Mujaheed, Abdullahi & Aliyu, Abdulrahman(2024). “Ƙarshen Alewa Ƙasa: Hoton Sata a Labarin Idon Matambayi na Muhammadu Gwarzo”. Biram: Journal of Contemporary Research in Hausa Studies (Bijochs), Vol. 2, Issue. 1, June, 2024. Department of Nigerian Languages and Linguistics, Sule Lamiɗo University Kafin Hausa, Jigawa State. Pg 228-241, ISSN: 2992-6173.
ƘARSHEN
ALEWA ƘASA:
HOTON SATA
A LABARIN IDON MATAMBAYI NA MUHAMMADU GWARZO
Daga
Abdullahi
Mujaheed
Sashen Harsunan
Nijeriya Da Kimiyar Harshe,
Jami’ar Jihar Kaduna
Imel: mujaheedabdullahi@gmail.com
Waya:
+2348069299109, +2348156747550
Da
Abdulrahman Aliyu
Sashen Harshen Hausa, Kwalejin Ilimi Mai Zurfi ta Kaura
Nuhu Abdulƙadir, Rimi
Imel: ksarauta@gmail.com
Waya:+2348036954354
Tsakure
Sata tana cikin munanan ɗabi’un da al’ummar Hausawa suke ƙyama, sai dai duk da wannan ƙyama ba ta hana wanzuwar ɓarayin a cikin al’ummar ba, ba kuma a daina yin satar ba,
kamar yadda sauran munanan ɗabi’u irin su karuwanci da luwaɗi da maɗigo da caca suke cigaba da wanzuwa. Irin wannan kallon
hadarin kaji ya sanya duk wani aikin adabi da yake ƙunshe da hoton waɗannan lamurra bai cika samun tagomashi
a idon Hausawa ba, har a fagen nazari da sharhi. Shi ya sa labarin Idon
Matambayi duk da kasancewarsa ɗaya
daga cikin labaran da suka lashe gasar shekarar 1933 wadda ita ce ta haifar da
‘ya’yan fari a sahun rubutaccen labarin Hausa, bai sha rubdugu wajen manazarta
kamar takwarorinsa da aka buga a shekarar 1934-1935, da ma wasu da suka biyo
bayansu suka sha ba.
Ba komai ya haifar da wannan ƙarancin
kulawa ba illa kasancewar littafin ɗamfare
da labarin sata da dabarun sata, musamman ta wancan zamanin da aka rubuta a labarin. Sai dai da yake adabi ‘hoto’ ne ko
‘madubin’ rayuwar al’umma, su kuwa hoto ko madubi ba sa ƙarya, sukan hasko al’amari
ne yadda yake, shi ya sa wannan maƙala ta nazarci hoton sata a
littafin na Idon Matambayi. An yi amfani
da hanyoyin bincike na kai-tsaye waɗanda suka haɗa da karanta littafin na Idon Matambayi da kuma
karance-karance daga wasu littattafai da kundayen bincike masu alaƙa da batun da aka tattauna a takardar. Sai aka ɗora nazarin a kan ra’in lalatattun lamurra (Ƙueer Theory), aka yi matsaya cewa ba abin ƙyama ne ko mamaki ba, don an tsinci labarin sata ko ma na
kowaɗanne
lalatattun lamurra cikin taskar adabin Hausa, muddin ba a iya raba al’umma da ɗabi’un. Saboda haka, takardar ta bayyana matsayin sata a
idon Bahaushe, sannan aka nuna hoton sata a labarin Idon Matambayi, tare da ƙwanƙwance
yadda makomar ɓarayi a
cikin labarin ta kasance, aka kuma jaddada makomar tasu a matsayin hujjar da ta
fayyace kasancewar sata abar ƙyama a
al’ummar Hausawa. Sai aka yi matsaya a kan cewa Malam Muhammadu Gwarzo ya
rubuta labarin ne domin ya nuna irin dabaru da nau’o’in sata a wancan lokacin saboda
al’umma ta faɗaku, ta
kiyaye, ta rungumi tafarkin neman na kai, maimakon satar gumin wani.
Keɓaɓun
Kalmomi:
Sata, Labari, Lalatattun Lamurra, Idon Matambayi
1.0
Gabatarwa
Idon Matambayi na Muhammadu Gwarzo ɗaya
ne daga cikin littattafan da suka zamo ‘ya’yan fari cikin taskar rubutaccen
labarin Hausa waɗanda suka wanzu sakamakon gasar da
Hukumar Fassara ta shirya a shekarar 1933, aka kuma buga a shekarar 1934[1]. Tsawon shekaru 85 da
wannan littafi ya yi a doron ƙasa
(1934-2019), bai sami tagomashin da takwarorinsa[2] suka samu ba a fagen
nazari da sharhi. Hakan ba ya rasa nasaba da kasancewar littafin ƙunshe da labarin sata da
dabarun sata irin ta zamanin da aka rubuta labarin, ita kuwa sata ɗabi’a
ce abar ƙyama
a al’ummar Hausawa jiya da yau. Ta yiwu kuma ana kallon rashin dacewar fitowar
wannan nau’in labari daga malami kamar Muhammadu Gwarzo[3]. To amma ba a nan gizo ke
saƙar
ba, a koda yaushe marubuci ya yi rubutunsa, rubutun ba ya rasa nasaba da
abubuwa uku; ko dai abin da ke jini da gado ko abin da marubucin ya ji ko ya
gani ko kuma abin da ya ci karo da shi a zamantakewarsa ta yau da kullum, (Malumfashi,
2018:13-20). Saboda haka, ba abin mamaki ba ne idan an ci karo da labarin sata
ko luwaɗi ko batsa ko caca ko duk wasu lalatattun lamurra daga
taskar malami, mutumin kirki ko akasin haka, bai kuma zama abin ƙyama ba a fagen nazari,
domin hoto ne na yadda wani ɓangare na al’ummar yake. Shi ya sa ma
a ra’in adabi, babu wani adabi mai kyau ko maras kyau, sai dai a inda aka sanya
son rai ko kuma ra’ayi na mai nazari. Hakan ba yana nufin cewa ba za a iya
samun rubutu ingantacce ko waƙa
tasarriya ko ƙayataccen
wasan kwaikwayo ko makamantan haka ba, sai dai ana yaba kyawun adabi, ana kuma
yin yabon ne bisa wasu matattakalai da aka gindaya a cikin ra’in domin a
bambanta tsakanin adabin da ke shiga zuci, cike da zaƙin saurare ko karantawa ko
kuma kallo da kuma wanda yake lami (Eagleton, 1983).
