ALLAH WADARAN NAKA YA LALACE: SHARHIN TURKE DA SALON WAƘAR GUGUWAR SAUYI TA AMINU ABUBAKAR LADAN (ALAN WAƘA)
Daga
Dano Balarabe Bunza
Sashen Koyar Da
Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo,
Sakkwato
Lambar Waya:
07035141980
Ƙibɗau: danobunza@yahoo.com
Da
Muhammad Abubakar
Zabi
Sashen Nazarin
Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo,
Sakkwato
08136844199
muhammadabubakarzabi@gmail.com
2016
Tsakure
Siyasa dama ce da
jama’a ke samu ta walwala. A irin wannan lokaci ne ‘yan ƙasa ke samun sukunin
bayyana ra’ayoyinsu dangane da manufofin gwamnati da kuma yadda ake mulkinsu ba
tare da jin tsoro ba. Wakokin siyasa sun ginu ne bisa tarihi. Sun faro tun
lokacin jihadin mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo inda suke
yin amfani da su wajen yin kyamfen. Hausawa mutune ne masu sha’awar waƙa, duk lokacin da
wani sabon al’amarin siyasa na jam’iyya ya zo musu, sai su shiga waƙe shi a inda suke
bayyana yanaye-yanaye tsari da kuma sigoginsa. Ta wannan hanya ce ake riƙa tallata jam’iyyu da
‘yan takara ta hanyar bayyana manufofinsu da ƙudurorinsu ga jama’a.
A cikin wannan takarda za a dubi ma’anar wasu kalmomin da ke cikin takenta yadda
masana suka faɗa da kawo tarihin wanda
ya yi waƙar wato, Aminu Abubakar Ladan (Alan waƙa), sannan a waiwayi sharhin
waƙar
‘Guguwar Sauyi’ kan turakunta da salailan da ke cikinta. A ƙarshe, hanzari da
kammalawa za su biyo baya kafin manazartar takardar da za ta biyo baya.
1.0
Gabatarwa
12.
Jagora: An zaɓi ruɓa-ruɓa namu da sunan waƙiltar ka,
:A ba su kuɗi su miƙa mu hannu ƙwarya hannu bakka,
:Tunaninsu iyalinsu
su tara abin da ba tamka,
:Suna tsoron
talaucewa suna tsoron zama talaka,
:Sun zaɓi zama talakkawa a
ranar komuwa gunka.
Amshi: Baƙar malfa baƙar jarfa
Mai shanye jinin
jikin talaka
Allah kaɗa guguwar sauyi
Buhari Janar karab da
gari.
(Waƙar Guguwar Sauyi ta
Aminu Ladan Ala).
Al’ummar Nijeriya ta
ga salon mulki iri daban-daban kama daga na Turawan mulkin mallaka tun kafin
samun ‘yancin kai da na jamhuriyar farko na shekarar 1956 da na soja da kuma na
farar hula mai cike da ruɗu, wata rana kuma,
sai sojoji su karɓe. Haka aka ci gaba
da yi har aka sami wasu sojoji suka fara rikiɗa daga soja domin komawa farar hula
saboda irin mulkin da ke gudana a Nijeriya na halin ko-o-ho da wasu shugabanni
ke yi domin su ne masu yin hukunci sun fi ƙarfin a hukunta su.
Bugu da ƙari akwai dalilin ganin ba mai bakin magana sai shugaba.
Idan mutum ya ce uffan ba na goyon bayan gwamnati ba, ba shakka ya san tasa ta ƙare. Wannan ya faru
saboda wasu abubuwa da takardar za ta ambata nan gaba kaɗan. Marubucin/mawaƙin ya kai kukansa
tare da na ‘yan ƙasa nagari wajen Allah da roƙon ya zaɓa musu shuwagabanni
na kirki domin ‘yan ƙasa su sami sauƙi ga matsalolin da
suke fuskanta da ba sai an faɗa ba domin, na wata ƙasa ya san su balle ɗan Nijeriya. Takardar
za ta kawo sharhin saƙo/saƙonnin waƙar tare da salailan
da ke cikinta. Kafin komi za a dubi ma’anar kalmomin da ke cikin taken takardar
da ke buƙatar hakan ta yadda masana suka yi bayani. Ga su kamar
haka:
2.0 Ma’anar Wasu Kalmomin da ke Cikin Taken Takarda
Kalmomin na da dama
da yawansu zai hana mu ba kowace kalma nata kan labara sai dai a haɗe su ta hanyar kawo
bayanan dan masana suka faɗa dangane da su. Kalmomin guda bakwai ne aka hango da ke
son a ɗan dubi gurbin yadda
aka yi amfani da su a cikin waƙar da za a yi sharhi. Akwai kalmar wadaran da lalace da sharhi da turke da salo da guguwa da kuma sauyi.
Kalmar wadaran da
wadarai da wadai da waddai duk abu ɗaya suke nufi sai dai kowace da wurin da ake
amfani da ita dangane da Karin harshe. An nuna a dubi ɗaya daga cikinsu idan
ana neman ma’anar ɗaya. Wadarai a dubi
wadai, waddai a dubi wadai, ma’anar wadai it ace, la’ana, ko tsine wa wani (Ƙamusun Hausa
2006:464).
