Mujaheed, Abdullahi (2025). “Samuwa da Bunƙasar Rubutattun Gajerun Labaran Hausa” Himmaa: Journal of Contemporary Hausa Studies, Vol. 10, No. 1 August, 2025. Department of Nigerian Languages Umaru Musa Yar’adua University, Katsina. Pg 63-77, ISSN: 2276-6685
SAMUWA DA BUNƘASAR RUBUTATTUN GAJERUN LABARAN HAUSA
Daga
Abdullahi, Mujaheed
Sashen Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harsuna,
Jami’ar Jihar Kaduna.
mujaheedabdullahi@gmail.com
08069299109
Tsakure
Rubutattun gajerun
labaran Hausa sun ratso mabambantan zanguna cikin tarihi. Sun samu tun daga
lokacin da harkar ɗab’i ta kasance a hannun hukumomin inganta adabi har zuwa yanzu inda ɗaiɗaikun marubuta da ƙungiyoyi da kuma
hukumomi suka ci gaba da samar da gajerun labaran Hausa. Haka kuma, duk da cewa
an gudanar da nazarce-nazarce da yawa a kan rubutaccen labarin Hausa bisa
manufofi daban-daban, amma har yanzu ba a sami wani nazari mai zurfi da ya
daddale ginuwa da bunƙasar gajerun labaran Hausa ba. Wannan dalilin ne ya haifar da gudanar da
wannan bincike domin fayyace yadda rubutattun gajerun labaran Hausa suka samu
kuma suka bunƙasa, tare da fito da batutuwan da suka gina su cikin zanguna mabambanta.
Hanyoyin da aka bi wajen gudanar da binciken sun haɗa da tattaro matanin rubutattun gajerun labarai da karance-karance daga rubutattun
bayanai da kuma tattaunawa da masana adabin Hausa da marubutan zuben Hausa. An
yi amfani da fasahar zamani wajen tattaro wasu bayanai musamman a kafar
intanet. Haka kuma, an yi amfani da Ra’in Gajerun Labarai (Short Story Theory) na Edgar Allen Poe
(1804-1849) wajen bin diddigin
tarihi da ginuwar rubutattun gajerun labaran Hausa. Binciken ya gano ire-iren
siffofin rubutattun gajerun labaran Hausa da kuma fasalta batutuwan da suka
gina su da bunƙasa su, tare da bayyana matsayinsu a rubutaccen zuben Hausa cikin zanguna
uku mabambanta daga 1929 zuwa 2023.
Fitilun Kalmomi: Samuwa, Bunƙasa, Labari, Gajeren Labari.
1.0
Shimfiɗa
Labari wani
zance ne da yake aukuwa tsakanin mutane ko tsakanin mutum da mutum ko wanda ya
wuce tsayawa a gaisa kurum. Kusan duk wani abu da ya danganci samar da wani abu
game da wani lamari mai tsawo ko gajere ana iya kiran shi labari
(Sabe, 2011:42). Saboda haka, labari zai iya kasancewa bayani ne tsararre mai ma’ana wanda
yake da farko da kuma ƙarshe, kuma zai iya cusa tarbiyya ko a koyi wani darasi daga cikinsa (Sabe,
2011: Shf.42).
Su labarai, musamman na adabi, sukan kasance ko dai dogaye ne da za a ɗauki lokaci mai tsawo wajen bayar da su, ko kuma wajen karanta su idan
rubutattu ne, ko kuma gajeru ne waɗanda za a iya labarta su a magance
ko a karance cikin ƙanƙanin lokaci. Dogayen labarai da gajerun labarai dukkansu nau’o’i ne na ƙagaggun labaran Hausa,
sai dai sun sha bamban ta wasu fuskoki ko siffofi da dama.
Yawanci akan tsara rubutattun gajerun labarai ne a kan wani batu ɗaya tilo mai ƙunshe da manufa ɗaya tare da taƙaitattun taurari cikin taƙaitaccen lokaci a wani ayyanannen
wuri. Irin wannan fasaha ta rubutun gajerun labarai tana da dogon tarihi a ƙasar Hausa kuma labaran
suna ci gaba da ginuwa da bunƙasa, sai dai manazarta ba su mayar da hankali sosai ga
bin diddigin wannan fasali ba. Babbar manufar wannan bincike ita ce bin
diddigin gajerun labarai tare da fito da batutuwan da suka bunƙasa rubutattun gajerun
labaran Hausa.
Saboda haka, wannan takarda ta ƙunshi bayani kan rubutattun gajerun labaran Hausa tun
daga samuwarsu zuwa yadda suka bunƙasa da matsayin da suke ciki a wannan zamani. An kawo
bayani kan ma’anar gajerun labarai da abubuwan da suka ƙunsa, sai kuma yadda suka ginu tare
da bunƙasa cikin zanguna mabambanta tun daga shekarar 1929 zuwa 2023. An bayyana
gudummawar hukumomi da marubuta a ɗaiɗaikunsu da ƙungiyoyinsu, sai kuma aka dubi yadda gasa ta taimaka wajen bunƙasar rubutun gajerun
labaran Hausa.
2.0
Ra’in Bincike
Ra’in da aka ɗora kan wannan bincike shi ne Ra’in Gajerun Labarai (Short Story Theory), wanda Edgar Allen Poe (1804-1849) ya ɗabbaƙa a aikinsa mai suna Review of Hautherns Twice-Told Tales
(1842), da kuma wasu ayyukansa guda biyu wato “The
Philosophy of Composition” (1846) da “The Poetic Principle” (1850). Waɗanda suka biyo bayan Edgar Allen Poe a wannan fasali sun haɗa da Nathaniel Hawthorne (1974) da Brander Mathews (1974) da Joseph Berg
Esenwein (1909) da Serwood Anderson(1974). Daga cikin manufofin wannan ra’i akwai bayyana siffofi da
sigogin gajeren labari tare da bambance shi da dogon labari. Haka kuma yana fayyace gajerun labarai a
matsayin nau’in adabi mai zaman kansa da kuma fito da batutuwan da suka gina gajerun labarai daga rayuwar gaskiya zuwa ƙirƙirarrun batutuwa ko abin da ke cikin
zuciyar marubucin ko kuma gamaɗen waɗannan batutuwa. Wata manufar ra’in kuma ita ce bayyana fasalce-fasalcen gajerun labarai dangane da yawan kalmomi da zubi da
tsarinsu da kuma adadin taurarinsu. Sai kuma siffanta yadda
gajerun labarai suke ɗarsuwa
da sanya shauƙi a zukatan masu karatu, cikin taƙaitawa da daidaituwa da kuma kula da yanayin jituwa tsakanin saƙo da taurari da wuri a ginin gajerun
labarai (Besseler, 2011). Saboda haka, wannan ra’in yana duba batutuwan da suka shafi fasalin ayyukan adabi na gajerun
labarai, kuma wannan bincike ya ƙudurci bayyana ginuwa da bunƙasar rubutattun gajerun ƙagaggun labaran Hausa ne. Don haka, wannan bincike yana da dangantaka da wannan
ra’in, kuma ra’in zai iya zama mizani ga wannan aikin.
3.0
Gajeren Labari Bisa Faifai
Gajeren labari kamar yadda Natahniel Hawthrone ya ruwaito cikin aikinsa mai
suna Natahniel Hawthrone Tale (1974),
cewa, Edgar Allen Poe ya ce gajeren labari yana nufin:
“Gajeren labarin zube ne wanda yake buƙatar rabin sa’a zuwa sa’a ɗaya ko biyu wajen karantawa, wanda aka gina domin isar da wani saƙo ɗaya tal wanda aka tsara a taƙaice” (Fassarar mai bincike).
Ke nan, gajeren labari kamar yadda Ridout da Stuart (1968: shf. xix) suka
jaddada:
“Daidaitaccen aikin zube ne wanda yawanci bai wuce kalmomi dubu goma ba
kuma yake ƙunshe da batutuwan ƙirƙira da aka zubo su a tare da wani tauraro da yake fuskantar wani ƙalubale wanda dole sai
ya tunkara. (Fassarar mai bincike).
