: “Kuɗi shi ne mataki na farko wajen kawar da gado daga
mulkin mallaka” (Thioune, 2024). Wannan ya kawo ƙalubale kai-tsaye
ga tsarin gudanar da harkokin kuɗi da ECOWAS
take yi a halin yanzu.
Domin kauce wa tsanantar matsaloli a yankin da kuma kare tsarin
kasuwanci da yake kasancewa a yanzu, ECOWAS ta fara aiwatar da matakan sarrafa
rikici. Bayan ƙasashen uku sun sanar da ficewarsu daga ECOWAS,
ECOWAS ta gudanar da taron ƙoli na musamman a Abuja a watan Fabrairu 2024, inda
ta sanar da cewa za ta janye wasu takunkumin tattalin arziki da aka sanya wa waɗannan ƙasashe. A ƙarshen shekara, ECOWAS ta sake bayyana cewa za ta ba
su lokacin watanni shida don sake yin tunani a kan ko za su fice daga ƙungiyar gaba-ɗaya ko a’a. Waɗannan matakan
sun nuna cewa, a matsayin ƙungiyar haɗin guiwar
tattalin arziki na yanki, yanzu ECOWAS tana karkata hankalinta daga tilasta
mambobinta don riƙe ƙa’idojinta zuwa ainihin yanayi don tabbatar da ci
gaban haɗin guiwar
tattalin arziki a yammacin Afirka.
Sauye-sauyen Ruɗanin Siyasa
Ƙasashen Nijar
da Mali da Burkina Faso sun kafa tsarin mulki na Ƙungiyar Ƙasashen Sahel
ta hanyar juyin mulkin soja. Wanda yake sake tsara yanayin ruɗanin siyasa da tsaro a yammacin Afirka. A cikin ƙungiyar, ta
hanyar rattaba hannu a kan yarjejeniyar kare juna da tsarin haɗin guiwar tattalin arziki. Sun mai da tsaron
mambobinta fiye da kome, inda suka kafa wani sabon tsarin siyasar tattalin
arziki mai ƙarfi da ya kawo cikas ga cigaban ECOWAS. Ban da haka
kuma, ƙasashen ukun sun fara faɗaɗa ƙawance da ƙasashe da
dama, inda suke amfani da saɓanin da suke
da shi da tsofoffin ƙasashen mulkin mallaka (musamman Faransa). Domin
tabbatar ’yantar da kai daga mulkin mallaka. A sakamakon haka, sun samu taimako
daga Rasha domin haɗin guiwa a
fannonin horar da sojoji da samar da kayayyakin aikin sojoji, da haɓaka haƙa ma’adinai na Uranium. Haka kuma, suna neman buɗe hanyar kasuwanci daga Algeria zuwa Arewacin Afirka
da Tekun Bahar Rum, domin kawar da dogaro da ƙasashen
ECOWAS. Abin da yake da muhimmanci sosai shi ne, ƙasashen ukun
sun fitar da wani sabon fasfot wanda ba yake ɗauke da tambarin ECOWAS, matakin da yake nuna
rarrabuwar kai tsakanin tsarin shugabanci na yanki da matsalolin ruɗanin siyasa na yanzu da ECOWAS take fuskantarwaa
wannan yanayi.
Kodayake ƙungiyar ƙasashen uku ba su kai ECOWAS ƙarfin soja ba
tukuna, amma ta hanyar haɗin kai da
samun tallafin kuɗi da
shawarwari daga ƙetare, sun sami cigaba sosai wajen gina ƙarfin sojoji.
A gefe guda, tun bayan da ECOWAS ta shiga tsakanin juyin mulki na Gambiya a
2017, akwai matsalar rashin gogewa a fagen fama da ƙarancin kuɗin ga ƙasashe mambobin da kuma yunƙurin shiga
tsakani ta hanyar tura sojoji na ECOWAS yana fuskantar cikas. Waɗannan suna daga cikin manyan dalilan da suka tilasta
wa ECOWAS sassauta matsayinta a kan batun Nijar.