Kalmar lalace kuma,
an nuna a dubi kalmar lalata mai nufin ɓata wani abu. Haka ita kuma kalmar lalaci duk
‘yan gida ɗaya ne mai nufin
rashin kataɓus ko rashin kuzari (Ƙamusun Hausa
2006:299,300).
An bayyana ma’anar
kalmar sharhi da cewa a dubi sharha mai nufin rubutaccen bayani don ƙara fahimtar abu (Ƙamusun Hausa,
2006:409).
Ga abin da aka ce
dangane da ma’anar kalmar turke: “Turke a ƙa’idar masu nazarin
waƙar
baka na nufin saƙon da waƙa take ɗauke da shi (Gusau, 2008:370)”.
Ita kuma kalmar salo
an ce “Salo yana nufin duk wata dabara ko hanya wadda mawaƙi ya bi domin ya isar
da saƙon da yake son ya isar. Ita wannan dabara ko hanya tana
yi wa waƙa kwalliya ta yadda saƙon waƙar zai isa ga mai
saurare ko karatun waƙa (Yahya, 2016:30)”.
A wani wuri kuma cewa
aka yi, salo na nufin yayi ko sauyi ko launi ko fice (Ƙamusun Hausa,
2006:385). Har yanzu an sami wurin da aka fassara kalmar salo da style[1].
Ita kuma kalmr guguwa
na nufin iska mai ƙarfin gaske wadda take miƙewa sama tana juyawa,
(Ƙamusun
Hausa, 2006:173). Kalmar sauyi kuma na nufin canji ko juyi (Ƙamusun Hausa,
2006:394).
A tamu fahimta kalmar
wadaran na nufin yin tir da wani hali ko aiki da aka yi. Lalace na nufin fitar
mutumin kirki daga kyawawan ɗabi’unsa da kuma ɗaukar munana ko nakkasar wani abu daga ingancin
da aka sani gare shi. Sharhi a wurinmu na nufin ƙarin bayanin kan
maganar da wani ya yi ko rubutun da aka yi. Turke da salo kuwa, mun dakata ga
ma’anonin da aka bayar zuwa nan gaba. Kalmar guguwa da aka yi amfani da ita a
cikin waƙar da za a yi sharhi kanta na nufin wani al’amari mai ban
mamaki da bai taɓa faruwa da ake ganin
zai faru dangane da zaɓen shugaban ƙasa da aka yi a
Nijeriya ta fuskar mai takara ya doke wanda ke saman kujera.
3.0 Taƙaitaccen Tarihin Aminu Abubakar Ladan (Alan Waƙa)
An haifi
Alhaji Aminu ranar 11 ga watan Fabrairu a shekarar 1973, a unguwar Yakasai da
ke cikin garin Kano. Aminu ya yi karatun firamare a makarantar Tudun Murtala
yayin da ya yi sakandare a unguwar Dakata Kawaji. Alhaji Aminu ya cigaba da
karatun gaba da sakandare a makarantar Fasaha da Ƙere-Ƙere da ke Kano wato, School of Technology Matan Fada
Kano. Aminu ya sami takardar shedar karatun Diploma a fannin Art and Industrial
Design. Har yanzu kuma, yana nan yana ci gaba da neman ilimin don kasancewarsa
gishirin rayuwa.
Aminu
marubuci ne kafin ya zama mawaƙi don ya
rubuta littafai da suka haɗa da
‘Sawaba’ da ‘Baƙar Aniya’ da sauransu. Har yanzu yana da sha'awar
rubutu a ransa don nakan tuna wani labari mai ɗaukar hankali da ya fara rubutawa a wani gida mai kama da wanda ya yi wa
suna "Ƙuƙumi" wanda
a halin yanzu yana nan yana rubuta shi tare da duba yiwuwar buga shi. A fannin
sana'arsa ta waƙa a yau, za a iya cewa Aminu ya zarce tsara ƙwarewa da jajircewa da kuma sarrafa harshe tare da
adana adabin Hausa. Hakan ya sa yake da kyakkyawar alaƙa da jami'o'i da kwalejojin ilimi, da har suke karrama
shi tare da nazarin waƙoƙinsa. Aminu na da halastattun albam guda 27 a kasuwa
daga albam na Alhaji Aminu magidanci ne, yana da mãta da 'ya'ya wanda suke
zaune cikin farin ciki da walwala. Duk da dai Alan kan ce "Ni mai mata ne
da neman ƙari kuma, mai 'ya'ya ne da neman ƙari". Fatarmu Allah ya albarkaci waɗanda yake da ya ƙara masu
albarka ya kuma yalwata arzikinsa, ya ba shi ikon kula da su.
4.0 Sharhin Turken Waƙar Guguwar Sauyi ta
Aminu Abubakar Ladan Ala (Alan Waƙa)
Waƙar ‘Guguwar Sauyi’ waƙa ce mai ɗauke da turken addu’a
sai dai, akan sami wasu tubalan ginin turke da suka taimaka ga ginuwarsa. Babu
shakka waƙar siyasa ce mai ɗauke da saƙon addu’a daga mawaƙin tare da bayyana
halayen jama’arsa na wulaƙantar da kai da suke yi ga waɗanda ba su ko kai su
ba balle su fi su. Haka kuma ya bayyana mafi yawan waɗanda aka zaɓa ba suna zuwa domin
jama’arsu ba ne sai don kawunansu. Duk bayanan da za a yi a cikin wannan
takarda zai tafi tare da rakiyar ɗa ko ɗiyan waƙar da ake sharhi
kanta domin tabbatar da iƙirarin da aka yi.