Da yake adabi ‘hoto’ ne ko
‘madubi’, kuma mun san hoto ko madubi ba sa ƙarya, wato abin da ka hango
a madubi, shi ne kake ƙaraswa,
haka abin da hoton da ke gabanka ya nuna maka, haka abin yake a zahiri. Ashe kuwa
idan ka yaga hoto don rashin jin daɗin abin da ka gani, ko ka
fasa madubi domin ba ka son ganin abin da ka gani a ciki, ba zai canza lamarin
ba. (Malumfashi, 2012). Saboda haka, abin da labarin Idon Matambayi ya ƙunsa
ba abin ƙyama
ba ne a fagen nazari, duk kuwa da cewa sata abar ƙyama ce a rayuwar Bahaushe,
kamar dai yadda ra’in lalatattun lamurra (Ƙueer Theory)[4], da suka haɗa
da sata da luwaɗi da maɗigo da batsa da bore da
sauransu ke nunawa, wato fito da hoton irin waɗannan lamurra da yadda suke
a cikin al’umma. Wannan ya ba mu damar yi wa labarin Idon Matambayi dubar ƙwarƙwata domin fito da hoton
sata cikin labarin, ko ba komai, babu wani adabi karkatacce, illa yanayin adabi
yanayin al’umma.
2.0 Ra’in
Lalatattun Lamura (Ƙueer
Theory)
Ra’in Lalatattun Lamura ya haɗa abubuwa mabambanta a wuri guda. Da farko, akwai masu neman maza (homoseɗual) sannan akwai ‘yan maɗigo (lesbianisms) da kuma sauran
abubuwa irin su Sata batsa da karuwanci da tsafi da bore da sauran al’amura. Wannan ra’i ya tsiru ne daga ra’in
matantaka (feminisms) wato masu rajin kare ‘yancin mata. Bayan boren Stonewall
a Newyork (1969) inda aka samu haɗuwar
mata ‘yan maɗigo da maza
‘yan luwaɗi a wannan
lokacin wani ɓangare na
masu neman ‘yancin mata suka haɗu
da maza ‘yan luwaɗi
(Plain Da Sellers, 2007:183) domin tabba tar da wannan tunani.
Wasu
masana kuma irin su Ado (2017) sun bayyana cewa wannan ra’i ya tsiru ne daga
ra’in Fanɗarewar daga Keɓaɓɓun Al’adun Al’umma (Deɓine Theory) in da ya bayyana cewa wani bature mai suna
Geoffry Leach ne ya fara batun ra’in Fanɗarewa
a wajen nazarin harshe da adabi a shekarar 1969.
Wannan
rai’i bai samu zama da gindin sa ba sai a 1990 bayan wata mujalla mai suna “A Jornal of Feminist cultural studies”
ta fitar da rahoton taron da aka yi Jami’ar Calfornia mai taken “Special Issue of Differences. Bayan
fitar wannan rahoton a watan Fabarairu na 1990 sai aka samu rubuce-rubuce na
samuwar wannan ra’i daga Lauren Berlant Gloria Anzaldua da Eɓe Kosofsky Sedgwick da kuma Judith
Butler. Waɗannan su ne waɗanda suka ƙirƙiri wannan mazahabar a matsayin hanyar nazarin wani
matanin adabi. A taƙaice dai an ƙirƙire ta ne a 1990.
Tun bayan taron Jami’ar Calfonia wannan ra’i ya ci gaba
da watsuwa an samu marubuta irin su, Annamarie Jagose wanda ya rubuta littafin Ƙueer theory: An Introduction in (1997) bayan shi kuma sai Janik Bastien- Charlebois
wanda ya ruba ta wani littafi mai suna Realities
of the Interseɗ eɗperience. Daga nan marubuta irin su
Mathew Lewis da Lorda Byron da Walf Whitman da Katherine Mansfield da sauransu
da dama suka yi rubuce-rubuce kan wannan ra’i.
A yankin Afirka wannan ra’i ya samu bunƙasuwa ta hannun ‘Yan Afirka
da suka je ƙasashen
Turai suka koyo waɗansu munanan ɗabi’u. Marubuta irin su
Maddy mai littafin No Past, No, Present
No Future (1973) da littafin Our
Sister Killjoy (1977) na Aidoo da Frantz Fanon mai littafin Black Skin, White Mask (1952) da Wale Soyinka wanda ya rubuta Interpreter (1965) da Dillibe Onyeama wanda ya rubuta littafin Seɗ is a Nigger’s Game (1976) da sauran su da dama duk sun samo ɓirɓishin
wannan tunani tun kafin ra’in ya zauna da gindinsa.
A ƙasar
Hausa Marubuta da dama sun yi rubuce-rubuce kan irin wannan ra’Iimisali
Littafin ‘Yartsana na Ibrahim Sheme
da Littafin Kyan Ɗan Maciji na Bilkisu Ahmad Funtua da
littafin Butulu na Auwal Anwar da
Littafin Tashin Hankali na Rahma
Abdulmajid da sauransu da dama. Wannan ra’i na da manufofi da dama da suka haɗa
da:
* Bayyanar da kalaman tayar da sha’awa
* Kare haƙƙin tsirarru
* Yin fito na fito da hukumomi
* Bayyanar da sha’awar jinsi
* Ƙarfafa
mabiya yin alfahari da aƙidunsu
* Bayyana manufofinsu fili
* Bijirewa tanade-tanaden addinai
* Barin tsarin al’ada da zamantakewar al’umma
*Neman ‘yancin aiwatar da alfasha da gurɓatattun
al’amurra da sauran su.