Sakamakon Bincike
A sakamakon wannan bincike an fahimci yanayin
matsalolin siyasa na cikin gida na ECOWAS, dogaro da juna a fannin tattalin
arziki da dangantakar da take tsakanin al’umommin ƙasashe. Haka
kuma, da rashin daidaiton matsayar ƙasashe masu ƙarfi kamar Nijeriya da matsaloli cikin gida,
dukkansu sun sa an canja matsaya daga shiga tsakani zuwa sassautawa. Wannan
sakamako ya nuna gazawar ƙungiyar yankin wajen daidaita harkoki tsakanin ɓangarori daban-daban.
Haka kuma, ECOWAS ta fitar da “Burin 2050” (ECOWAS
Vision 2050) a shekarar 2021, wanda manufar wannan shi ne gina ECOWAS da za ta
kasance ƙungiya wadda za ta samar da dunƙulewar ƙungiyar ƙasashen
yammacin Afirka ta bai ɗaya mai haɗin kai. Wanda za ta samar da zaman lafiya da wadatar
tattalin arziki da ingantacciyar rayuwa, da ingantaccen tsarin shugabanci da
girmama ’yancin ɗan’adam tare
da ƙarfafa ci gaba mai ɗorewa. Tsarin ya yi shirin zai faɗaɗa haɗin kai a fannoni da dama kamar kasuwanci da tsarin
kuɗi da tsaro
(Hou, 2023). Don cim ma wannan buri, ECOWAS ya kamata ta yi amfani da wannan
dama wajen zurfafa gyare-gyaren cikin gida, ƙarfafa haɗin kai tsakanin ƙasashe
mambobi, da haɓaka ƙwarewar shiga
tsakanin rikici cikin gaggawa. Ta hakan ne za a samar da wani ingantaccen
tsarin tsaron yanki da zai kasance mai ƙarfi da daidaito, wanda zai wanzar da zaman lafiya
da wadata ga dukkan ƙasashen yankin a nan gaba.
Kammalawa
A wannan takarda an yi tsokaci a kan dalilin da suka
sa ECOWAS ta canja matakanta na shiga tsakani zuwa sassautawa, ta hanyar
nazarin ci gaban juyin mulki a Jamhuriyar Nijar da matakan shiga tsakanin na ƙungiyar
ECOWAS. Tsarin shiga tsakani na ECOWAS ya haɗa da tattaunawar siyasa da saka takunkumin da amfani
da ƙarfin soja, da kuma yanayin tarihi taka muhimmiyar
rawa wajen samar da tsaro a yankin. Halin yanzu inda yawan juyin mulki a
yammacin Afirka yake ƙaruwa sosai da saɓanin ra’ayoyin shiga tsakani a cikin mambobin ƙasashe ya nuna
tasirin tsoma baki daga ƙasashen waje ya ɓullo sosai, sakamakon matakan shiga tsakani na
ECOWAS.
Manazarta
Africa Defense
Forum. (2023, September 26). Hausa Connection Could Be Key to Diplomacy With
Niger. https://adf-magazine.com/2023/09/hausa-connection-could-be-key-to-diplomacy-with-niger/
Alake, D.
(2023, July 30). ECOWAS Imposes Sanctions on Niger Junta, Calls for Immediate
Release, Reinstatement of President Bazoum. Nigeria State House.
https://statehouse.gov.ng/news/ecowas-imposes-sanctions-on-niger-junta-calls-for-immediate-release-reinstatement-of-president-bazoum/
Bai, B. (2023,
August 15). Niger coup makes West worry about "domino effect" [Nijar
juyin mulki ya sa Yamma damuwa game da 'Domino Effect']. Beijing Daily, 004.
BBC News.
(2023, August 11). Niger Coup: Russia Warns ECOWAS Not to Take Military Action.
https://www.bbc.com/news/world-africa-66478430
China Military
Online. (2022, January 11). ECOWAS announces new sanctions on Mali [ECOWAS ta
sanar da sabbin takunkumi kan Mali]. http://www.81.cn/jfjbmap/content/2022-01/11/content_307075.htm
ECOWAS
Commission. (n.d.). Fundamental Principles. https://www.ecowas.int/fundamental-principles-2/
ECOWAS
Commission. (2023, July 26). ECOWAS Commission condemns the attempted coup
d’Etat in Niger. https://amaniafrica-et.org/wp-content/uploads/2023/08/ECOWAS-Commission-condemns-the-attempted-coup-dEtat-in-Niger-July-26-2023.pdf
ECOWAS.