4.1 Turken Addu’a a Cikin Waƙar
Guguwar Sauyi
Kafin a shiga cikin
waƙar
don kawo hujjojin da ke tabbatar da cewa jigonta shi ne addu’a, sai a duba tun
a baitin farko da mawaƙin ya yi a ga abin da ya fara faɗa. Ga abin da ya ce:
1.
O Allah kaɗa guguwar sauyi
Buhari Janar ya karɓi ƙasa,
Ku aje kube sauyi ya zo x2,
Ku aje kibau sauyi ya
zo x2,
Masu sanduna sauyi ya
zo,
Mai barandami sauyi
ya zo,
Bana ƙuri’a fa za ta aje
malfa x2
Sai godiya
hamdullahi,
Allah alhamdullahi x3
Idan aka lura da abin
da mawaƙin ya faɗa a baitin farko za a fahimci roƙon Allah ne ya yi ta
hanyar yin addu’a da roƙon Allah kan matsalar da ke ci masa tuwo a ƙwarya. Matsalar da
mutum ke fuskanta da buƙatar da yake da ne ke sanya shi yin addu’a, balle
matsalar da mawaƙin ke addu’a kanta ba tasa kaɗai ba ce, ta shafi
mafi yawan al’ummar Nijeriya. Saboda ɗaukin da yake yi na Allah ya karɓa masa addu’arsa har
ya sanya ya biyo da maganar da ke nuna kamar an gaya masa an karɓa masa, inda ya ci
gaba da cewa, a aje kube da kibau da
sanduna da barandami da faɗar bana ƙuri’a za ta nuna an karɓi addu’arsa. Ba wannan kaɗai ba, ga ladabin addu’a idan buƙata ta biya, godiya
ake ga wanda aka yi roƙon gare shi kuma, ya biya buƙatar da aka roƙa. Za a ga haka a
inda yake godiya yana cewa, “Sai godiya
hamdullahi, Allah alhamdullahi”. A nan, muna da fahimtar yana magana da
talakawan ƙasa ne ta duban abubuwan da ya jero da faɗar a aje su ganin
kamar an ɗauko su ne an fito
zuwa neman ‘yanci domin, ba a haɗa mai mulki da mai hali da waɗannan abubuwa da aka
kawo domin ba daidai suke da su ba.
Bayan jagoran waƙa ya faɗi abin da ke ƙona masa zuciya da
yin addu’a, ‘yan amshinsa ma ba a bar su a baya ba sai da suka yi addu’a irin
ta jagora inda suka ce:
Amshi: Baƙar Malfa baƙar jarfa,
Mai shanye jinin
jikin talaka,
Allah kaɗa guguwar sauyi,
Buhari Janar karab da gari.
Ba a nan kaɗai ba, daga amshin
farko har zuwa na ƙarshe akwai addu’a a ciki. A idon manazarta duk abin da
mawaƙi da ‘yan amshi suka fi faɗa a cikin waƙa dole a sami yana
daga cikin saƙon da suke son isarwa ga jama’a. A wani wuri sukan ƙasƙantar da kai tare da
nuna cewa abubuwan da suka faru da ke nan suna faruwa babu shakka mu muka janyo
wa kanmu. Tare da haka kuma, sai su yi addu’a domin neman Allah ya magance waɗannan matsalolin da
ke faruwa. Za a ga irin wannan a baiti na uku inda suka ce:
3. Jagora:Subbahanaka rabbi mun gode mu jaddada
godiya gunka,
Amshi:Baƙar malfa baƙar jarfa
Jagora:Allah
Alhamdulillahi gwani sarki kinin bauta ba ma yi maka
Amshi:Shanye jinin
jikin talaka
Jagora: Duk yadda ka
so da bayinka ba mai tuhuma a mulkinka
Amshi:Baƙar malafa baƙar jarfa
Jagora:Muna tuba da
aibunmu ka yafe mana laifuka
Amshi:Shanye jinin
jikin talaka
Jagora: Allahu ka dubi bayinka an tashi hana mu
bautar ka
Amshi:Baƙar malfa baƙar jarfa
Mai shanye jinin
jikin talaka
Allah kaɗa guguwar sauyi
Buhari Janar karab da
gari.
A wurin da jagora ke
cewa, Allahu ka dubi bayinka an tashi
hana mu bautar ka kuka ne yake yi tare da addu’ar neman Allah ya kawo
mafita ga matsalolin da suka taso. A farkon baiti na huɗu kuma, addu’a ce
yake yi ganin bala’o’in da ke faruwa sun yawaita tare da wuce tunanin mutane
kuma, ba abin da ya janyo haka sai rashin adalcin shuwagabanni ga mabiyansu. Ga
abin da suka faɗa:
4. Jagora: Masifu sun
buwaye mu ka saukar mana jinƙanka
Amshi: Baƙar malfa baƙar jarfa
Jagora :Baƙin mulki na zalunci
ake a ƙasarmu ba shakka
Amshi: Shanye jinin
jikn talaka
…………………………………
Haka kuma, abin da
zai ƙara tabbatar da cewa babban saƙon da waƙar ke ɗauke da shi addu’a ce
shi ne baiti na ishirin da biyu da na ishirin da uku kamar haka:
22. Ka yi mana kariya
Allah da dangina masoyanka,
Masoya masu bin waƙa bisa lura da sam
barka,
Allah ga General namu
ka karɓi nufinsa bawanka,
Ka yo sanadi na ceton
mu ta hanyar ba shi mulkinka,
Ya share mana kukanmu
mu bar ƙangin jinin kaska.