2.1 Dangantakar
Ra’in Da Wasu Ayyukan
Adabi
A fagen adabi babu maganar adabi mai
kyau ko marasa kyau, sai dai a yi duba kan abin da al’umma ke kallon nau’in
adabin, domin shi aikin adabi abu ne da ke kallon yadda al’umma suke gudanar da
rayuwarsu, saboda haka duk yadda ya zo wajibi ne a karɓe shi, sai dai a fagen nazari ne kawai aka iya rarrabewa,
tsakanin ɗanɗanon wannan da wannan.
Irin alaƙar da adabi ya ke da shi da al’ada shi ya sa wasu ke yiwa wasu ayyukan
adabi kallon lallatattun ko kuma fanɗarraru, amma a zahiri ba lallatattun ba ne ba kuma fanɗararrun ba ne, domin in aka yi duba kan manufofi na ra’in
lalatattun lamura ba wai ya ta fi ba ne kai tsaye kan yadda za a riƙa aiwatar da ɓanna a cikin al’umma.
Malumfashi (2013) ya rawaito cewa,
“daga binciken da na yi kan wanna fanni sai na fahimci cewa yawancin irin
wannan adabi, na batsa ne ko na sata ko na karuwanci ko na daudanci ko na bore
ko na tashin hankali, ana ɗaukar sa
a matsayin karkataccen adabi, shi ya sa nakan tambayi kaina, Wa ko Me ya
karkatar da shi, amsar da nakan ba kaina ita ce ba wanda ya karkatar da irin
wannan adabi face al’umma da ya samu kansa a ciki, domin ita ce ta samar da
yabanyar da adabin ya rayu cikinta, ba wannan ba ma ai muna sane da cewa ita
kan ta al’ummar ai kala biyu ce, ko dai wadda ke tafiya da rayuwar masu danniya
ko kuma wadda ke janye da karikitan waɗanda ake dannewa. A
cikin wannan zubin rayuwa guda biyu ake samun adabawa da ke riƙe da kowane hannun riga
guda.”
Shi ma Ado (2017) ya bayyana cewa fanɗarewa
iri biyu ce akwai mai amfani akwai kuma marasa amfani, ya danganta da yadda
marubuci ko kuma al’umma suka kalleta.
Za mu kalli wasu daga cikin manufofin wannan ra’i waɗanda
suka yi daidai da binciken da aka gudanar kan littafin Idon Matambayi domin mu nazarce su muga yadda suka
yi alaƙa da
wannan aiki da kuma in da suka shafe shi.
3.0
Muhammadu
Gwarzo Da Littafin Idon Matambayi[5]
An haifi Muhammadu Gwarzo a
shekarar 1911 a gundumar Gwarzo da ke jihar Kano a yanzu. Ya yi karatu a Makarantar
Lardin Kano daga shekarar 1923 zuwa 1928, daga nan ya wuce Kwalejin Horar Da
Malamai ta Katsina ya kammala a shekarar 1932. Ya yi ayyuka da hukumar En-e ta
Kano waɗanda suka haɗa da malanta da jami’in
lantarki da samar da ruwa da sauransu, ya kuma yi aiki a sashen ayyukan al’umma
na hukumar En-e ta Kano da kuma Makarantar Midil ta Kano daga shekarar 1939,
inda ya kai matsayin hedimasta daga shekarar 1948 zuwa 1952. Haka kuma, ya zama
jami’in yaƙi
da jahilci da jami’in ma’aikata a hukumar En-e ta Kano da cibiyar mulki, ya
kuma yi wakilin tsare-tsare da horarwa daga baya kuma ya zama kwamishina na
dindindin a ma’aikatar ƙananan
hukumomi ta jihar Kano daga 1975 zuwa 1980, (Hassan, 2014). Malam
Muhammadu Gwarzo ya zama ɗan majalisar wakilai ta tarayya mai
wakiltar mazaɓar Ƙaraye
daga 1959 zuwa 1966. Ya zama shugaban hukumar bayar da tallafin karatu ta jihar
Kano daga shekarar 1970 zuwa 1975. Har ilau yau, ya kasance cikin majalisar
gudanarwa na Jami’ar Ibadan da Jami’ar Benin a lokaci guda. Yawancin ɗalibansa
sun riƙe
muhimman muƙamai
a ma’aikatun gwamnati da masu zaman kansu a ƙasar Nijeriya, (Hassan, 2014).
Kenan, Muhammadu Gwarzo malami ne, ma’aikacin gwamnati ne, kuma ɗan
siyasa ne.
Muhammadu Gwarzo shi ne
marubucin littafin Idon Matambayi, wanda
ya zo na huɗu a gasar 1933 da aka buga a shekarar 1934.
3.1
Warwarar Labarin Idon Matambayi
An gina labarin ne a kan
wani kyakkyawan saurayi mai suna Idon Matambayi, wanda ya kasance ƙaƙƙarfa kuma Allah ya hore
masa gudu kamar zomo. Ko da Idon Matambayi ya soma tasawa, sai ya shiga ‘yan ɗauke-ɗauke,
har ya addabi maƙwafta.
Duk da ba su iya yi masa komai saboda suna jin nauyin mahaifinsa, har sai da mahaifin
nasa ya sami labarin halin da ɗan nasa yake ciki. Shi kuwa mahaifin
ya ce Idon Matambayi ya tattara kayansa ya bar masa gida. Dama abin da yake so
kenan, sai kawai ya kama gabansa.
