Arc. Ahmad Musa Dangiwa Literary Foundation wadda take shirya gasar rubutun gajerun labarai na Hausa. A wannan shekarar gasar za ta maida hankali ne kan matsalolin barace-barace musamman ga ƙananan yara. A gasar ta bana ana buƙatar marubuta su fito da dalilan da ke kawo barace-barace, misali dalilai na tattalin arziƙi da matsalar tsaro da al'adu da rashin fahimtar addini da yanayin zamantakewa da yadda matsalolin barace-barace kan yi tasiri ga cigaban al'ummar ta fuskokin da aka ambata. Cikin salo na ayyanawa za a buƙaci marubutan da su fito da matsalar yadda za a iya fahimtarta. Gasar ta bada dama ga dukkan marubuta maza da mata, tsofaffi da sababbi, har ma da masu sha’awar fara rubutu matuƙar za su kiyaye ƙa’idojin da aka tsara.
MAUDU’IN GASAR
1. Kalubale da Matsalolin
Yawaitar Barace-Barace Musamman na Ƙanana Yara a Ƙasar Hausa.
MANUFOFIN GASAR
1. Ƙarfafa marubuta su yi nazari da zurfafa
tunani kan matsalar yawaitar barace-barace da tasirinta a rayuwar al’umma.
2. Tattauna dalilai da sakamakon
zamantakewa da tattalin arziƙi da tsaro da ke tattare da wannan
matsala, musamman ga ƙanana yara.
3. Ƙirƙirar mafita ta hanyar rubutu, wacce za ta
iya taimaka wa gwamnati da kungiyoyi wajen rage wannan matsala.
4. Gina hangen nesa tsakanin
marubuta da masu aikin jinƙai, hukumomi, da kungiyoyin tallafi domin samun haɗin gwiwa wajen magance
barace-barace.
5. Ƙarfafa basira da ƙwarewa ta fuskar rubutun
gajerun labarai a kan muhimman batutuwan yau da kullum.
6. Fito da tasirin barace-baracen
ga ƙananan
yara musamman wanda ya shafi kiwon lafiya, da ilimi da makomarsu gaba ɗaya.
TSARE-TSAREN SHIGA GASAR
1. Za a turo samfurin labari
cikin kalmomi 500 zuwa 1000 a wannan adireshin: dangiwaliterary2020@gmail.com.
daga ranar 15/1/2026-15/2/2026.
2. Za a tace a zaɓi labarai 20 mafi burgewa a
cikin kwanaki ashirin (16/2/2026 – 6/3/2026).
3. Za a gudanar da bita ta
musamman ga waɗanda
aka zaɓa, domin ƙara
fahimtar matsalar barace-barace, da fasahar rubutu mai jan hankali..a cikin
watan Maris
4. Bayan bitar za a bayar da wata
ɗaya ga marubutan
domin aiko cikakken labarinsu mai ɗauke
da kalmomi 3500 zuwa 4000.
5. Za a sanar da labarai sha
biyar da suka yi nasara a watan Mayu na 2026.
SHARUƊƊAN
SHIGA GASAR
1. Labarin ya zama na asali wanda
bai taɓa shiga wata
gasa ko bugawa a kafar watsa labarai ba.
2. A tabbatar da cewa labarin ya
ta’allaka kan matsalar barace-barace, musamman ta ƙanana yara, tare da
nazari a fuskar zamantakewa, tsaro, da tattalin arziƙi.
3. A rubuta da daidaitacciyar
Hausa tare da amfani da haruffa masu lanƙwasa (ɓ,
ɗ, ƙ, ‘y)
4. A aiko da labarin cikin tsarin
Microsoft Word ko PDF zuwa adireshin da aka bayar.
5. Mutane biyu za su iya haɗuwa su rubuta labari ɗaya.
6. Dole ne a turo labarin cikin
lokacin da aka ƙayyade.
7. Dukkan Labaran da suka kai
zagaye na ƙarshe
mallakin gasa, ba za a iya ɗaukarsu
domin shiga wata gasa ba.
7. Hukuncin alƙalan
gasa shi ne na ƙarshe ba za a tattauna wani abu ba bayansa.
KYAUTUTTUKA
1. Za a ba da kyaututtuka na
musamman ga labarai uku (3) da suka fi ƙayatarwa, da kuma labarai sha uku da suka
tsalleke zagayan ƙarshe.
2. Za a ba da takardun karramawa
ga marubutan da suka shiga gasar daga na 1 zuwa na 15. Sannan za a buga labaran
a cikin littafi guda da za a ƙaddamar a wani ƙwarya-ƙwaryan
taro da za a shirya a Katsina.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.