23. Allah ka amsa roƙonmu muna kuka da roƙon ka,
Masifu sun buwaye mu
muna kwaɗayi ga tanyonka,
A nan zan sa ɗigon aya a kan nusar
da bayinka,
Ka sa waƙar da na tsara ta zan
ƙaimi
ga bayinka,
Ala mai waƙe al’umma masoyin
sahibi naka.
Idan ma aka tsaya ga
baitocin da ke sama guda biyu da aka kawo masu lamba ta 22 da 23, za su gamsar
kan cewa jigon waƙar guguwar sauyi addu’a ce. A baiti na 22 za a ga cewa
layi na 1 da na 3 da na 4 roƙo ne ga Allah kan matsalolin da ake
fuskanta cikin ƙasa. A baiti na 23 ma idan aka dubi layin farko za a ga
cewa mawaƙin ya faɗa da bakinsa cewa addu’a ce yake yi a inda ya ce, Allah ka amsa roƙonmu
muna kuka da roƙon ka. Haka layi na biyu ma addu’a ce tare da faɗin irin matsalolin da
ake ciki na damuwar rayuwa. Haka ma layi na huɗu akwai addu’a a ciki inda ya ce, Ka sa waƙar da na tsara ta zan
ƙaimi ga bayinka. Da wannan ɗan taƙaitaccen bayani mai
karatu na iya fahimtar cewa, saƙon da wa\ɗark e ɗauke da shi babba
addu’a ce.
4.2 Ƙananan Jigogin Waƙar Guguwar Sauyi ta
Aminu Abubakar Ladan
Bayan babban jigon
addu’a da waƙar ke ɗauke da shi akwai ƙananan saƙonnin da ke cikinta
da mawaƙin ya kawo. Daga cikin ƙananan saƙonnin da waƙar ke ɗauke da shi akwai:
4.2.1 Labartawa
Labartawa na nufin faɗar wani abu da ya
faru ko ke kan faruwa ga wanda ake ganin bai san shi ba ko kuma, ya san da shi
da manufar isar masa da wani saƙo. Akwai wuraren da mawaƙin ya kawo, idan aka
dubi baiti na goma da na sha ɗaya da na goma sha uku da na goma sha huɗu da kuma na goma sha
biyar za a ga cewa labartawa ne yake yi ga mai karatu ko mai sauraro kan
halayen waɗanda ake zaɓe domin su waƙilci jama’arsu.
Maimakon su yi waƙilci nagari sai suka lalace suka mayar da kansu almajirai
ga waɗanda ko bara za a yi
su suka fi cancanta da yin bara ba jama’armu ba. Ga baiti na 10-15 a nazarce su
a gani ba tare da amshi ba kamar haka:
10-Jagora: Arewar
babu mai tari suna tsoron gidan sarƙa
Sun zamto damisar kwali
hayagaga a hotonka
Kyanwar Lami cikin ɗaki ba cizo babu
bautar ka
Ruɓaɓɓu a ciki namu suna
kuma ci da bautarka
Suna inuwa ta addini
suna cutar da bayinka.
11.Jagora: Suna miƙa wulayarmu ga mai ƙi a yi bautar ka
Kamar dabba suke jan
mu da zalinci muna kuka,
An ƙona wajen karatunmu
ana kishin mu ɗaukaka
An ƙone kasuwancinmu a
yau baƙi suna shakka
:Ba mai sha’awar ya
zo gun da hulɗar kasuwa barka
12. :An zaɓi ruɓa-ruɓa namu da sunan waƙiltak ka,
:A ba su kuɗi su miƙa mu hannu ƙwarya hannu bakka,
: Tunaninsu iyalansu
su tara abin da ba tamka,
: Suna tsoron
talaucewa suna shakkar zama talaka,
:Sun zaɓi zama talakkawa a
ranar komuwa gunka.
13. Jagora:Sun maishe
mu kamar kaji, a ba ka hatsi ka sa bakka,
: Da an buga tambarin
zaɓe mutane babu tsoron ka,
:Su sa riga, su sa
hula, su ɗau hoto suna ba ka,
:Su ce ma je ka mammanna
a ɗau na abinci am ba ka,
:Da sun hau karagar
mulki da ƙyar su gane sunanka.
14 - Jagora: Duw wanda ya hau kujera nan abin ƙin sa a ce sauka
:Ya hau ɗamara ta shiryawa da
zango ya yi zai sauka,
:A hau fasali da
tsarawa ana son sabuwar doka,
:Ana wai za a sabunta
a yo doka da ba kyanka,
:Kundi na gudanuwar
mulki su tsarmo sabuwar doka.