Marubucin ya kitsa labarin
nasa ne da nuna yadda Idon Matambayi ya tafi wajen boka don neman asirin da zai
fi ƙarfin
jama’a a kan abin hannunsu bayan da aka kore shi daga gida. Daga nan sai ya
zarce kasuwa inda ya kwashe kuɗin mutane ya arce daji da zummar cigaba
da sana’arsa ta sata. A nan ne ya haɗu da wasu mutane biyu, Ɗauke da Ƙwace suka ƙulla zumunta bayan sun gane
duk sana’arsu guda suka shiga aikata sace-sace a daji da birane. Su waɗannan
samari wato Ɗauke
da Ƙwace
sun daɗe
suna sata, har ma suna da wani gida a kogon dutse cikin surƙuƙin dajin da suke kira
Sauke-mu-raba.
Daga bisani kuma wannan
tawaga ta haɗu da wani mutum wanda shi ma ɓarawon ne mai suna Batsokana suka cigaba
da tafka ta’asa ta sata a cikin gari da daji ta amfani da dabaru mabambanta. Ta
haka ne har suka je wani gari mai suna Kafi suka yi sata a gidan wani attajiri
mai suna Musa bayan sun kashe Sarkin Gadi. Sarkin Kafi ya sa aka shirya mutane
don su farauto ɓarayin da ke wannan sace-sace, kuma
aka kama Ƙwace
da Ɗauke
da Batsokana, shi kuwa Idon Matambayi ya gudu ya koma ƙauyensu inda ya tarar
mahaifinsa ya riga ya rasu, sai ya je gaban sarkin garin ya rantse cewa ya tuba
da sata. Amma duk da haka, bai fi wata guda ba sai gobara ta tashi a maƙwafta da tsakar rana, ta ƙone gidan su Idon
Matambayi, kayansa da dukiyar da ya tara duk suka ƙone ƙurmus. Duk labarin an gina
shi ne a garin Kafi da Dajin Sauke-mu-raba da kuma garin su Idon Matambayi inda
aka ƙulla
labarin a farkonsa kuma aka warware a ƙarshe.
4.0
Sata a Idon Bahaushe
Sata ita ce ƙoƙarin mallakar wani abu
mallakar wani ko more wa gallonsa ta fuskar wayo da dabara ko nuna ƙarfi ko makami ko yaudara
irin ta zamba cikin aminci. Maƙasudin
sata a more wa abin da aka sata ba tare da an wahalar da jiki ko tunani ba.
Saboda haka, babban muradin kowane gogaggen ɓarawo shi ne biyan buƙatarsa ta wannan ɗan
lokaci ya amfana da abin da ya sato ko ya amfanar da wanda ya so a lokacin da
ya so (Bunza,
2010). Masana al’ada sun bayyana cewa, sata takan iya zamewa ciwo a wajen mai
yin ta, ta yadda in har bai yi satar ba, ba ya samun kwanciyar hankali. Shi ya
sa ma suka fayyace fuskokin da ake gane ciwon sata a al’adance da suka haɗa
da; gado wajen uwa ko uba ko kaka a zuriya, ko kuma a yi wa mutum makaru wato
jifa, idan bai ci nasara a kansa ba ya faɗa kan iyalansa. Kuma akan
ci karo da ita a bisa ƙaddara
ko kuma a jefi wasu fitattun ɓarayi su kamu da ciwon sata, su mutu
cikin lalurar. Har ila yau, bakin iyaye ko magabata na kama taƙadari ko maras kunya ko
maras ladabi ko maciyin zarafin mutane ya kamu da ciwon sata. A wani lokacin
kuma, idan aka yi wa yaro hatimin fahami ya sha, in bai samu karatu ba ƙarshe ya zama mawaƙi ko ɓarawo
(Bunza, 2010).
Daga abin da ya gabata, za
mu iya tsinkayar cewa labarin Idon
Matambayi ya nuna mana kwatankwacin hoton rashin bin iyaye da taƙadarci da cin zarafin
mutane a matsayin dalilin kamuwa da ciwon satar da Idon Matambayi ya yi cikin
labarin, shi kuwa ra’in lalatattun lamurra ya fito mana da hoton sarari, amma
da yake sata abar ƙyama
ce a wurin Bahaushe, sai ƙarshen
labarin ya nuna mana duk dukiyar da Idon Matambayi ya tara a fafutukarsa ta
sata ya rasa ta sakamakon gobara. Abin da za mu yi a nan shi ne bin ba’asin
wannan lamari a gaɓa ta gaba.
5.0
Nazarin Ra’in Lalatattun Lamura a Littafin Idon
Matambayi
Nazarin ra’i a cikin kowane
irin aikin adabi
yanayi na nuna tsarin labari wanda ya kan
jero manufofi ko kuma siga ta yadda aka gudanar da adabin.
A cikin litattafan Hausa akwai masu wannan yanayi, na lallatattun lamurra
wanda suka ƙunshi sata ko fashi ko madigo ko luwaɗi da sauran wasu abubuwa makamanta
waɗannan.
An dai yi nazarin
littafi mai suna Idon Matambayi a wannan
maƙala domin fito da misalin yadda wannan ra’i yake wanzuwa
a cikin litattafan Hausa da kuma irin yadda yake samun gindin zama a adabin
Hausa.
5.1 Dacewar
Ra’in da Littafin Idon Matambayi
Wannnan
littafin ya fito da manufofin ra’in lallatattun lamurra ta sigar bore da tayar
da hankali, haka kuma wasu daga cikin manufofin wannan ra’i sun yi matuƙar dacewa da wannan littafin waɗannan manufofin da suka dace da
littafin sun haɗa da:
* Yin fito na fito da hukumomi
* Bayyana manufofinsu fili
* Bijirewa tanade-tanaden
addinai
* Barin tsarin al’ada da
zamantakewar al’umma
Waɗannan su
ne wasu daga cikin manufofin wannan ra’i da suka bayyana a cikin wannan fim ɗin
karara, bari mu ɗauke su ɗaya bayan ɗaya domin gani dacewar su a cikin fim ɗin.