(1999). Protocol relating to the mechanism for conflict prevention, management,
resolution, peace-keeping and security.
Hou, Q.
(2023). ECOWAS 'Vision 2050': Background, Measures and Challenges [ECOWAS
'Burin 2050': Tarihi, Matakai da Ƙalubale]. China Investment, (Z3), 104-107.
Huang, R.
(2021). Research on Conflict Management of ECOWAS [Bincike kan Gudanar da
Rikici na ECOWAS] [Master's thesis, China Foreign Affairs University].
DOI:10.27373/d.cnki.gwjxc.2021.000157
Jiang, X.
(2023, August 4). ECOWAS discusses military intervention in Niger [ECOWAS tana
tattauna shiga tsakani na soja a Nijar]. Global Times, 002.
Lamin, A.
(2006). West Africa’s Evolving Security Architecture: Looking Back to the
Future. Center for Conflict Resolution.
Le Monde.
(2023, August 7). Niger Coup: From North to West Africa, Voices Speak Out
against ECOWAS Military Operation. https://www.lemonde.fr/en/le-monde-africa/article/2023/08/07/niger-coup-from-north-to-west-africa-voices-speak-out-against-ecowas-military-operation_6083415_124.html
Li, H., &
Li, D. (2019). ECOWAS response to internal political turmoil in its member
states since the 21st century [Martanin ECOWAS game da rikice-rikicen siyasa na
cikin gida]. Journal of Francophone Studies, (02), 30-38.
Liu, H., &
Deng, W. (2014). ECOWAS armed intervention in West African conflicts:
Background, process and trends [Tsoma bakin soja na ECOWAS a rikice-rikicen
Yammacin Afirka]. Asia & Africa Review, (2), 1-12.
Nigeria
National Bureau of Statistics. (2024). CPI and Inflation Report.
Obasi, N.
(2023). ECOWAS, Nigeria and the Niger Coup Sanctions: Time to Recalibrate.
Crisis Group. https://www.crisisgroup.org/sites/default/files/2023-12/ecowas-05xii23_0.pdf
Okafor, O.
(2023, August 20). Battle-ready Niger Coup Leader Promises to Handover within
Three Years. BusinessDay. https://businessday.ng/news/article/battle-ready-niger-coup-leader-promises-to-handover-within-three-years/
Oluropo, F. J., et al. (2024). The Resurgence of
Military Coups in West-Africa States: The Case of Niger Republic and Its
Implications on Peace, Security and Transnational Activities in Nigeria. Global
Journal of Humanities and Social Sciences, 3(4), 26-37.
Premium Times.
(2023, August 7). ECOWAS Delegation: How Abdulsalami, Sultan Were Humiliated by
Niger Junta. https://www.premiumtimesng.com/news/headlines/614794-ecowas-delegation-how-abdulsalami-sultan-were-humiliated-by-niger-junta.html
Sowale, A. O.
(2024). The Military Coup in Niger Republic: Anti-democracy or Pro-autocracy,
and Ominous Conflict Trend Implications for Nigeria in West Africa. Africa
Review. https://doi.org/10.1163/09744061-bja10172
Sun, H.
(2023). Niger coup triggers fierce game among parties [Nijar juyin mulki ya
haifar da wasan ɓangarori].
World Knowledge, (17), 45-47.
Thioune, T.
(2024, March 14). Burkina Faso, Mali and Niger Hint at a New West African
Currency: What It’ll Take for It to Succeed. The Conversation. https://theconversation.com/burkina-faso-mali-and-niger-hint-at-a-new-west-african-currency-what-itll-take-for-it-to-succeed-225517
United
Nations. (2017, January 21). Note to Correspondents - Joint Declaration on the
Political Situation in The Gambia. https://www.un.org/sg/en/content/sg/note-correspondents/2017-01-21/note-correspondents-joint-declaration-the-political-situation-the-gambia
Yabi, G. (2023). The Niger Coup’s
Outsized Global Impact. Carnegie Endowment for International Peace. https://carnegieendowment.org/posts/2023/08/the-niger-coups-outsized-global-impact?lang=en
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.