15 - Jagora:Su daidaita da son ransu kawai don kar
a ce sauka
:Cikin dimokaraɗiya ake son rai ake
hauka
:A mulkin nan na
al’umma na zaɓan ra’ayin sonka,
:Mulki daga al’umma
aka ce cikin zaɓi na son ranka,
:Ana yi don mutane ne
misalin ba ka ‘yancinka,
Ta la’akari da
baitocin da ke sama ne ya sanya muka raɗa wa takardar suna “Allah Wadaran Naka Ya
Lalace”. Bisa ga ƙa’ida kowa zaɓen sa aka yi don haka, babu dalilin da zai sa
mutum ya nakkasa kansa har ya komo baya ga wanda bai dace ya zama Karen
farautarsa ba. A farkon baiti na goma cewa mawaƙin ya yi, babu mai
yin ko tari a cikin ‘yan arewa saboda tsoron ɗauri. A fahimtarmu ba tsoron ɗauri ba ne, lalacewa
ne suka yi suka koma bayan wasu suna fadanci domin tasu buƙata ba ta jama’arsu
ba. Idan aka ba su kuɗi domin wata buƙatar masu ba su kuɗin, sai su karbi kuɗin ko da za a cuci al’ummarsu
ne domin kansu suke waƙilta a can ba jama’arsu ba. Da jama’arsu suke waƙilta da ba su karbi
kuɗin da ake ba su ba,
kamar yadda mawaƙin ya nuna. Aikinsu kawai shi ne shiga inuwar addini ana
cutar da bayin Allah kamar yadda layin ƙarshe a baiti na goma
ya nuna. A farkon baiti na goma sha ɗaya mawaƙin ya faɗi cewa suna ba maƙiyansu goyon baya
saboda kwaɗayin abin da suke
samu amma, ba su damu da wulaƙancin da ake yi wa jama’arsu ba. Wannan
ke tabbatar da samuwar ƙaramin jigon labartawa cikin wannan waƙa.
4.2.2 Sukar Ra’ayi
Suka na ɗaya daga cikin ƙananan saƙonnin da waƙar ‘Guguwar Sauyi’ ke
ɗauke da su. A
fahimtarmu suka na nufin faɗar illar wani mutum ko wani abu ga jama’a domin su ƙi shi ko su ƙi wannan abu nasa da
yake tare da shi, ko kuma domin a guje shi saboda wata manufa da yake da ita
mummuna zuwa ga mutane ko kuma domin wata cuta da ya taba yi wa mutane. Mutum
ba ya taba suka abin da yake so sai dai ya yaba shi. Haka kuma, an fi samun
sukar ra’ayi a siyasa da sauran abubuwan da mutum biyu ke nema bayan an
tabbatar da mutum ɗaya ke samun sa. Waƙa ce da aka yi kan
siyasa mai cike da abubuwa daban-daban da suka shafi siyasa ga abin da ya
bayyana na zahiri a ciki. Al’adar siyasa ce a yabi wani a soki ra’ayin wani,
kamar yadda aka gani a cikin kowane amshi a layuka biyu na farko. Ga abin da
aka faɗa a cikin layukan
biyu:
Baƙar malfa baƙar jarfa
Mai shanye jinij
jikin talaka
Kalmar jarfa na nufin
(sn, mc) (i) shasshawa ko tsaga da ake yi don ado ko don magani (ii) abin da
ake yin shasshawa da shi. A cikin wannan waƙa ma’ana ta biyu ce
ta fi dacewa da abin da waƙar ke nufi wato, ƙarfen da ake yin
shasshawa da shi ga dabbobi marasa lafiya.
4.2.3 Zambo
Zambo na nufin ƙaga wa mutum Magana
wadda za ta muzanta shi ba tare da bayyana wanda ake yi wa ba; maroƙa sun fi yin haka a
cikin waƙa.[2]Bayan
wannan akwai wurin da sukar ra’ayin ta rikiɗe ta koma zambo kai tsaye saboda tsananin ƙiyayya. Za a ga
wannan a baiti na ishirin inda mawaƙin ke cewa:
20. Matakin kansula
har kan president zabi mai son ka
Ku lura da kyau
talakkawa kuna zango tsaka-tsaka
Muna dama ta ƙarshe ne gaba ɗaya ba ragen ɗakka
Ƙoyaye kwarkwata tamu
a yo zabi a gunshe ka
Da kunne ya ji mun tsira da zalunci na ‘yan iska
Idan aka dubi layi na
ƙarshe
da aka ture rubutunsa za a ga kalmar ‘yan
iska zagi ne kai tsaye ga masu zaluntar jama’a, musamman ta bangaren waƙilcin siyasa.
5.0 Salailan Da Ke Cikin Waƙar
‘Guguwar Sauyi’
Ba sai an ambaci
ma’anar salo a nan ba domin bayaninsa ya gabata a shafi na biyu. Akwai salailai
masu dama da suka fito cikin waƙar ‘Guguwar Sauyi’ kamar yadda za a
gani a cikin sharhin salailan da za a yi. Daga cikin salailan da aka samu a
cikin waƙar sun haɗa da waɗannan:
5.1 Salon Buɗewa
Waƙar ‘Guguwar Sauyi’ na
da mabuɗin da mawaƙinta ya yi amfani da
shi domin buɗe waƙarsa tun a baiti na
farko inda yafara da addu’a, yana roƙon Allah ya tare da
faɗarburinsa a fili inda
ya ce:
1.Jagora: O Allah kaɗa guguwar sauyi
Buhari Janar ya karɓi ƙasa.