5.2 Hoton
Sata a Littafin Idon Matambayi
Idan aka
yi la’akari da yadda rayuwar Idon Matambayi ta kasance a cikin labarin Idon Matambayi, za a iya cewa, tauraron
ya kamu da ciwon sata ne sakamakon bakin iyaye da magabata maƙwafta da ya addaba da sace-sace tun tasowarsa. Tun a
farkon labarin an nuna yadda Idon Matambayi ya ɓata wayonsa tun a ƙuruciya
ta hanyar jefa kansa cikin sace-sace, har ya addabi maƙwafta duk da suna jin nauyin mahaifinsa sun kasa sanar da shi, har sai da
mahaifin ya ji labarin. Jin
wannan labari ya fusata mahaifin nasa har ya kore shi daga gidansa:
“Ana
nan ubansa ya ji labarin abin da yake yi, sai ya sa yaronsa ya je ya kirawo
shi. Da zuwansa ubansa ya ce, “Tattara ‘yan kayanka duka, yau ka bar mini
gidana. Na yarda ka, kada wata rana ka je ka jawo mini abin da ya fi ƙarfina.” (IM, shf na 1)
Ana iya cewa tun daga wannan baki ne sata ta
zame wa Idon Matambayi ciwo har ya zama gawurtaccen ɓarawo duk da cewa tun
tasowarsa yake ‘yan ƙananan
sace-sace a gida da maƙwafta.
Ta ɓangaren
abokan sana’arsa ta sata kuwa, wato Ɗauke da Ƙwace, su ma kamar yadda
suka faɗa da bakinsu a lokacin da Idon Matambayi ya kawo shawarar
su bar sata tun da burinsu na tara dukiya ya cika tun bayan da suka yi sata a
gidan Musa a garin Kafi, Ɗauke
ya ce:
“….Amma
dai ga zancen barin sata da ka ce, ni tun ina yaro da ita na buɗe ido, cikin dukan sana’o’i ban san ko
ɗaya ba. Ka kuwa sani mai
hali ba ya bari, ko na ce na bar sata, ƙarya nake yi.” (IM, shf na 54).
Shi ma ɗan’uwansu,
wato Ƙwace
ko da buɗe bakinsa cewa ya yi kamar ciki ɗaya suka fito da Ɗauke, don haka batun su bar
sata ba ta ma taso ba. Wannan ya nuna ƙarara cewa sata a wajensu ta zama ciwo
wanda ya yi masu katutu tun ƙuruciya.
Labarin Idon Matambayi ɗamfare yake da sace-sace da
dabarun da ɓarayi kan bi wajen yin sata musamman a zamanin da. Hausawa
sun yarda cewa dabara ko wayo ba ga kowa ake samun su ba, shi ya sa sukan ce;
“dabara ta fi ƙarfi”,
wato mai dabara ya zarce mai ƙarfi.
Babu shakka, a rayuwar Hausawa mai dabara ko hikima mutum ne mai ƙima. Amma Hausawa kan ɗauki
duk wani mutum mai dabara ko wayo a matsayin wani wanda ba nagari ba; wai wayo
ko dabara idan sun yi yawa cuta ne, (Jibril, 2014: 124).
Da yake littafin Idon Matambayi ya ƙunshi labarin sace-sace ne,
kenan dole a sami dabara ko wayo a cikinsa. Domin Bahaushe a rayuwarsa yana
kallon wayo a matsayin sata ne, wato ɓarawo kullum dabara yake yi
don ya raba mutum da kayansa. Wannan ne ma ya sa Hausawa kan ce; “Mai son
abinka ya fi ka dabara.” A wannan nazari, an lura da hoton sace-sace cikin
littafin Idon Matambayi a wurare da
dama kamar haka:
5.2.1
Wubce/ Ƙwace
Ƙawace nau’in sata ne da za
a fizge abin mai abu a hannunsa a gudu ko a tsaya a yi artabu, Bunza, 2016:43).
Irin wannan satar ta fito a labarin Idon
Matambayi a lokacin da ya yi sata a kasuwar garinsu a shafi na 2:
“Da
fitar Idon Matambayi gidan boka ya tafi tiran-tiran bai dire ba sai a kasuwa,
har inda aka zuba kuɗin cinikin
hajja a kan tabarma, ya laɓaɓo kamar wanda zai sayi wani turmin
sanda. Wuf! Ya duntse tsabar kuɗi sule-sule ya sheƙa a guje, ana bin sa ana ku
tare ku tare. Shi kuma yana kutsawa cikin mutane yana cewa ku tare ku tare, don
kada a kama shi. Da dai ya sami ɗam
fili ya rankaɗa da gudu, ya
yi maza ya faɗa wani gida,
daga nan kuma ya faɗa wani. Ya yi
ta yin haka har kafin a jima an rasa inda yake takamaimai, aka gaji aka ƙyale shi.” (IM, shf na 2).
Dabarar ƙwace kuwa ta fito ƙarara a
inda Ƙwace yake shaida wa Idon Matambayi dalilin wannan sunan
nasa ‘Ƙwace’ cewa ba komai ba ne dalilin sanya masa suna Ƙwace ba, sai don yakan gamu da mutum da kayansa ya ƙwace ya tsere a guje. (IM, shf na 5-6).
5.2.2 Fashi
Fashi na nufin amfani da
makami domin a karɓi dukiya a hannun mai ita. A labarin
Idon Matambayi mun ga hoton fashi tun daga lokacin da Idon Matambayi ya ƙulla alaƙa da su Ƙwace da Ɗauke inda bayan sun koma
masaukinsu sun huta suka yanke shawarar fita domin yin fashi a kan hanya. Ai
kuwa hakan aka yi, ko da Idon Matambayi da Ƙwace suka fita daidai inda
suka saba laɓewa da ɗan’uwansa Ɗauke su tsimayi masu wucewa
har su yi masu fashi, Ƙwace
ya shaida wa Idon Matambayi cewa:
“….Ka
ga wurin nan yau kusan shekararmu guda kenan muke fashi, ba ranar da kuwa ba mu
samun wani abu. Gama saboda sanin ba ma rabo da nan har idan mun ce wa matafiyi
ya ba mu abu kaza, maza-maza, yakan ba mu, jikinsa na rawa.” (IM, shf na 8).