Shi ya sa wannan nau’i zai iya kasancewa daga gajeren labari mai kalmomi
dubu biyar zuwa matsakaicin labari mai kalmomi dubu goma. Ƙagaggen labari ne wanda yake ƙunshe da wani batu ɗaya tal da ya mamaye labarin a kan babban tauraro ɗaya. Kuma yana ƙunshe da zubi wanda yake a matse kuma a tsare domin samar da sakamako guda ɗaya” (Ihakaram, 1990: shf. 274). Sai dai, a fahimtar wannan bincike, adadin
kalmomin kowane gajeren labari yana farawa ne daga kalmomi dubu ɗaya (1,000) zuwa dubu bakwai da ɗari biyar (7,500).
Har ila yau, ana iya samun wasu gajerun labarai cikin mafi ƙarancin kalmomi kamar
haka:
-
Ƙagaggen labarin da bai kai kalmomi ɗari biyar (500) ba, wato Micro-Fiction.
Wannan shi ne mafi gajarta.
-
Ƙagaggen labarin da bai wuce kalmomi ɗari biyar (500) zuwa dubu ɗaya (1,000) ba, ana kiran sa Walƙiyar Labari, wato Flash Fiction.
-
Ɗan gajeren rubutu mai ƙunshe da wani bayani kan
wani batu guda ɗaya (cikin falle ɗaya) mai ƙunshe da shafuka huɗu ƙanana, wato Phamplets (Goring,
et-al, 2001:378; Di
Yanni, 2002:41-4; Smith, 2001:313-322).
Yawanci akan gina gajerun labarai ne a kan wani batu guda ɗaya, a wani ayyanannen lokaci. Suna da zubi da tsari sassauƙa, wanda ke ƙunshe da taƙaitattun taurari. Wani lokacin ma tauraro guda ɗaya ne a labarin, saboda gajartar labarin. A ire-iren waɗannan labaran, ana warware ƙulli cikin sauri. A wasu lokutan kuma akan ƙare shi a buɗe, a bar mai karatu da yanke hukunci. Ana iya karanta gajeren labari a zama
ɗaya kuma ya shiga ran mai karatu ya yi tasiri a zuciyarsa. Gajerun labarai,
kamar sauran nau’o’in adabi, suna tafiya ne ko wanzuwa daidai da sassauyawar rayuwar al’umma. Bugu
da ƙari, rubutattun gajerun labarai sun samu ne bayan samuwar rubutu da karatu
a cikin al’ummar da aka same su, wato waɗanda aka wallafa su
cikin littafi ko intanet da sauran hanyoyin rubutu da karatu na zamani.
Fasahar samar da gajeren labari a matsayin nau’in adabi,
ba sabon abu ba ne. Haka kuma, gano ainahin asalin gajeren labari na baka yana
da wahala, sai dai wanda ya fara ƙirƙiro rubutun da za a iya gani a siffar gajeren labari (na
adabi) shi ne Nicola Vasilievitch GoGol wanda aka haife shi a Sorochintsky ta ƙasar Rasha a shekarar
1809, daidai da shekarar da aka haifi Edgar Allen Poe a Baltimore. Daga waɗannan mutane ne za a iya ɓuɓɓugo farkon samuwar gajerun labarai na zamani, wato rubutattu (Bates
1972:Sh.6 cikin Abdo El-Rahman, 1996: Sh.7). Wani abin la’akari, shi ne kusan
kowace al’umma da take da fasahar rubutun gajerun labarai a duniya ta fara ne
daga labarun gargajiya na baka zuwa rubutattu na zamani. Akwai ire-iren waɗannan misalai a adabin al’ummomin Larabawa da Turawa da
Indiyawa da kuma wasu al’ummomin nahiyar Afirka (Malumfashi,
2009: Sh. 28; Sabe, 2016: Sh. 71-72).
3.1 Samuwa da
Bunƙasar Rubutattun Gajerun Labaran Hausa
Duk da yake Turawa sun shigo ƙasar Hausa, sun samu Bahaushe da adabinsa na baka da kuma
hanyar rubutu da karatu ta amfani da ajami. An yi amfani da shi wajen taskace
sassan adabin baka na zube irin su labaran gargajiya da tatsuniyoyi da sauransu.
Saboda haka, zuwan Turawan ma ya ƙarfafa wannan fasali, domin kuwa tun shigowar Turawa ‘yan leƙen asiri, irin su J.F
Schon. Duk da cewa bai taɓa takowa ƙasar Hausa ba, amma ya samar da
littafin Magana Hausa daga abubuwan
da ya tsinta daga mutanen da ya yi hulɗa da su. Littafin ya ƙunshi gajerun labaran
baka na tatsuniyoyi da labarai da sauransu. Asalin littafin shi ne Farawa Littafin Magana Hausa wanda aka
samar a shekarar 1856, aka faɗaɗa zuwa Magana Hausa a shekarar
1862 (Bunza, 2015:Shf. 39).
Har ila yau, J.F Schon ya watsar da aikin Farawa Littafin Magana Hausa a shekarar 1847, sai bayan ya samu
labarai daga bakin Dorugu ya haɗa da wasu labarai biyu(2) da ya samu
daga Reberen J.C John guda goma sha takwas (18). Sai kuma Mista G.A Krause da ya
ƙara masa labarai guda takwas (8). Waɗannan tatsuniyoyi da
labarai da tarihe-tarihen rayuwa da karin magana da waƙoƙi, su ne Schon ya harhaɗa ya samar da littafin Magana Hausa a
shekarar (1885). Daga cikinsu ne kuma J.F Schon ɗin ya samar da African Proverbs,
Tales and Historical Fragments, (Bunza, 2015: Shf. 54).
Ke nan, wannan littafi na Magana
Hausa shi ne za a iya cewa ya share fagen taskace gajerun labaran Hausa na
gargajiya cikin rubutun boko. Wato, shi ya fara haska fitila ta rubutun gajerun
labaran Hausa. Haka kuma, irin wannan fasalin Turawa suka ci gaba da bi wajen tattara labarai da tatsuniyoyi da karin
maganganu da sauran maganganun azanci da al’adun Hausawa wuri guda a takarda
cikin rubutun boko, tun kafin a kafa mulkin mallaka a ƙasar
Hausa. A irin wannan fasali ne aka samu littattafai irin su Specimen of Hausa Literature na C.H Robinson (1896) da Hausa
Stories and Riddles na H.C Harris (1908) da Littafi na Tatsuniyoyi na Frank
Edgar (1924) da Hausa Saying and
Folklore na Flectcher, R.S (1912) da sauransu. Wani littafin gajerun labarai da ya
shahara a ƙasar Hausa shi ne Dare Dubu Da Ɗaya wanda yake fassara ne daga littafin Alfu Laila wanda Frank Edgar ya fara
wallafa littafi na 1 da na 2 a shekarar 1924. Akwai kuma wani Malam Mamman Kano
da ya fassara littafi na 3 da na 4 da na 5, duk daga Larabci zuwa Hausa. Daga
bisani an tattaro sauran fassarar labaran baki ɗayansa daga wasu sassan ƙasar Hausa, aka adana su wuri guda. Sai dai har yau ba a kammala buga su
cikin littafi ba (Malumfashi da wasu, 2015: Shf. xii).
Har ila yau, cikin ƙungiyoyin
Mishan masu yaɗa addinin Kiristanci a
ƙasar Hausa, waɗanda suka shahara irin su Church Missionary Society (C.M.S) da
kuma musamman Sudan Interior Mission
(S.I.M), akwai wadda ta fitar da littafin ƙagaggen
adabin Hausa na farko mai suna Littafi na
Karatun Hausa a shekarar 1922. Littafi ne da aka samar ta hanyar harhaɗa gajerun labaran baka na Hausa, irin su
almara da hikaya da tatsuniya da sauransu (Bunza, 2015: Shf. 46). Saboda haka,
wannan Littafi na Karatun Hausa ya yi
wa waɗancan na ‘yan leƙen asiri ladanci wajen
samuwar gajerun labaran Hausa a rubuce.
Wannan ya sake nuna cewa fitillar da ta
fara haska rubutun labaran Hausa daga nau’in tattara ko taskace gajerun labarai
ne. Domin kuwa, ko da Turawa suka kafa mulkin mallaka daga wannan fasali suka ɗora wajen samarwa da bunƙasa rubutaccen adabin Hausa a ƙarƙashin hukumomin inganta adabi (Yahaya, 1998; Sabe 2011; Malumfashi, 2009 da
Bunza 2015).