Ku aje kube sauyi ya
zo × 2
Ku aje kibau sauyi ya
zo × 2
Masu sanduna sauyi ya
zo
Mai barandami sauyi
ya zo
Bana ƙuri’a fa za ta aje
malfa ×2
Sai godiya hamdullahi
Allah alhamdulillahi
×3
Bayan wannan buɗewa da mawaƙin ya yi ta fuskar
neman Allah ya kaɗa guguwar da za ta zo
da sauyin shugabanci a Nijeriya tare da faɗar buƙatarsa dangane da
wannan sauyi idan ya zo. Bai wuce ba sai da ya faɗi yadda yake buƙatar sauyin ya
kasance kamar yadda ya nuna a baiti na ɗaya. Haka su kuma ‘yan amshi, duk a mabuɗin sun amsa wa jagora
da cewa:
Baƙar malfa baƙar jarfa
Mai shanye jinin
jikin talaka
Allah kaɗa guguwar sauyi
Buhari Janar ya karbi
ƙasa.
5.2 Salon Rufewa a Cikin Waƙar
Guguwar Sauyi
Yadda aka sami salon
buɗewa a cikin waƙar haka ma akwai
salon rufewa wato closing doxology.
Akan sami waɗannan salailai a
cikin mafi yawan waƙoƙin sha’irai matuƙar ba mantuwa ta same
su ba ko yanayin waƙar domin wasu waƙoƙi ba a buɗa su ko rufe su kan ƙa’idar da aka sani ta
buɗe waƙa da rufe ta ba. Mawaƙin ya rufe waƙarsa a baiti na
ishirin da uku kamar haka:
23:Jagora:Allahu ka
amsa roƙonmu muna kuka da roƙonka
:Masifu sun buwaye mu
muna ƙwaɗayi da tanyonka
:A nan zan sa ɗigon aya a kan nusar
da bayinka,
:Ka sa waƙar da na tsara ta zam
ƙa’imi
ga bayinka,
: Ala mai waƙe al’umma masoyin
sahibi naka,
5.3 Salon Kamance
Salon kamance bangare
ne na babban salon siffantawa. Salo ne wanda ke bayyana sifar wani abu ta
fuskar kwatanta shi da wani abu daban tare da amfani da kalmomin da za mu ba
suna mizani.[3]Waƙar na ɗauke da salailan
kamance guda uku da masana suka yi bayani da suka haɗa da kamancen fifiko
da kamancen daidaito da kuma kamancen kasawa. Akwai salailan kamance da suka
fito cikin waƙar ‘Guguwar Sauyi kamar haka:
5.3.1 Salon Kamancen Fifiko
Kamar yadda sunansa
yake nuni kamancen fifiko yakan ɗauki abubuwa biyu: da wanda yake ƙoƙarin ya siffanta da
kuma wanda da shi ne yake ƙoƙarin ya siffanta na
farkon, sai y ace wannan na farkon ɗin ya fi wannan da ya kawo ma wand aka rig
aka sani. Wato dai y ace gwarzona ya fi wancan da ka sani.[4] Akwai
kalmomoin mizanin da suka haɗa da : ya fi, ta fi, ya zarce, ta zarce, ya wuce da dai
sauran irinsu. Akwai kamancen fifiko a cikin waƘar ‘Guguwar Sauyi’ a
baiti na takwas da na goma sha biyu inda za mu ɗauki misalinmu a baiti na takwas kamar
haka.
8. Jagora: A sa riga
ta Islamu a yo wauta ƙazantarka,
:Sannan fa a jingina
kan mu waƙilai babu mai tanka,
:Mu yi burin mutuwa
bayi idan mun taka alhakka,
:Tutur ata fau ba za
mu yi ba saboda abin da mun shuka,
:Mu bar Allah maƙaginmu mafi girma da ɗaukaka.
Idan aka dubi layin ƙarshe za a ga cewa,
mawaƙin ya fifita Allah a kan kowa da komi inda ya yi amfani
da kalmar mafi. Babu shakka haka
maganar take domin babu mai girma sai wanda Allah y aba shi kuma, Allah ke ɗaukaka kowa a ban ƙasa. Haka kuma duk
yadda mutum ya girma ya sami ɗaukaka, bay a kamar Allah.
5.3.2 Kamancen Daidaito
Akwai kamancen
daidaito a cikin waƙar ‘Guguwar Sauyi’ da mawaƙin ya yi amfani da
shi wajen haɗa abubuwa biyu da
suke daidai da juna. Wannan salon a da kalmomin mizani da suka haɗa da awa,kamar, wa,
i, ƙoƙa, ya, ce kake da
kuma daidai da.[5]
Akwai misalign kamancen daidaito a cikin baiti na 9, 10, 11, 13, 15, 16, da 17.
Ga baiti na 13 domin ganin misalin da mawaƙin ya kawo na
kamancen daidaito kamar haka:
13. Jagora:Sun maishe
mu kamar kaji, a ba ka hatsi ka sa
bakka,
:………………………………………………………
…………………………………………………….....