5.2.3 Sane
Sane nau’in sata ne ta
hanyar yankan aljihu ko saka hannu a aljihun mutum a sace masa kuɗi
cikin dabara. Irin wannan nau’in satar ta fito a labarin Idon Matambayi, alal misali, inda Ɗauke ya shiga gari domin
duba masu inda ya dace su leƙa
su yi sata da dare shi da abokansa, wato Idon Matambayi da Ƙwace. Bayan dawowarsa ne
yake ba ‘yan’uwan nasa labari cewa:
“…Da
shiga ta kasuwa na kama hanya har wurin ‘yan tsire, na je na sayi na sisi. Mai
tsire ya zare ya ƙunshe
mini a takarda. Na karɓa dai kenan
sai wani mutum ya wuce ta gabana, ga aljihun kaftaninsa da ɗan tudu, na ga kuwa lalle tudun nan ba
banza ba. Na yi ta bin sa duk inda ya yi, har muka shiga cikin runtsin mutane.
Na zo na goge shi kamar wanda zai wuce, na duƙa kaɗan
na sa hannu a cikin aljihun kaftanin, na sami jaka na ɗauke,
ashe da kuɗi a ciki.
Lokacin da na ɗauke kuɗin ashe wani mutum yana kallona, da
ciro jakar sai ya buga mini kururuwa, “Ɓarawo! Ɓarawo!” Kasuwa ta yi caa a kaina. Da
na ga haka sai na tuna da guduna. Da dai na sami wani ɗam
fili tsakanin mutane sai na sheƙa
a guje, mutanen kasuwa kuma sai kallo da sallallami.” (IM, shf na 16).
Wannan ya nuna ƙarara yadda sane yake cikin
nau’o’i da dabarun sata. Har ila yau, Ɗauke ya nuna cewa daga wannan dabara
ta sane ne ya samo sunansa ‘Ɗauke’,
wato duk inda mutum ya sa kuɗinsa yana iya ɗaukowa ko da ƙarfi ko da wayo. (IM, Shf
na 6).
5.2.4 Shiga a Ɗauko
A irin wannan satar ɓarawo
kan fasa ko ya buɗe gida ne ko ɗaki ko shago ko wata
ma’ajiyar dukiya, ya shiga ya yi sata, (Bunza 2016:43). Irin wannan sata ta
fito ƙarara
a labarin Idon Matambayi. Misali, inda
Ɗauke
ya rasa ta yadda zai yi sata a garin Kafi, sai kawai ya yi dabarar sanya wuta a
wani ɗaki
cikin wani gida. Da gobara ta tashi sai jama’a duk suka tafi kai ɗauki,
shi kuwa Ɗauke
sai ya sami damar yin satarsa yayin da jama’a ke ƙoƙarin kashe wuta:
“Da
jin ihun nan mutanen gida da maƙwafta
duk suka fito gudummawa. Waɗanda
suna jin tsoron kada wuta ta kama ɗakunansu,
suka yi ta fitad da kayansu a gigice. Da Ɗauke ya ga haka, sai ya fito ya riƙa kamar wanda ya zo
gudummawar wutar. Yana zazzagawa sai ya ga wani ɗan
kwatashi a ajiye, ya tafi ya jinjina sai ya ji shi da nauyi. Ya buɗe ya iske shi cike da kuɗi sule sule da fataka fataka, ya tara
rigarsa ya juye kuɗin ya yi
tafiyarsa.” IM, shf na 34).
Bugu da ƙari, a lokacin da su Idon
Matambayi da Ƙwace
da Ɗauke
da Batsokana suka je gidan attajiri Musa a matsayin fatake masu sayen goro,
domin su sami damar zama a gidan har su yi masa sata. Idon Matambayi da Ƙwace da Ɗauke sun sulale cikin dare
daga masaukinsu sun bar Batsokana, saboda sun ƙosa da abin da suka bayyana
a matsayin jan ƙafa
da yake yi kafin ya shirya masu dabarar da za su yi satar a gidan Musa. Saboda
haka sai suka haura gidan Musa su uku, suka shiga wani ɗaki da yake ɗamfare
da dukiya suka yi satarsu suka gudu suka bar Batsokana a gidan. (IM, shf na
43-51).
Ko shakka babu, wannan ya
fito da hoton nau’in satar da ake shiga gida ko ɗaki a ɗauko
abin da za a sata ta bin wasu dabaru don cim ma gaci.
Duk waɗannan
misalai sun nuna hoton nau’o’in satar da ɓarayi suke yi, musamman a
daidai zamanin da aka rubuta labarin (1933-1934), kuma za su taimaka wa al’umma
su fahimci yadda ɓarayin ke shirya dabarun sata domin a
nemi hanyar kiyayewa.
5.3 Ƙarshen
Alewa Ƙasa
Bahaushe ya aminta cewa
akwai cutar sata, amma al’adarsa ba ta yi na’am da sata ba, don haka sata ba
wata haja ba ce a ƙasar
Hausa, (Bunza, 2010). Saboda haka, shi ma marubucin
labarin Idon Matambayi bai nuna sata
tana da wani muhimmanci ba, shi ya sa ma aka nuna babban tauraron
labarin wato Idon Matambayi saurayi ne abin sha’awa ga kowa, amma ya ɓata
rayuwarsa da ɗabi’ar sace-sace, har ya haɗu da Ɗauke da Ƙwace da Batsokana, suka
zauna a dajin Sauke-mu-raba suka yi ta tafka sace-sace da fashi da makami, tun
bayan barowarsa gida sakamakon korar da mahaifinsa ya yi masa. Sai dai daga ƙarshe an nuna abin nan da
Bahaushe kan ce; “rana dubu ta ɓarawo, rana ɗaya
ta mai kaya”, inda aka kama sauran ɓarayin[6], shi kuma Idon Matambayi ya
gudu ya tuba, amma duk da haka sai da ya zama ba tsuntsu ba tarko.Wannan ya
nuna illar sata da rashin amfaninta.