Ke nan, kamar yadda aka yi bayani bayan
Turawan mulkin mallaka sun samu gindin zama a ƙasar
Hausa, kuma an tabbatar da cewa ƙishirwar abubuwan
karantawa a ire-iren makarantun boko da Turawan suka buɗe ne ya haifar da yunƙurin samar da littattafai (ciki har da na adabi). An yi haka ne ta hanyar
kafa hukumomin inganta adabi, irin su Hukumar Fassara (1929) da Hukumar Talifi
(1936) da sauransu. Sai dai tun kafin kafa waɗannan hukumomin, gasar
da Hukumar Ƙasa da Ƙasa ta Nazarin
Harsuna da Al’adun Afirka ta shirya, domin rubuta labarai cikin harsunan Afrika a shekarar 1929, ta
taimaka wajen iza wutar dafuwar rubutun gajerun labaran Hausa.
Saboda haka, bayan samuwar rubutattun
gajerun labaran Hausa, lamarin ya ɗauki fasalce-fasalcen bunƙasa daga maɓuɓɓugarsu, wato ƙoƙarin
hukumomi da ɗaiɗaikun marubuta da ƙungiyoyi da kuma ta hanyar sanya gasannin samar da gajerun labarai. Bayanin
waɗannan
fasalce-fasalce yana biye cikin zanguna mabambanta, tun daga shekarar 1929 zuwa 2023.
3.1.1 Zango na Farko: Gajerun
Labaran Hausa Daga Hukumomi (1929-1970)
Hukumomi su ne tsittsigen da rubutun gajerun labaran Hausa ya tusgo daga
gare su. Domin kuwa, tun daga shekarar 1929, Hukumar Ƙasa da Ƙasa ta Nazarin Harsuna da Al’adun Afirka wadda take da
ofishinta a Ingila, ta yanke wa rubutun gajerun labarai
cibi. Wato, hukumar ta gudanar da gasa
domin samar da littattafan zube daga harsunan Afirka ciki har da Hausa. A
wannan gasa, an samu labaran Hausa waɗanda suka sha yabo, wato Hausa Stories guda biyu na H.B.G Nuhu da na Malam Dodo, sai Zaman Dara na Malam Ahemed Mettedden da Littafin
Karatu Na Hausa na Malam Bello Kagara da Takobin Gaskiya na
Malam Nagwamatse sai kuma Labaran Hausa
na Ɗan Malam Alƙali
Sokoto (Ɗan’Amarya,
2012: Shf. 78).
Duk da yake ba a samu labaran a hannun ba, amma dai marubutansu sun
samar da su ne ta hanyar harhaɗa labarai da tatsuniyoyin Hausa, in ban da labarin Takobin Gaskiya wanda marubucin ya gina shi a kan artabun sarakunan
ƙasar Hausa da
Turawa a zamanin kafa mulkin mallaka. Shi ya sa, ko daga jin sunan wasu daga
cikin waɗannan labarai, an
gane cewa kundaye ne na gajerun labarai. Misali, Hausa Stories da Labaran
Hausa, da sauransu. Hakan ya tabbata ne idan aka yi la’akari da littafin Hausa Stories na Malam Dodo wanda ya
rubuta shi ta hanyar harhaɗa tatsuniyoyin Hausawa. Hakan ta sanya littafin ya yi armashi wajen samar
da nishaɗi ga al’umma da
kuma samun abin karantawa ga ɗalibai.
A nan ƙasar
Hausa kuwa, hukumar farko ta inganta adabi wadda Turawan
mulkin mallaka suka kafa ita ce Hukumar
Fassara a shekarar 1929. Kuma ita ce ta kasance unguwarzoma wadda ta yanke cibin samar da littattafai na ƙagaggun labarai na Hausa, ciki kuwa har da
gajerun labarai. Daga cikin ƙoƙarin
da wannan hukuma ta yi wajen samuwar gajerun labarai, akwai yin gyare-gyare ga
littafin Labaru Na Da Da Na Yanzu a shekarar 1931, inda an fassaro sassan tarihin ƙasar Hausa da suke rubuce cikin harshen Larabci, aka zuba su a cikin wannan
littafin. Babi na huɗu na wannan littafi wanda aka yi masa take
da “Hikayoyi da Labaru” cike yake da gajerun labarai guda sittin da biyar (65)
waɗanda
aka samar daga tatsuniyoyi da hikayoyi da labaran gargajiya waɗanda suka shahara a ƙasar Hausa a wancan lokacin. A nan ma, an samu wani fasali na taskace
labarun baka cikin takarda.
Har ila yau, Hukumar Fassara ce ta samar da littafin Magana Jari Ce I-III a shekarar 1937, amma
dai sai a 1939 Hukumar Talifi ta fitar da littafin ya shiga kasuwa. Littafin
wanda Abubakar Imam ya rubuta, ya ƙunshi gajerun labarai
ne guda tamanin da ɗaya (81) masu tushe ɗaya daga uwar labari ɗaya, waɗanda aka fassaro wasu
labaran daga wasu harsunan, aka ayyana wasu, aka kuma baddala wasu daga adabin
baka (Malumfashi, 2019: Sh. 323-324).
Bayan Hukumar Talifi ta lura da littattafan
Magana Jari ce I-III sun yi wa yara
‘yan aji 1 zuwa 2 na Elementare wuyar fahimta, sai aka sake sanya Abubakar Imam
ya rubuta littafin Ƙaramin Sani Ƙuƙumi Ne a shekarar 1938, tare da taimakon Dakta
R.M East.
Kodayake, tun kafin 1938, samar da
rubutattun gajerun labaran Hausa cikin littattafai ya ci gaba ne a shekarun
1937 zuwa 1941, lokacin da Hukumar Talifi ta yi yarjejeniyar buga littattafan
adabin Hausa da ƙungiyoyin Mishan domin amfanin ɗalibansu. Hakan ya
bayar da damar samar da wasu littattafan gajerun labarai guda uku a shekarar
1938, waɗanda
aka ƙago daga labarai daban-daban da suka jiɓinci adabin baka cikin
salon koya karatun Hausa a littafin farko na jerin domin ya share fagen sauƙaƙa karatun sauran littattafai biyun (Bunza,
2015: Shf. 56-57; Jibril, 2019: Shf. 40-41). Waɗannan littattafai su
ne, Ka Koyi Karatu (1938) da Ka Ƙara Karatu (1938) da Ka Yi Ta Karatu (1941).
Har ila yau, littafin Ƙaramin Sani Ƙuƙumi 1 &2, (1944) yana cikin littattafan
gajerun labarai da hukumomi suka samar, Hukumar Talifi ce ta samar da shi don
karantawa a makarantu, musamman la’akari da cewa labaran cikin Magana Jari Ce da aka samar kafin shi,
sun yi wa yara ‘yan aji 1 zuwa 2 na elemantare tsauri. Littafin yana ƙunshe
da gajerun labarai masu sauƙin fahimta ga yara ‘yan makaranta (Ahmad, cikin Malumfashi, 2019: Sh.296).
Ita ma hukumar NNPC ta bayar da gudummawa wajen sake buga wasu littattafai
na gajerun labarai inda a shekarar 1968 ta sake buga littafin Labaru Na Da Da Na Yanzu wanda ya ƙunshi wasu labaru na
gargajiya da aka taskace cikin littafin. Sai kuma a shekarar 1970, kamfanin
buga littattafai na NNPC ɗin dai ya sake fitar da littafin Dare
Dubu Da Ɗaya, 1-5.
Ke nan, galibi littattafan gajerun labarai
waɗanda
hukumomi suka samar sun fi mayar da hankali ne kan taskace adabin baka domin
amfani ga makarantu da kuma cusa darussan koyar da tarbiyya ga yara cikin
al’umma.
3.1.2 Zango na Biyu: Ɗaiɗaikun Marubuta da Bunƙasar Gajerun Labarai (1971-2013)
Daga shekarar 1971, marubuta maza da mata, a ɗaiɗaikunsu, suka fara samar da rubutattun gajerun labaran Hausa ta fuskoki
mabambanta a cikin littattafai. Littattafan sukan kasance ko dai kundin gajerun
labarai na marubuci ɗaya ko kuma haɗaka ta marubuta da yawa cikin
littafi guda ɗaya, walau a kan jigo ɗaya ko mabambantan jigogi.