5.3.3 Kamancen Kasawa
Kamar sauran
kamance-kamancen da aka yi bayani a sama, kamancen kasawa ma na da wasu
kalmomin mizani da ake gane shi da su a cikin waƙa ko rubutu baki ɗaya. Kalmomin mizani
da ake amfani da su a cikin gane kamancen kasawa sun haɗa da bai kai ba, ya
kasa, gara, bai yi kamar, ba ta yi kamar da sauransu. Idan aka dubi wannan waƙa za a sami salon
kamancen kasawa a baiti na 16 kamar haka:
16 - Jagora:O amma ko
mulukiya ba ta yi kamar haka hauka
………………………………………………….
Idan aka dubi rubutun
da aka ture da ke cikin baitin da ke sama za a fahimci salon kamancen kasawa ne
mawaƙin ya yi amfani da shi inda ya ce:
O amma ko mulukiya ba ta yi kamar haka hauka.
Wannan na nuna cewa,
salon mulkin mulukiya ma bai kai tsananin mulkin da mawaƙin ke magana a kai
ba. A fahimtar maaƙin, salon mulkin mulukiya ne ƙoli ga zaluntar
jama’a duk da hakanan, salon mulkin da mawaƙin ke zance a kai bai
ya zarce na mulukiya da rashin adalci. Ke nan, mulkin mulukiya bai kai tsananin
wanda mawaƙin ke magana a kai ba.
5.3.4 Salon Gangara
Akan samu baiti a
cikin waƙa wanda kan ƙunshi wani ɗango wanda zaren
labarinsa bai cika ba sai a wani ɗango mai bin sa. To irin wannan saƙa ita ce ake kira
salon gangara a nazaarin waƙa.[6] Ga
binciken da muka yin a wannan waƙa mun tarar da akwai
salon gangara a cikin dukkan amshin da ke cikin waƙar kuma, an same shi
a cikin baiti na goma sha uku. Ga misalin amshi da baiti na 13:
Amshi :Baƙar malfa baƙar jarfa
:Mai shanye jinin
jikin talaka
:Allah kaɗa guguwar sauyi
:Buhari Janar ya karɓi ƙasa.
Abin da ake nufi da
salon gangara shi ne, a sami a cikin baitin waƙa ɗaya mai layi biyu ko
uku ko huɗu ko kuma biyar
kowane layi bay a tsayi da kansa domin ba da cikakkiyar Magana har sai ya
jingina ga wani layi mai bin sa. Idan aka nazarci amshin da ke sama za a tarar
da babu layin da ke tsayawa da ƙafarsa domin ba da kammalalliyar
ma’ana. Maimakon haka dole sai ya haɗa da ɗan uwansa kafin a sami ma’ana cikakkiya.
Misali, inda y ace ‘Baƙar malfa baƙar jarfa’ ma’ana ba
ta fito ba amma a layi na biyu da ya ce ‘Mai shanye jinin jikin talaka’ ma’ana
ta cika. Haka kuma, cewar da ya yi ‘Allah kaɗa guguwar sauyi’ akwai sauran magana a baya
da ake sauraro domin ma’ana ta cika. Layi na biyu kuwa, shi ya taimaka ga cikar
maganar da ke a layi na uku. Duk wurin da aka sami irin wannan maganar da ba ta
cika a layi na farko sai na biyu ko na uku ko na huɗu ko kuma na biyar,
shi ake nufi da salon gangara. Ga wani misali a baiti na goma sha uku inda
kowane layi ya dogara ga ɗan uwansa ga ba da
cikakkiyar ma’anar maganar da mawaƙin ya yi kamar haka:
13. Jagora:Sun maishe
mu kamar kaji, a ba ka hatsi ka sa bakka,
: Da an buga tambarin
zabe mutane babu tsoron ka,
:Su sa riga, su sa
hula, su ɗau hoto suna ba ka,
:Su ce ma je ka
mammanna a ɗau na abinci am ba
ka,
:Da sun hau karagar
mulki da kyar su gane sunanka.
5.3.5 Salon Aron Kalmomi
A cikin mafi yawan waƙoƙin da marubuta ke
rubutawa da waɗanda ke rerawa na
Hausa akan sami salon aron kalmomi daga wasu harsuna da suka haɗa da Turanci da
Larabci, wani lokaci har da Fulatanci da sauransu. A cikin waƙar da muke sharhin
jigo/turke da salailanta mawaƙin ya ari kalmomin Turanci da na
Larabci ya yi amfani da su a cikin waƙarsa. Idan aka dubi
baiti na 1,2,8,18,20,21 da kuma na 22 duk akwai kalmomin da mawaƙin ya ara daga wasu
harsuna ya yi amfani da su a cikin waƙarsa. A baiti na 1
akwai kalmar hamdullahi da alhamdulillahi, a na 2 akwai haɗari da sahibul
sabariyya, a na 8 akwai kalmar alhaƙƙa, na 18 akwai kalmar
Turanci ta weapon, a na 20 akwai kalmomi biyu na Turanci kansila
(councilor) da ta president, a na 21 kuma akwai kalmar janar (General) da kuma kalmar general a baiti na 22.