A ƙarshen labarin, an nuna
cewa ranar da Idon Matambayi ya shiga garinsu ya iske mahaifinsa ya rasu,
washegari sarki ya sa aka kama shi aka ɗaure har kwana uku. Sannan
sarki ya ce muddin bai bar sata ba zai ɗaure shi rai-da-rai, a nan
Idon Matambayi ya tabbatar ya bar sata:
“Idon
Matambayi ya ce, “Ranka ya daɗe,
kada ka yi zancen ɗauri rai da
da rai, kai dai ka ce in tuba, na kuwa tuban. Da ma don na tuban ne shi ya sa
ka ga na komo garin nan. In kana shakka ka sa a kawo mini Alƙur’ani in rantse, ba zan ƙara sata ba.” (IM, shf na
60).
A nan sarki ya yafe masa,
kuma ya ce jama’a su yi wa mahaifinsa addu’a. Wannan ya nuna ƙarara cewa, a rayuwar
Hausawa sata abar ƙyama
ce.
Bugu da ƙari, saboda marubucin ya
jaddada hakan, a ƙarshen
labarin an ga yadda gobara ta ƙone
gidan su Idon Matambayi ta cinye duk kuɗin da ya samu a harkar sata.
Wannan shi ne ya zama kamar marufin labarin:
“Idon
Matambayi ya koma gidansu ya yi ta jin daɗi.
Bai yi wata guda da zuwa ba sai gobara ta tashi a kusa da gidansu da rana kata,
ta ƙone
gidan maƙwabtan
da na su Idon Matambayi, kayansa duk suka ƙone, kuɗinsa
suka lalace, ya koma ba wuri ba wurin zama.” (IM shf na 60).
Faruwar wannan gobara da ta
yi sanadiyyar ƙarewar
duk dukiyar da Idon Matambayi ya samu ta hanyar sata, ta tabbatar da irin
matsayin da sata take da shi a wajen Bahaushe, wato abar ƙyama ce, kuma duk irin
tarin dukiya ko alatun da aka tara ta hanyar sata ba abar toƙabo ba ce domin za ta waɗanɗane
tamkar lamarin da ake cewa ‘ƙarshen
alewa ƙasa.
6.0
Sakamakon Bincike
An gina
wannan bincike ne bisa manufar bayyana nau’o’in sata a idon Bahaushe tare da
fito da makomar mai aikata satar, duk a cikin labarin Idon Matambayi, ta amfani da ra’in lalatattun lamurra. Sakamakon
binciken ya gano cewa ra’in lalatattun lamurra yana hasko yadda lamurran suke
ne ta madubin adabi walau masu kyau ko munana domin yi wa nazari adalci. Shi ya
sa ra’in bai samu karɓuwa ba a
nazarce-nazarcen Hausa da ma galibin adabin Afirka saboda kallon da ake yi wa
lamurran sata da karuwanci da luwaɗi da maɗigo da
sauransu a matsayin baƙin lamurra da
Turawa suka zo da su kuma al’adar mafi yawancin al’umomin Afirka musamman
Hausawa ba ta yi na’am da su ba. Sai dai babu wanda
zai yi musu cewa akwai masu aikata luwaɗi
da maɗigo da karuwanci da sata da sauran miyagun ɗabi’u
a cikin al’ummar Hausawa. Don haka wannan takarda ta jaddada cewa bai zama abar
ƙyama
ba a fagen nazari, don an tsinci irin waɗannan miyagun ɗabi’u
a cikin adabin al’umma, ko da kuwa adibin ba ya aikata su[7]. Idan kuwa haka ne (kuma hakan ne), littafin Idon Matambayi na Muhammadu Gwarzo duk da yana kimshe da labarin
sace-sace da dabarun sata (waɗanda ababen ƙyama ne a al’adar Hausawa), ba zai rasa
abin tsinta a ciki ba ta fuskar nazari. Haka kuma, nazarin ya gano cewa ba sata
ko dabarun sata Muhammadu Gwarzo ya yi nufin koya wa al’umma ba, illa nuna
illolin sata da rashin amfaninta, sai kuma abin da ya shafi illar bijire wa
iyaye da muhimmancin neman na kai, duk a cikin littafinsa na Idon Matambayi.
7.0
Shawarwari
Hanyoyin
samar da labari ko wane iri ne, musamman na adabi ba sa rasa nasaba da rayuwar
yau da kullum. Shi ya sa a kowane matani aka duba, ba a rasa wani abu ko dai
daga jini ko gado ko abin da aka ji ko aka gani, ko kuma abin da zamantakewa ta
haifar. Saboda haka, abin da ke da muhimmanci a nazari shi ne fito da batutuwa
yadda suke, domin fasalta yadda al’umma take. Haka ne, za a fahimci yadda
al’umma take kallon kowane al’amari cikinta. Shi ya sa kamar yadda a wannan
nazari aka fito da hoton sata a labarin Idon
Matambayi, an kuma fayyace yadda al’ummar Hausawa suka ƙyamaci satar da kuma nuna irin makomar da mai aikata
satar ke ƙarewa. Don haka, shawara ga manazarta ita ce, babu wani
adabi karkatacce, sai dai kowane matani yana hasko hoton wata aukuwa ce cikin
al’umma. Ke nan, fito da ire-iren waɗannan batutuwan tare da fayyace
yadda al’umma take
kallon su da kuma yadda za a magance su, shi ne ke da muhimmanci, ba wai ƙyamatar nazarin su ba.
8.0
Kammalawa
Ƙoƙarin jaddada jituwar ra’in lalatattun lamurra da wasu nau’o’in adabin Hausa ya sa aka
daddagi littafin Idon
Matambayi na Muhammadu Gwarzo, aka yi masa
dubar ƙwarƙwata tare da tsokaci kan
hoton sata da dabarun sata a labarin. Sai
dai ko kafin nan, an waiwayi bayanin ra’in da kuma dacewarsa a wannan
nazari, sai kuma aka daddagi matsayin sata a idon Bahaushe ta yadda aka fayyace yadda ciwon
sata yake da kuma yadda ake kallon sata da mai aikata ta cikin al’ummar Hausawa.