A
irin wannan fasali ne, a shekarun 1978 zuwa 1982, aka samar da littattafai guda
huɗu na gajerun labarai. Wato, a shekarar 1978
aka samu Alhaji Hyder Aliyu ya
rubuta littafin Abokin Hira 1, sai
kuma littafin Da'u Fataken Dare, na
Malam Tanko Zango wanda ke ƙunshe da gajerun labarai guda huɗu(4) mabambanta, wato labarin “Da’u Fataken Dare” na Malam Tanko
Zango da labarin “Sarki Mai Gaskiya” na Malam Abdu Maƙarfi da labarin “Wa Ya Fi Adalci?” na Malam Nuhu
Bamalli da kuma labarin Wane Ne Bunu?” na Malam Jumare Zariya.
Littafin Nuni Cikin Nishaɗi na Hassana Umar shi ne ya biyo baya a shekarar 1980.
Littafi ne da ya ƙunshi gajerun labarai da aka samar daga labarun gargajiya domin taskace al’adu na
zamantakewar ƙasar Hausa, kamar yadda marubuciyar ta bayyana a shimfiɗar littafin. Sai a shekarar 1982 Alhaji Hyder Aliyu ya fitar da littafin Abokin Hira 2.
Baya ga wannan, a shekarar 1979 da ta 1982, Thomas Nelson ya wallafa wasu
littattafai biyu masu ƙunshe da gajerun labarai, wato Hikayoyin
Kaifafa Zukata 1 & 2 waɗanda Malam Aminu Kano ya samar da su daga labaran gargajiya da hikayoyi da
tarihi da tarihihi. Cibiyar bincike ta Mumbayya
House wadda take ƙarƙashin Jami’ar Bayero Kano, ta sabunta su a shekarar 2003. Su waɗannan littattafai, kamar yadda sunansu ya nuna, ƙunshe suke da hikayoyi
da labarai na gargajiya waɗanda marubucin ya tattara su domin kyautata tarbiyyar yara masu tasowa da
manufar ‘yan baya su yi koyi.
Daga wannan lokaci, sai a shekarar 2001 aka samu littafin Gajerun Labarai, na Bashir Othman Tofa,
wanda yake ƙunshe da gajerun labarai guda takwas (8) waɗanda marubucin ya samar ta hanyar ƙagawa daga batutuwan da ya ci karo da su a rayuwa ko kuma
suke tattare da rayuwar tasa, kamar yadda marubucin ya bayyana cewa:
“Ina tabbatar wa
da masu karatu cewa dukkannin waɗannan labarai nawa ne, koda yake za
ta yiwu na sami matashiyar ne daga wasu al’amura na rayuwata
ko kuma daga nazarin zantuka ko rayuwar wasu mutane daban da na ji a wani guri.” (Tofa, 2001:
Shf. 4).
Ke nan, ana iya cewa littafin Gajerun
Labarai na Bashir Tofa, shi ne kundi na rubutattun ƙagaggun gajerun labaran Hausa na
farko da aka samu, wanda marubuci ɗaya ya rubuta a karan kansa ba da
gudummawar wata hukuma ba. Waɗannan labaran sun kasance ba fassaro
su aka yi ba, ba kuma labaran baka ne aka taskace ko baddala ba, a’a ƙaga su aka yi domin
samar da littafin gajerun labaran Hausa na zamani.
Daga wannan lokaci, sai a shekakar 2010 aka samu littafin Magana Doki Ce daga Sa'idu Sulaiman.
Littafin ya ƙunshi gajerun labarai guda goma sha biyu (12), waɗanda marubucin ya gina su ta bin salon zubi irin na littafin Magana Jari Ce na Abubakar Imam. Sai dai
saɓanin yadda aka bayyana ita magana, ai jari ce ta yadda Waziri Aku ya yi
amfani da fasaharsa ta ruwaito labarai domin ɗauke hankalin Musa kada ya fita fagen yaƙi a littafin Magana Jari Ce I-III. Shi Sa’idu Sulaiman ya gina uwar labarin nasa
ne a kan wani mai suna Maishanu wanda yakan sanya gasar a ba shi labarai masu
nishaɗantarwa duk lokacin da yake hutawa a gidan gonarsa bayan sallar la’asar a kowace
rana. Shi ya sa ya shimfiɗa dokoki uku ga duk wanda zai shiga
gasar bayar da labarin. Wato labarin ya kasance ba a taɓa jin sa a bakin wani ba, kuma na nishaɗantarwa ne, sannan ya zama yana ɗauke da wani darasi ko nasiha ga al’umma.
Abu mafi muhimmanci a wannan gaɓar shi ne, salon gina gajerun
labarai daga uwar labari irin yadda aka yi a littattafan Dare Dubu Da Ɗaya da kuma Magana
Jari Ce, shi ne aka yi amfani da shi aka gina labaran littafin Magana Doki Ce.
Har ila yau, wani fasali da aka fara samu a wannan zango shi ne, ƙoƙarin ƙungiyoyin marubuta wajen samar da rubutattun
gajerun labaran Hausa. Ire-iren waɗannan ƙungiyoyi sun haɗa da Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya (Association
of Nigerian Authors, ANA) reshen jihar Kano wadda ta samar da littafin Ƙwaryar Ƙira a shekarar 2010. Littafin, wanda Farfesa Yusuf M. Adamu
da Ado Ahmad Gidan Dabino suka yi wa edita, ya ƙunshi dukkan ɓangarori uku na rubutaccen adabi. Ya ƙunshi rubutacciyar waƙa da rubutaccen wasan kwaikwayo da
kuma rubutaccen labari. Sai dai labarai ashirin da ɗaya (21) ne daga cikin ashirin da biyu (22) da suke cikin littafin, suka
kasance gajerun labarai daga marubuta mabambanta maza da mata. Idan aka aza a
kan sikelin gane gajerun labarai da aka bayyana a baya. Ko ba komai littafin ya
kasance ɗanba ga ƙungiyoyin marubuta wajen yin haɗaka ko gamayya domin samar da
rubutattun gajerun labarai.
Daga abin da ya gabata, an lura wannan
zango ya samar da littattafan gajerun labarai daga ɗaiɗaikun marubuta ne masu ɗauke
da jigogin tarbiyya da nishaɗantarwa
da kuma samar da abin karantawa a makarantu, ƙari
a kan abin da hukumomi suka samar. Wani abin lura kuma shi ne, a wannan zango
ne aka fara samun haɗaka na marubuta maza
da mata domin samar da littafin gajerun labarai ƙarƙashin inuwar wata ƙungiya.
3.1.3 Zango na uku: Gasa, Ƙungiyoyi da Gajerun
Labarai a Intanet (2013-2023)
Bincike ya tabbatar da cewa, an fara shirya gasa domin samar da ƙagaggen labarin Hausa tun a shekarar 1927 a
Kwalejin Katsina, amma fa abin da aka rubuta ɗin bai zo hannu ba.
Baya ga wannan, kamar yadda aka
yi bayani, a shekarar 1929 kuma Hukumar Ƙasa da Ƙasa ta Nazarin Harsuna da Al’adun Afirka mai mazauni a Ingila ta samar da
rubutattun gajerun labaran Hausa ta hanyar gasa, wato Hausa Stories guda biyu na H.B.G Nuhu da na Malam Dodo, da kuma Labaran Hausa na Ɗan Malam Alƙali Sokoto (Ɗan’Amarya, 2012: Shf. 78).
Daga wannan lokaci, an ci gaba da samun gasa
domin samar da ƙagaggun labaran Hausa, tun daga shekarar 1933. Amma sai a gasar Gidauniyar Injiniya
Muhammad Bashir Ƙaraye, wadda aka fara gabatarwa tun daga
shekarar 2007 har 2009, ta samar da littafin Saba Ɗan Sababi na Hafsat M.A Abdulwaheed, wanda ya zo na
uku a gasar ta shekarar 2008. Littafin ya kasance kundin gajerun labarai ne
guda goma sha biyu (12) masu alaƙa da juna, inda
marubuciyar ta tsara su da zubi irin na littafin Magana Jari Ce 1-3 na Abubakar Imam. Ta gina gajerun labaran da
suke cikin littafin ne daga uwar labarin da ta ƙulla
tun daga farko (Faruƙ, 2018). A taƙaice dai, littafin na gajerun
labarai ne masu ɗauke da darussa na nishaɗantarwa da tarbiyyantarwa waɗanda aka tsara domin samar da abokin hira
ga masu sha’awar karatun littattafai.
