Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya ya gudana cikin nasara a ranar 31/12/2025 a garin Dutse jihar Jigawa, inda ya haɗa marubuta, manazarta, malamai, ɗalibai, da wakilan gwamnatoci daga sassa daban-daban na Nijeriya da maƙwabtanta. Taron ya ƙara jaddada muhimmancin rubutun Hausa a ƙarni na 21, musamman a fuskokin tsaro, tattalin arziki, al’adu, da ci gaban al’umma.
Muhimman Abubuwan da Taron ya
Tattauna
1. Ƙalubalen
Tsaro da Al’adar
Karatu:
An jaddada cewa duk da ƙalubalen
rashin tsaro, akwai babbar matsala ta raguwar al’adar karatu musamman a tsakanin matasa, wadda ke buƙatar
tsayuwar daka. An ba da shawarar a fara gyara tunani tun daga makarantu, ta
hanyar kafa kulob-kulob na karatu da al’adu,
tare da gayyatar marubuta su rika yi wa ɗalibai
bita kan muhimmancin rubutu da karanta littattafai.
Yadda za a yi amfani da fasahar
AI domin gina rubutu mai inganci da kuma sauƙaƙawa marubuta da amfanin hakan ta fuskar
tsaro da tattalin arziƙi.
2. Zaurukan Tattaunawa
(Panels):
“Rubutun Zube na Hausa a Onlayin:
Ina aka dosa?” inda masana suka tattauna muhimmanci da ƙalubalen rubuce-rubucen
onlayin, musamman matsalar rubutun batsa.
“Marubuta Mata a Jiya da Yau: Ina
aka dosa?”
“Rubutun Gajerun Labaran Hausa:
Ina aka fito? Ina ake? Ina aka dosa?”
"Tattaunawar waƙoƙin
Hausa."
"Rubutun Hausa a wajen ƙasar
Hausa"
Waɗannan
zauruka sun samar da ilimi mai zurfi da gogewa wadda ke da wahalar samuwa a
wuri guda.
3. Halarta da Wakilci:
Taron ya samu halartar marubuta
sama da 250 daga faɗin
Nijeriya, tare da wakilcin gwamnatocin Arewa musamman Kano, Katsina da Jigawa.
Haka kuma, an samu baƙi daga ƙasashen Togo, Kamaru, Senagal da Nijar.
Ƙalubale da Abubuwan da za a Gyara
An lura cewa Kwamitin Yaɗa Labarai na cikin gida bai
samu cikakkiyar dama ba wajen aiwatar da aikinsa kamar yadda ya kamata; an
yanke shawarar gyara wannan a taro na gaba.
An kuma fuskanci matsalar kayan
sauti a farkon taron, amma an shawo kanta; za a ɗauki
matakan da suka dace domin kauce wa irin haka a nan gaba.
Rashin daratta lokaci ga
marubuta, wanda hakan ya haddasa rasa abubuwa da yawa masu muhimmanci. Mutum ya
kwana a wajen taron kuma ta dalilin taron ya zo an fada masa za a fara taro
karfe 10 amma bai shigo dakin taro ba sai karfe 11:24 kuma yana maganar ba a
bashi damar karanta gajeren labari ba.
Abin da taron ya samar
Littafi mai ɗauke da gajerun labarai 27
kan gudunmuwar fasahar AI ga tsaro da tattalin arziƙi wanda aka ba suna
"Ninki Biyu".
Taron ya samu damar haifar da
taron horas wa kan sanin hanyoyi da dabarun yadda ake rubuta bukatar neman
daukar nauyin ko bayar da gudunmuwa daga ƙasashen waje, wadda za a zabi marubuta
daga jihohi da kuma malaman jami'a a koma Jigawa a karamar hukumar Kirikisamma
a lokacin bikin karamar Sallah mai zuwa in sha Allah. Wanda Kwamishina yaɗa labarai da matasa da
wasanni da al'adu na jihar Jigawa zai ɗauki
nauyi baki ɗaya za a
zabi marubuta da basu gaza 20 ba domin halartar wannan taro na bita.
Haka kuma ana kan tattaunawa mai
karfi tsakanin wakilan gwamnatin jihar Jigawa da Katsina da jamhuriyar Nijar
domin samar da wani bikin baje koli da marubuta zasu taka rawa da zai hada
Najeriya da Nijar In sha Allah.
Shugabanci da kuma Jihar da za
a yi taron 2026
Jagororin da suka shirya taron
bana wa'adinsu ya kare ne kan taron na bana, daga nan zuwa watan Afrilu ake sa
ran marubuta su zaɓi
waɗanda suke so su
jagoranci taron gaba.
Maganar jihar da za a yi taro ita
ma ana sa ran daga nan zuwa karshen watan Fabrairu masu buƙata su
nuna buƙatar
su tare da dalilan masu ƙarfi na iya ɗaukar
nauyin taron. Idan ba a samu wadanda suka nuna bukatarsu ba a rubuce, wannan
kwamitin kafin wa'adinsa ya ƙare a wata Afrilu zai bayyana jihar da za
a yi taron gaba tare da miƙa ragamar jagorancin ga wadanda marubuta suka zaɓa domin su jagorance su a
taron 2026.
Sannan kwamiti ya amince ya fara
raba takardar godiya ga wadanda suka bayar da gudunmawa a wannan taro daga
ranar Litinin 12/1/2026.
Shawarwarin
Ana bada shawara taro na gaba ya
zama na kwana biyu domin yin abubuwa da yawa masu muhimmanci.
Ana bayar da shawara ga wadanda
za su jagoranci taron gaba da su kiyaye ƙalubalen da aka samu a wannan taron.
Godiya da Yabo
Taron ya miƙa
godiya ta musamman ga dukkan kwamitoci bisa jajircewa da sadaukarwa. Ana
jinjina wa manyan malamai da marubuta da suka bayar da gudummawarsu na ganin an
yi wannan taro lafiya.
Haka kuma, ana jinjina ta
musamman ga wakilan Gwamnatin Jihar Jigawa ƙarƙashin jagorancin Sagir Ahmad Musa da muƙarraban
Gwamna Umar Namadi Danmodi, bisa irin goyon bayan da suka ba taron da kuma
gasar rubutun da suka saka.
Ana kuma yabawa wakilan Gwamnatin
Jihar Katsina bisa rawar da suka taka wajen inganta taron. Jihar Katsina ta
bayyana aniyarta na ɗaukar
nauyin taron na gaba, tare da ci gaba da tallafawa idan ba a samu wata jiha da
ta ɗauka ba.
Kammalawa
Taron ya tabbatar da cewa rubutun
Hausa ginshiƙi
ne na gina tunani, tsaro, da tattalin arziki, kuma dole ne a ƙara ƙaimi
wajen farfaɗo da
al’adar karatu da rubutu, musamman a tsakanin matasa. An amince da ɗaukar darussa daga ƙalubalen
da aka fuskanta domin ƙara inganta taruka na gaba.
An fitar da wannan sanarwa domin
amfanin al’umma da masu ruwa da tsaki.
Abdulrahma Aliyu PhD
A madadin kwamitin shirya
taron ranar marubuta Hausa ta Duniya 2025

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.