Manazarta
Bunza, A.M. (2010). “Ciwon
Sata A Al’adar Bahaushe.” Cikin Funtua, A.I da Gusau, S.M.(ed). Al’adu Da Ɗabi’un Hausawa da Fulani. Kaduna: El-Abbas Printers
and Media Concepts.
Bunza, A.M. (2016). In Ba Ka San Gari Ba Saurari Daka: Muryar
Nazari Cikin Tafashen Cairo: ElKods Printing House.
Eagleton, T. (1983). Literary Theory: An Introduction. Oɗford:
Blackwell.Gwarzo, M. S. (1934). Idon
Matambayi. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company Limited.
Hassan, M.B. (2014). “Brief
Biography of the Early Indigenous Hausa Noɓelists.” In Gusau,
S.M. et- al (ed).Garkuwan Adabin Hausa: A Festchrift in
Tribute to Abdulƙadir
Ɗangambo. Department of Nigerian
Languages, Faculty of Arts and Islamic Studies, Bayero University, Kano. Zaria:
Ahmadu Bello University Press Limited.
Jibril, M.S.(2014).“Rayuwar
Hausawa Daga Littattafan Gasar Labaran Hausa Na Shekarar 1933:
Nazari Kan Littattafan Jiki Magayi Da Ganɗoki Da Idon Matambayi.” Kundin Digiri Na Ɗaya. Sashen Harsunan
Nijeriya Da Kimiyyar Harsuna. Kaduna: Jami’ar Jihar Kaduna.
Maiyama, U.M (2001).
“Jirgin Sata Cikin Ƙagaggun
Labaran Hausa.” Kundin Digiri na Biyu. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Malumfashi, I. (2012). “Muhammadu
Gambo Mai Waƙar
Ɓarayi:
Tsakanin Tuba Da Adabi.”
Cikin Amfani, A.H. da
wasu(ed). Champion of Hausa Cikin Hausa:
A Festschrift in Honour of Ɗalhatu
Muhammad.
Zaria: Department of African Languages and Cultures, Ahmadu Bello University.
Malumfashi, I. (2018) (ed).
Labarin Hausa A Rubuce 1927-2018. Zaria:
Ahmadu Bello University Press and Publishers.
Olaniyan, T.
da Ƙuayson, A. (2007). African
Literature: An Anthology of Criticism and Theory. Melden
Blackwell Publishing.
[1] Gasar
1933 ita ce ta uku a tarihin rubutaccen labarin Hausa bayan ta 1927 da ta 1929
waɗanda duk ba a sami
buga sakamakonsu ba. Hukumar Fassara ƙarƙashin
jagorancin Dr. R.M East ta shirya gasar ne domin samar da littattafai da abin
karantawa don nishaɗi. Duba
Yahaya, 1988 da Malumfashi 2009 da 2018 domin ƙarin
haske.
[2]
Takwarorinsa su ne Ruwan Bagaja na
Malam Abubakar Kagara da Ganɗoki na Malam Bello
Kagara da Shaihu Umar na Malam
Abubakar Bauchi da Jiki Magayi na
East Da Tafida. Su kuwa Boka Buwaye
na Malam Nagwamatse da Yarima Abba na
Malam Jumare Zariya, ba a buga ba duk da sun sha yabo, ballantana ma a nazarta.
[3] Ta yiwu wannan shi ne dalilin da iyalansa
suka haramta bugawa da yaɗa
littafin, har hakan ta haifar da ɓacewarsa
tsawon lokaci.
[4] Ra’in lalatattun lamurra bai samu mazauni ba, a yawancin adabin Afrika. Kamar yadda (Olaniyan da Ƙuayson; 2007:726) suka bayyana maɗigo da luwaɗi da karuwanci da sata baƙin al’amura ne a nahiyar Afrika da Turawa suka kawo luwaɗi a tsakanin sojoji da fursunoni a gidajen yari da maɗigo a makarantun kwana na ‘yan mata, duk zuwan boko ne ya kawo shi.
[5] Duk da
kasancewar Idon Matambayi ɗaya daga cikin littattafan da suka
ciri tuta a gasar shekarar 1933, bai sami kulawa ta fuskar nazari kamar
takwarorinsa ba, wato Jiki Magayi da Shaihu Umar da Ruwan Bagaja da Ganɗoki waɗanda a mabambanta lokuta bisa
manufofi daban-daban an yi tarkensu an kuma baddala su zuwa wasan kwaikwayo,
wasu ma an fassara su zuwa Ingilishi. Shi kuwa Idon Matambayi har ɓacewa ma
ya yi, tsawon lokaci ba a jin ɗuriyarsa
daga bisani aka lalubo shi. Duk da haka, an sami wasu ayyuka da suka taɓo littafin kamar (Ahmed,
1982; Ahmed,
1987; Abdurra’uf, 1985;
Guga, 2001; Habibu, 1986; Ibrahim,
1987; Kabir, 1986; Lawal,
2006; Mukhtar, 2004; Malumfashi,
2009 da 2018; Turaki, 1987
da sauransu). Sai dai galibi waɗannan ayyuka ambaton
labarin Idon Matambayi kawai suka yi,
inda aka yi sharhin kuma bai taka kara ya karya ba.
In
ma an yin, ai bukin Magaji ba ya hana na Magajiya.
[6] Wato
abokan sana’arsa ta sata da ba su tuba ba, su Ɗauke da Ƙwace
da Batsokana.
[7] Shi ya sa aka taɓo bayanin matsayin jini da gado da ji da gani da kuma zamantakewa a ƙumshiyar adabi. Dubi Malumfashi (2018:13-20) domin ƙarin bayani.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.