Bugu da ƙari, Makarantar Malam Bambadiya,
wadda Farfesa Ibrahim Malumfashi ya assasa ta kafar intanet ta Facebook, ita ma ta kasance wani bagire
da ya bunƙasa rubutun gajerun labarai na Hausa. Domin kuwa a ranar 24 ga watan
Nuwamba na shekarar 2013 aka samar da gajerun labarai da aka raɗa wa suna ‘Yan Yau. Labari ne a kan tarbiyyar yara wanda ya ƙunshi gajerun labarai daga marubuta
daban-daban, waɗanda suka kasance ɗalibai ne na wannan
makaranta ƙarƙashin jagorancin Farfesa Ibrahim Malumfashi. Shi ne ya kawo uwar labarin
mai suna ‘Yan Yau, a take kuma wasu marubutan suka ƙulla da nasu labaran masu alaƙa da juna.
Bincike ya tabbatar da cewa rubutun
labarin Hausa a kafar intanet, ya samo asali ne tun daga Majalisar Marubuta ta
Intanet wato, Yahoo Group wadda
Farfesa Abdallah Uba Adamu ya assasa a shekarar 2003. Wannan kafa ce ta fara
share fagen rubutun gajerun labarai na Hausa a intanet. Sai dai kuma yawaitar kwamfutoci da wayoyin smartphones da androids daga shekarar
2013, ya sanya karance-karance ga matasa ya koma
intanet, musamman a shafukan sada zumunta (Maimota, 2021:133-134).
A taƙaice dai, yawaitar tu’ammali da kafofin sadarwa na zamani
ya taimaka gaya wajen bunƙasar rubutun gajerun labarai, ta yadda hatta gasannin da
akan sanya domin samar da rubutattun gajerun labarai, manhajoji irin su Facebook da WhatsApp suna taimakawa wajen yayatawa da shelanta dokoki da sauran
batutuwan da suka jiɓance su gasannin.
Saboda haka, daga shekarar 2013 aka fara shirya
gasa, musamman domin samar da rubutattun gajerun labarai lokacin Makarantar Malam Bambadiya (wani dandali
a kafar intanet ta Facebook) ƙarƙashin jagorancin Farfesa Ibrahim Malumfashi, ta shirya gasar rubutun
gajerun labarai a kan matsalar bara a ƙasar Hausa, wadda aka yi bikin bayar da kyautuka a watan Satumbar 2014 a
Jami’ar Jihar Kaduna. An tsara za a
buga labaran da suka shiga gasar kuma suka ƙayatar daga na ɗaya zuwa na ashirin (20) cikin littafin da aka raɗa wa suna Jamhuriyar
Mabarata, wanda har zuwa lokacin da ake gudanar da binciken nan, ba a buga
littafin ba.
Daga wannan lokaci, sai kuma gasar ta lafa, inda ɗaiɗaikun marubuta da ƙungiyoyi suka ci gaba da samar da gajerun labarai
bisa mabambantan manufofi. A daidai wannan lokaci ne Ƙungiyar Marubutan Mace Mutum ta
samar da littafin gajerun labarai mai suna Hannu
Da Yawa...(HD), a shekarar (2014). Littafi ne wanda aka tattara gajerun
labarai guda talatin da bakwai (37) waɗanda marubuta mata zalla
suka rubuta a kan batutuwan da suka shafi rayuwar al’umma kai-tsaye. An tsara
labaran ƙarƙashin kowane batu da ya shafi talla da fyaɗe da aikatau da rikice-rikice da almundahana da yaƙi da jahilci da daba da
barace-barace da kuma rayuwa irin ta yanar gizo. Duk da yake wasu labaran da
suke cikin littafin sun shafi rayuwar maza da mata musamman batutuwan da suka
shafi daba da barace-barace da almundahana. Shi ya sa a gabatarwar littafin aka
bayyana cewa:
“In aka duba waɗannan labarai za a ga sun taɓa jigogi da dama cikinsu akwai bautar
da ‘ya’ya mata ta hanyar talla da aikatau da kuma cin zarafin mata ta hanyar
fyaɗe. Sauran labaran sai suka fita daga cikin gida zuwa duniyar maza inda suka
taɓo bayanai a kan almundahana da rashawa da cin hanci da maguɗin zaɓe da rikicin ƙabilanci da bara da yaƙi da jahilci da sauransu.” (HD: Shf. 6).
Ko ba komai dai, littafin ya sake buɗe wani fage na bunƙasar rubutattun ƙagaggun gajerun labaran
Hausa, inda a karon farko aka samu kundi guda na gajerun labarai daga marubuta
mata a ƙungiyance. Su kuwa marubutan a ɗaiɗaikunsu, sun ci gaba da samar da littattafan gajerun labarai jefi-jefi.
Misali, daga shekarar 2013 zuwa 2016, Kabiru Yusuf Fagge (Anka) ya samar da
littattafai guda biyar (5) na gajerun labarai waɗanda suka haɗa da:
i.
Mu Sha Dariya (2013)
ii.
Kai Ma Ka Dara (2015)
iii.
Abokin Dariya (2016)
iv.
Malamin Ban Dariya (2016)
v.
Gidan Dariya (2023).
Akwai kuma Yahaya Garba
(So), wanda ya samar da littattafai biyu na gajerun labarai a shekarar 2017,
wato Mati da Lado (2017) da Wuta Sallau (2017).
A shekarar 2018 kuwa an
sake jin ɗuriyar rubutattun gajerun labarai daga ƙungiyoyin marubuta, inda aka samar
da littafin Gobarau daga taron
Gamayyar Marubutan Hausa, wanda aka gudanar a Katsina a ranakun16 zuwa 18 ga
watan Maris na shekarar 2018. Littafin yana ƙunshe da gajerun labarai daga
marubuta maza da mata, sai dai littafin bai shiga kasuwa ba.
Koda yake, daga shekarar 2016 zuwa 2018, gasar rubutun gajerun labarai ta
sake kunno kai da wani sabon salo, inda aka
shimfiɗa tabarmar ware wani jigo na musamman domin sanya gasar rubutun gajerun
labarai a kan shi. Wato, an samu wasu gasannin waɗanda suka haɗa da gasar gajerun labarai a kan jigon talauci,
wanda Makarantar Malam Bambadiya suka
haɗa gwiwa da Pleasent Library Katsina suka ɗauki nauyin shiryawa a shekarar 2018. An samu
labarai guda uku waɗanda suka lashe gasar, su ne “Matalauciyar Rayuwa” na Kabiru Yusuf Fagge
(Anka) da “A Sasanta” na Hassana Abdullahi Hunƙuyi
da kuma “Da Sandar Hannunka” na Zakariyya Haruna Ɗanladi.
Ita ma dai wannan gasar, ba a samar da littafi na labaran da suka yi nasara ba.
Bugu da ƙari,
a wannan zango ne hukumar Gidan rediyon BBC
da ke Landan suka fara bayar da gudummawa sosai wajen bunƙasar
gajerun labaran Hausa ta hanyar gasar Hikayata,
wadda suka assasa tun daga shekarar 2016 zuwa yau (2023), domin rubutun gajerun
labarai na mata zalla. Babbar manufar wannan gasa ita ce fitar da matsalolin da
suke addabar mata daga bakin mata ‘yan’uwansu, kamar dai yadda Bahaushe ya ce, ‘ciwon
‘ya mace na ‘ya mace ne’. To, sai dai ba a keɓe wani jigo na musamman da za a rubuta
labaran a kai ba. Duk da haka, a bisa wannan fasalin, duk shekara ana fitar da
labarai guda ɗari (100). Daga cikin ɗarin ne ake tace guda ashirin da biyar (25),
a cikinsu ne ake zaɓen guda uku (3) waɗanda suka yi zarra a matsayin na ɗaya(1) zuwa na uku (3). Ana karrama
marubutan nasu, inda na huɗu(4)
zuwa na goma sha biyu (12) kuma ake karanta su tare da ɗora su a kafafe da shafukan yanar gizo na
BBC Hausa ɗin, irin su youtube da sauransu. A ƙarshen
gasar ta kowace shekara,
ana karrama marubutan labaran da
suka lashe gasar da kyaututtuka. Amma har yanzu ba a taɓa tattara waɗannan gajerun labarai cikin littafi ba, saboda manufarsu ita
ce a saurara, ba a karanta ba. Sai dai ana wallafa su kuma ana sanya sautin murya na karatun labaran a
shafin www.bbchausa.com.
Wani abin burgewa shi ne, a shekarar 2020, Bankin Kula da Muhalli da Tsarin Yanka Filaye na
Tarayya (Federal Mortgage Bank), ƙarƙashin jagorancin shugaban bankin wato Arc. Ahmed Musa Ɗangiwa ya shirya gasar samar da gajerun labarai
na Hausa waɗanda suka haska mafita ga matsalolin muhalli irin su yanka
fili ba bisa ƙa’ida ba da matsalolin gidan haya da matsalar mallakar muhalli a
wuraren da ba su dace
ba, da kuma yanayin aikin wannan bankin.
Gajerun labaran da suka yi zarra, wato na ɗaya zuwa na uku su ne,
“Abun Da Ka Shuka” na Bashir Adamu, sai “Laifin Wa?” na Bilkisu Muhammad
Garkuwa, sai kuma “Sanin Hanya” na Aliyu Rabe Aliyu. Sai kuma labaran da suka samu yabo, aka bi su da kyaututtuka guda goma.
An fitar da sakamakon wannan gasa kuma an bayar da kyaututtuka
ga waɗanda suka sami nasara a watan Disamba na shekarar 2020. Sannan an buga waɗannan gajerun labarai a cikin littafin da
aka raɗa wa suna Muhalli, Sutura.
Daga wannan lokaci sai aka buɗe fage na wallafa sakamakon gasar gajerun labarai
cikin littafi. Domin kuwa a shekarar 2021 kamfanin Media Trust da haɗin gwiwar Gandun Kalmomi da Open Arts sun samar da wani littafi na gajerun labarai mai suna Dambarwar Siyasa. Littafi ne da ya ƙunshi gajerun labarai guda goma sha biyar (15) waɗanda aka tace daga cikin labarai (285) da suka
shiga gasar rubutun gajerun labarai kan siyasa, da kamfanin ya sanya a shekarar
(2020).
Gajerun labaran da suka yi zarra a wannan gasar
su ne, “Dimokuraɗiyyar Talaka” na Rufaida Umar Ibrahim da “Tufka da Warwara” na Mubarak Idris Abubakar da “Ranar Ƙin Dillanci” na Ubaida Usman, waɗanda suka zo na ɗaya da na biyu da na uku. Wannan ya haifar da
wani sabon jigo a rubutun gajerun labaran Hausa na gasa.
Hada-hadar siyasa da yaƙin neman zaɓen shekarar 2022 zuwa 2023, su ma sun taimaka
wajen shirya gasar rubutun gajerun labaran Hausa domin kuwa a shekarar 2022
Gidauniyar Mun Gani a Ƙasa Foundation a jihar Katsina, ƙarƙashin jagorancin Injiniya Surajo Yazid Abukur, ta sanya gasar rubutun
gajerun labarai da rubutattun waƙoƙi a kan ɗan takarar gwamnan jihar Katsina na jam’iyyar APC, kuma gwamnan Katsina a yanzu, wato Malam
Dikko Umar Raɗɗa. An tattara labarai da waƙoƙin da aka zaɓa waɗanda suka yi zarra da kuma waɗanda suka sha yabo a cikin littafin da aka raɗa wa suna Mizani,
wanda aka buga a shekarar 2023 kuma Dakta Shu’aibu Mustapha da Dakta Bashir Abu
Sabe da Abdulrahman Aliyu, su ne editoci na littafin.
Gajerun labarai guda goma (10)
da suka fito cikin littafin su ne, “Rawar Gani” na Fatima Bello Bala da “Tudun
Tsira” na A’isha Adam Hussain da “Shugaba Nagari” na Amrah Auwal Mashi, waɗanda suka zo na ɗaya da na biyu da na uku. Sai kuma sauran guda
bakwai waɗanda suka sha yabo. Duk labaran da waƙoƙin na siyasa ne, amma ko ba komai, wannan gasa mai ruhin siyasa, ta
taimaka wajen bunƙasar rubutattun gajerun labaran Hausa, tun da
yake, an dubi abin da ya shafi tsarin shugabanci, wato zaɓen shugaba nagari abin koyi, aka turke jigon
gasar rubutun gajerun labaran a kai.
Haka kuma, a shekarar 2022 ma
Gidauniyar Arc. Ahmed Musa Ɗangiwa ta sake sanya gasa ta biyu domin rubutun gajerun labarai a kan
matsalolin matasa, musamman abin da ya shafi taɓarɓarewar tarbiyya da zaman kashe-wando da kuma
safara da shaye-shayen kayan maye. Wannan gasar ta samar da littafin gajerun
labaran Hausa wanda aka sanya wa suna Ɗaukar Jinka. Littafin
yana ɗauke da gajerun labarai guda goma sha biyar (15) tun daga labarin “Tun Ran Gini” na Amrah Auwal Mashi da “Son Zuciya” na Rufaida Umar Ibrahim da “Sara Suka” na Fatima Bello Bala da “Ka Fi Ɗan’uwa” na Jibrin Adam Jibrin Rano, waɗanda suka zo na ɗaya zuwa na uku. Sai sauran labarai goma sha biyu
da suka tayar da littafin.
Baya ga waɗannan ma, ana iya cewa a yanzu, gasar rubutun gajerun
labarai na Hausa ta zama ruwan dare, ta inda wasu zauruka na marubuta a kafafen
sada zumunta ma sukan sanya gasar rubuta gajerun labarai cikin wani ƙanƙanin lokaci su ɗan bayar da na-goro ga waɗanda suka yi nasara. Ko kuma idan
wani marubuci yana bukin murnar zagayowar ranar haihuwarsa ko bukin aure, ko
wani bukin, nan ma sai ya sanya gasar rubutun gajerun labarai, musamman ga
marubuta masu tasowa domin ƙarfafa masu gwiwa. A irin wannan fasalin ne a shekarar
2020 aka sanya gasar rubutun gajerun labarai domin murnar bukin Fadila Aliyu
Kurfi. Sakamakon gasar ya samar da gajerun labarai guda goma (10) waɗanda Kabiru Yusuf Anka da Shamsuddeen Fatimiyya da Zaidu Barmo suka tattara
labaran, su kuma Abdulrahman Aliyu da Ibrahim Muhammad Indabawa da Shamsuddeen
Fatimiyya suka kasance alƙalai a gasar wadda ta samar da littafin Alƙalami...
Bugu da ƙari, a shekarar 2022 lokacin da aka naɗa Aminu Alan Waƙa sarautar Sarkin Ɗiyan Gobir, ya sanya gasar rubutun gajerun labarai wadda ya raɗa wa suna Gasar Tsibirin Gobir wadda ta samar da labarai guda goma (10).
Wani abin la’akari shi ne, duk da cewa gasa ce ta fi
tashe a wannan zangon, amma marubuta a ɗaiɗaikunsu ko a ƙungiyance sun ci gaba da samar da rubutattun gajerun labarai a cikin
littafi ko a intanet. Domin kuwa, ƙungiyar Dot and Pen
Gombe Writers Association ta jihar Gwambe, ta samar da littafin gajerun
labarai masu jigon tsaftace siyasa domin gudanar da ita ba tare da cutarwa ba.
Labarai goma sha ɗaya (11) ne daga marubuta goma sha ɗaya (11) aka samar cikin littafin da aka sanya wa suna Siyasa Ba Da Gaba Ba.
Wata ƙungiyar da ta sake bunƙasa rubutun gajerun labaran Hausa ita ce Ƙungiyar Tuntuɓa ta Marubutan Arewacin Nijerya, wato Northern
Nigerian Writers Summit (NNWS). A shekarar 2022, wannan ƙungiya ta samar da kundi
na rubutun fasaha wanda ta raɗa wa suna Tulu: A Multilingual Anthology of Northern Nigerian New Writings.
Shugaban ƙungiyar, Dakta Bashir Abu Sabe da wasu kamar Isyaku Bala Ibrahim da Khalid
Imam da Farfesa Musa Ahmed Karkarku, su ne suka kasance editoci na wannan
aikin.
Shi ya sa da yake ƙungiyar ta Arewacin Nijeriya ce gaba ɗaya, ta tattara rubutattun
gajerun labarai da rubutattun waƙoƙi da bitar littattafai da tattaunawa daga karikitan adabi na Ingilishi da
Hausa da Fulfulde da Nupe. Saboda haka, a fitowa ta farko ta wannan kundi, an
samar da rubutattun gajerun labaran Hausa guda goma sha uku (13) daga marubuta
maza da mata.
Har ila yau, Gamayyar Marubutan Zazzau a farkon shekarar 2023 su ma sun
samar da littafin Hannu Ɗaya Ba Ya Ɗaukar Jinka. Sun tattara gajerun labarai guda
goma (10) a kan batutuwan da suka shafi barace-barace da bangar siyasa da zaman
gidan haya da fasahohin al’umma da sauransu, waɗanda marubuta maza da mata na lardin Zazzau suka samar. Wani abin la’akari
shi ne, cikin gajerun labarai goma(10) da suka tayar da wannan littafi, shida
(6) duk daga marubuta mata ne, ragowar huɗun (4) ne daga marubuta
maza.
Daɗin daɗawa, a shekarar 2022 kuma, Muhammad Yahuza Bello ya samar da littafin Dahuwar Ruwan Sanyi, mai ɗauke da gajerun labarai guda ashirin da biyu (22). Labaran da suke cikin
littafin sun shafi yadda ake amfani da wasu hanyoyi na salon dahuwar ruwan
sanyi wajen magance wasu ƙalubale da aka fuskanta a rayuwar yau da kullum. Shi ya
sa ma marubucin ya bayyana cewa wasu daga cikin labaran da ya ƙaga cikin littafin sun
faru a rayuwa ta zahiri.
Bugu da ƙari, a shekarar 2022 ɗin dai an samu wasu littattafai biyu
na rubutattun gajerun labarai na Hausa daga wani marubuci mai suna R.A Adam
daga jihar Gwambe. Littattafan su ne Lu’ulu’u
A Cikin Juji, wanda yake ɗauke da gajerun labarai guda biyar, waɗanda marubucin ya gina su a kan labaran da wasu manyan mutane suke bayarwa
game da irin baiwar da Allah ya masu tun daga lokacin da suke ba komai ba, har
zuwa lokacin da suka zama komai. Littafi na biyu shi ne Duniyar Audu, wanda yake ƙunshe da walƙiyar labarai, wato flash
fiction guda ashirin (20), domin galibi labaran cikin littafin ba su ma kai
adadin kalmomi 500 ba. An gina labaran ne duk a kan babban tauraro ɗaya, wato Audu. Kuma jigon nishaɗantarwa, shi ne ya ratsa kuma ya haɗiye labaran littafin.
An yi ƙoƙarin samar da kundin gajerun labaran
Hausa mai suna Rigakafin Korona a shekarar
2021, wanda bai fita ba sai a shekarar 2023. Littafin da Khalid Imam tare da
Umma Aliyu Musa suka kasance editoci, ya ƙunshi gajerun labarai guda talatin da huɗu (34) daga marubuta talatin da ɗaya (31), wato mata goma sha uku
(13) da maza goma sha takwas (18). Cikin marubutan kuwa har da shehunnan
malamai da fitattu da sababbin marubuta da kuma ma’abota Hausa waɗanda ba Hausawa ba ne su, daga ƙasashen Jamus da Sin. An karkasa labaran zuwa sassa uku,
inda kowane sashe yake ƙunshe da labarai masu alaƙa da juna ko kuma masu alƙibla guda dangane da batutuwan da
suka shafi annobar ta cutar Korona. Wannan littafi ya kasance irinsa na farko a
matsayin kundin gajerun labaran Hausa daga marubutan Hausa da manazarta a ciki
da wajen ƙasar Hausa, waɗanda suka haɗa da Hausawa da waɗanda ba Hausawa ba, duk a kan jigo ɗaya, wato annobar cutar
korona. Wannan ya nuna cewa annobar korona, tana daga batutuwan da suka bunƙasa gajerun labaran
Hausa a wannan zango. Domin kuwa, kafin wannan littafin ma, an samu wasu
labaran masu ruhin cutar korona a kundin Tulu
na ƙungiyar Tuntuba ta Marubutan Arewacin Nijeriya (NNWS) da wasu labaran na Gasar Hikyata
ta BBC Hausa da sauransu.
Har ila yau, a shekarar 2023 an samu ɓullar wani kundin
gajerun labarai mai suna Darussan Malam
Sanau. Littafin ya zo da wani fasali na koyar da harshen Larabci ta yadda
aka tsara darussa guda goma sha biyar (15) waɗanda Malam Sanau yake gabatarwa. A ƙarshen kowane darasi ne sai ake kawo gajeren labari wanda
zai taimaka wajen sake fito da darasin da aka gabatar a fili. Da wannan fasali
littafin ya ƙunshi gajerun labarai waɗanda aka samar daga uwar labarin mai
suna “Malam Sanau”, sai kuma ‘ya’yan labaran da suka zo a ƙarshen kowane darasi guda goma sha
biyar (15). Daga nan sai aka rufe da labarin “Bankwanan Malam Sanau.”
Wani abin lura a wannan zango shi ne Bukin Baje-kolin Littattafai da
Fasahohin Hausawa (HIBAF), wanda kamfanin Open
Arts ke gudanarwa duk shekara, ya samar da wata kafa ta bunƙasa rubutun gajerun
labaran Hausa. A taron na shekarar 2021 wanda aka gudanar a Kaduna a ranakun
21-23/10/2021, an horar da wasu marubuta masu tasowa, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Ibrahim
Malumfashi, inda suka samar da gajerun labarai guda goma sha takwas (18), waɗanda suka tayar da littafin Furen Ƙarya wanda aka buga a shekarar 2023.
Akwai kuma wasu gajerun labarai da ake samu daga wasu marubutan waɗanda suke ɗorawa a shafukansu ko dandalinsu na Facebook ko WhatsApp ko
manhajojin irin su Okada da wattpadd da
sauransu. Misalan gajerun labaran da ake samu a kafar Facebook sun haɗa da: “Kitimurmurar Gado” na Amina Hassan
Abdulsalam da “Kuskuren Abokai” na Imam Abdu Bandirawo da “Sanyi Ne” na Kabiru Yusuf Fagge da
“Laifinta Ne Kuwa ?” na Muhammad Bin Ibrahim da “Ba Ku Samu Alƙali Ba” na Musaddam
Idriss Musa da “Masallacin Garinmu” na Ɗanladi Haruna da “Mahaukacin Gida” na Hassana
Abdullahi Hunƙuyi, da sauransu.
4.0 Sakamakon Bincike
Wannan bincike ya gano cewa gajerun labarai ne suka buɗe fagen rubutun ƙagaggun labarai na Hausa tun zamanin Turawa. Haka kuma, hukumomin su ne
suka fara assasa rubutun gajerun labaran Hausa. Bayan haka, fitillar da ta fara haska rubutun labaran
Hausa daga nau’in tattara ko taskace gajerun labarai ne. Domin kuwa, ko da
Turawa suka kafa mulkin mallaka daga wannan fasali suka ɗora wajen bunƙasa
rubutaccen adabi a ƙarƙashin hukumomin
inganta adabi.
An gano cewa a rubutattun gajerun labaran Hausa, akwai waɗanda asalinsu labarai ne na
gargajiya waɗanda ake da su tun tale-tale, tun kafin Bahaushe ya samu
hanyar rubutu da karatu. Daga bisani ne aka taskace su cikin littattafai domin
a adana. Wasu kuma labaran bakan ana baddala su ne ta siffar gajerun labarai. Ire-iren waɗannan labarai ne waɗanda aka taskace su domin kyautata tarbiyyar yara masu tasowa da kuma adana
tunane-tunanen Bahaushe domin kada su salwanta. Wasu labaran kuwa, suna da
tushe daga wasu al’ummomi na wasu nahiyoyin duniya, musamman Larabawa da Turawa,
waɗanda kuma aka fassaro su zuwa harshen Hausa. Hatta a irin littattafan
gajerun labarai na haɗaka ta ƙungiyoyi, ana samun nau’in fassararrun
gajerun labarai. Sai dai kuma wasu daga cikin gajerun labaran da ake samu yanzu
a ƙasar Hausa, musamman na cikin littattafai, ana samar da su ne ta hanyar ƙagawa. Saboda haka, ana
iya kiran wannan nau’i na na rubutattun gajerun labarai a matsayin ƙagaggu.
An gano cewa hukumomi, tun daga shekarar 1929, sun bayar da gudummawa sosai
wajen bunƙasar rubutattun gajerun labaran Hausa daga ɗaiɗaikun marubuta ta hanyar ɗaukar nauyin bugawa da tacewa ko
kuma tattarowa da bugawa a hukumance. Wannan fa, ban da hukumomin da suke samar
da gajerun labarai ta hanyar sanya gasa irin su BBC Hausa da sauransu.
Daga ƙarshe, an gano cewa gasa tana taimakawa wajen bunƙasar rubutun gajerun labaran Hausa,
musamman saboda romon da marubutan suke samu daga masu ɗaukar nauyin gasannin yana ƙara masu ƙwarin gwiwar samar da labaran. Shi ya sa a yau, gajerun
labarai suke ƙara bunƙasa har ma suke neman rufe shafin dogayen labaran Hausa.
5.0 Naɗewa
Bisa taƙaitawa, wannan takarda ta ƙunshi bayanai ne kan samuwa da bunƙasar rubutattun gajerun labaran
Hausa. Tun farko, an fayyace ma’anar gajeren labari tare da bayanin siffofinsa
da abubuwan da ya ƙunsa. Sai kuma aka bayyana samuwa da bunƙasarsa daga tubalin da hukumomi suka
aza da kuma gasannin da suka taimaka wajen bunƙasar su, tare kuma da gudummawar ɗaiɗaikun marubuta ko ƙungiyoyinsu; walau cikin littafi ko a intanet. An fasalta bunƙasar ne cikin zanguna
mabambanta har uku daga shekarar 1929 zuwa 2023. A ƙarshe kuma sai aka kawo sakamakon
bincike da bayanin naɗewa.
Manazarta
Abdo El-Rahman, H. E. M. (1996). “The Oral in Written: A Study of Orality
in Selected West African Short Stories.” Unpublished M.A Dissertation.
Department of English. Ahmadu Bello University, Zaria.
Adamu, Y. A. da Gidan Dabino A. A. (2010). Ƙwaryar Ƙira. Ƙungiyar Marubuta ta Jihar
Kano. Kano: Adamu Joji Publishers.
Anderson, S. (1974). “Form, Not Plot” In
Current-Garcia, E. and Patrick, W. R. (1974)(ed). What is the Short Story?
Glenview, IL: Scott, Foresman & Co.
Bates, H. E. (1972). The Mordern
Short Story: A Critical Survey. London: Michael Joseph Ltd.
Besseler, M. (2011). Theories and Typologies of Short Stories. In: Basseler & Nünning
(eds.) A History of the American Short Story. Genres – Periods – Developments. Trier: WVT 2011. PP, 4164.
Bunza, U. A. (2015). “Talife-Talifen Hausa a
Zamanin Mulkin Mallaka: Yanayinsu da Sigoginsu.” Kundin Digiri na Biyu. Sashen
Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Danfodiyo.
Di Yanni, R. (2002). Literature: Reading
Fiction, Poetry and Drama. New York: McGraw- Hill Companies Inc.
Ɗan’amarya, I. A. (2012). “Tarihi
da Gudummuwar Gasa a Samarwa da Bunƙasa Kagaggun Labaran Hausa.” Kundin Digiri na Biyu. Sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya.
Sakkwato: Jami’ar
Usmanu Danfodiyo.
Ɗangambo, A. (1984).
Rabe-Raben Adabin Hausa da
Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph Publishing Company.
Ɗangambo, A. (2008).
Rabe-Raben Adabin Hausa. Sabon Tsari. Zaria:
Amana Publishers.
Faruk, A. (2018).“Nazarin Biɗau a Cikin Littafin Saba
Ɗan Sababi na Hafsat A.M Abdulwahid.” Cikin Sulaiman, A.I(ed). Kadaura Journal of Hausa Multi
Disciplinary Studies. Vol. 1, No. 4 January 2018. Special Edition.
Department of Nigerian Languages and Linguistics. Kaduna: Kaduna State University, Kaduna- Nigeria.
Ferguson, C. S. (1994). “Defining Short
Story. Impressionalism and Form” In May, C.E.(Ed). The New Short Stories Theories. Athens, Ohio: Ohio University Press, Pp.
218-230.
Frye, N. (1957). Anatomy of Criticism. Four Essays. Princeton & Oxford:
Princeton University Press.
Goring, P. et-al. (2001). Studying
Literature. London: Bloomsbury Publishing Plc.
Gusau, S. M. (2008).
Dabarun Nazarin Adabin Hausa. Kano:
Benchmark Publishers
Limited.
Gusau, S. M. (2015).
Mazhabobin Ra’i
da Tarke a Adabi da Al’adu na Hausa. Kano:
Century Research Publishing
Limited.
Hawthorne, N. (1974). “Self-Criticism” In
Current-Garcia, E. and Patrick, W. R. (1974)(ed). What is the Short Story? Glenview, IL:
Scott, Foresman & Co.
Smith, J. (2001) (ed). Short Stories for
Students: Presenting Analysis, Context and Criticism on Commonly Studied Short
Stories. Volume 12. New York: The Gale Group.
Iheakaram, P. O. (1990). The Short Story in Africa: The Nigerian Situation
in Literature and Black Aesthetics.
Department of English and Literary Studies, University of Calabar. Nigeria:
Heinemann Educational Books. Ed. Earnest, N. Emenyonu.
Jibril, H. (2019). “Jigogin Gajerun Labarai don
Yara: Nazari Daga Littafin Ka Yi Ta Karatu.” Kundin Digiri na Farko. Sashen Harsunan Nijeriya
da Kimiyyar Harshe. Kaduna:
Jami’ar
Jihar Kaduna.
Maimota, A. S. (2021).“Kwatanta Wasu Littattafan Ƙagaggun Labaran Hausa da Wasu Ƙagaggun Labaran Hausa na Shafukan Sada Zumunta na Intanet.” Kundin Digiri na Uku, Sashen Harsunan
Nijeriya.
Kano: Jami’ar
Bayero.
Malumfashi, I.
(2009): Adabin Abubakar
Imam. Sakkwato: Garkuwa Media Service Ltd.
Malumfashi, I. da wasu(2015). Labarun Dare Dubu Da Ɗaya, Mujalladi na Ɗaya. Kaduna-Nijeriya. Garkuwa Media Services
Limited.
Malumfashi, I. (2019)
(ed). Labarin Hausa A Rubuce 1927-2018.
Zaria: Ahmadu Bello University Press and
Publishers.
Mathews, B. (1901). “The Philosophy of
Short Story.” In May, C.E.(Ed). The New
Short Stories Theories.
Athens, Ohio: Ohio
University Press, Pp. 73-80.
Mathews, B. (1901).
“The Philosophy of Short Story.” In Current-Garcia, E. and Patrick, W. R. (1974)(ed). What
is the Short Story? Glenview, IL: Scott, Foresman & Co.
May, C. E. (1994). “The Nature of Knowledge
in Short Fiction.” In May, C.E.(Ed). The
New Short Stories Theories. Athens, Ohio: Ohio University Press, Pp.
131-143.
Mukhtar,
I. (2004). Jagoran Nazarin Ƙagaggun Labarai. Kano:
Iya Ruwa Publishers.
Poe, E. A (1846). “The Philosophy of
Composition” In May, C.E.(Ed). The New
Short Stories Theories. Athens, Ohio: Ohio University Press, Pp. 59-72.
Pratt, M. L (1994). “The Short Story. The
Long and The Short Of It” In May, C.E.(Ed). The
New Short Stories Theories. May, C.E.(Ed).
Athens, Ohio: Ohio University Press, Pp. 91-113.
Ridout, A. K. and Stuart, J. (1968). Short
Stories for Discussions. Newyork: Charles Scribners Songs.
Sabe, B. A. (2011).
“Adabin Kasuwar Kano: Nazari da Sharhi
Game da Ƙagaggun
Labaran Hausa, 1984-2008”. Kundin Digiri na
Biyu. Sashen Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Tucan, G. (2014). What is a Short Story Besides Short? Questioning Minds in Search of Understanding Short Fiction. West University of Timişoara. DOI: 10.2478/rjes-2014- 0018.
Yahaya, I. Y.
(1988). Hausa a Rubuce: Tarihin
Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company
Limited.
Yusuf,
J. (2012). “Adabin Kirista: Nazari Kan Labarin Fatima.” Kundin Digiri Na Ɗaya. Sashen
Harsunan Nijeriya da Kimiyar Harshe,
Jami’ar Jihar Kaduna.
Yusufu, S. (2019). “Dabarun
Bayar da Labarai a Wasu Littattafan Balaraba Ramat Yakubu.” Kundin Digiri na Uku. Sashen Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu
Danfodiyo.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.