Kalmomin da ke cikin
baitin farko na Larabci ne masu nufin godiya ga Allah da godiya ta tabbata ga
Allah. Kalmar haɗari (Khaɗar) na nufin abu mai
matsala da ya kamata a shiga saunar sa. Sahibul sabariyya kuwa na nufin
ma’abuci haƙuri. Alhaƙƙa na nufin gaskiya a baiti na takwas
inda weapon da councilor da president da general duk kalmomin Turanci ne.
Weapon na nufin makami. Councilor na nufin wanda aka zaba a mazabar ƙaramar hukuma domin
ya waƙilci jama’ar da ta zabe shi. Kalmar president na nufin
shugaban ƙasa inda general ke nufin babban muƙami na gidan soja da
ake ganin na ƙoli ne ko ba ƙolin-ƙoliyo ba. Duk da
bayanin da aka kawo ya dace a kawo ko da baiti ɗaya a matsayin misali. Ga baiti na 20
don ƙara tabbatarwa:
20 - Jagora: Matakin kansila har kan President zaɓi mai son ka,
:…………………………………………………….
……………………………………………………..
5.3.6 Salon Luguden Adabi
A baben adabi da ake
lugude a nan su ne irin su Karin Magana da salon Magana da baƙar Magana da
tatsuniya da kirari da tashe da makamantansu. Idan aka so a saka su yadda aka
san su suka kasa shiga a waƙa sai a kakkarya su a faffalle su a niƙe su a ɗiyan waƙa a bar mai sauraro
da dabarar ƙoƙarin gano dawa ce aka niƙe ko masara?[7] Akwai
salon luguden adabi a cikin waƙar ‘Guguwar Sauyi’ a baiti na shida da
na ishirin inda aka yi amfani da karin Magana. A baiti na shida an yi amfani da
Karin maganar nan da Hausawa ke cewa ‘A bugi jaki a bugi taiki’ amma saboda
lalurar waƙa ga yadda mawaƙin ya saka Karin
maganar:
Jagora: Arewa ƙasarmu ya Allah ta
zamma kufai kamar bukka
: Ana ta bugu a kan taiki shi ko jakki yana
harka
:…………………………………………………
Karin maganar da ke
cikin baiti na ishirin ita ce ‘In kunne ya jiya jiki ya tsira’. Saboda lalurar
waƙa
sai mawaƙin ya juya ta ta koma ‘Da kunne ya ji mun tsira da
zaluncina ‘yan iska’. Ga yadda abin ya zo cikin baitin kamar haka:
:…………………………………………………
:………………………………………………….
Jagora: Da kunne ya ji mun tsira da zalunci na ‘yan
iska
6.0 Hanzari
Hausawa sun ce ‘Wani
hanzari ba gudu ba’. Mu kuma a nan muna sheda wa al’umma cewa duk abin da aka
gani a cikin wannan aikin sharhi namu, ba ra’ayinmu ba ne mun dai faɗe shi gwargwadon
yadda muka fahimce shi daga abin da mawaƙin ya faɗa tare da ‘yan
amshinsa. Ba a yi domin cin zarafin kowa ba sai dai, an san cewa mai kaza
aljihu baya jimrin as. Idan aka sami kuskuren harshe daga gare mu, muna ba da
uzurin kasancewar mu ‘yan tara da ba su kai goma ba. Haka kuma, takardar ta yi ɗan yawan da ba za ta
bari a saka ratayen waƙar a ciki ba ta yadda za a ga abin da mawaƙin ya faɗa sai dai, duk bai
hana saƙon isa ga waɗanda aka yi abin domin su ba.
7.0 Kammalawa
An raɗa wa wannan takarda
suna ‘Allah Wadaran Naka Ya Lalace:
Sharhin Turke Da Salailan Da Ke Cikin Waƙar Guguwar Sauyi Ta
Aminu Abubakar Ladan (Alan Waƙa) ganin sunan ya ɗan dace da abubuwan da mawaƙin ya bayyana a cikin
waƙarsa.
Takardar na ɗauke da gabatarwa da
bayanin ma’anonin kalmomin da ke cikin takenta. Biye da shi kuma taƙaitaccen tarihin mawaƙin ne aka kawo. Bayan
tarihin mawaƙin a taƙaice an biyo da sharhin babban turken
waƙar
wanda yake shi ne, turken addu’a ko jigon addu’a/roƙon Allah. Bayan
babban turken da aka kawo an biyo da ƙananan turakun waƙar da suka haɗa da labartawa da
sukan ra’ayi da kuma zambo. Daga nan ne aka cirata zuwa ga sharhin salailan da
waƙar
ta ƙunsa
da suka haɗa da salon buɗewa da na rufewa da
salon kamancen fifiko da na daidaito da kuma na kasawa. Bayanin salailan bai
tsaya a nan ba sai da aka tabo salon gangara da salon aron kalmomi na wasu
harsuna da mawaƙin ya yi amfani da su a cikin waƙarsa da suka haɗa da kalmomin Turanci
da na Larabci. Takardar ba ta tsaya a nan kaɗai ba sai da ta kwance zare da abawan salon
luguden adabin da ya fito a cikin waƙar. Bayan abubuwan da
aka lissafo akwai bayanin hanzarin marubuta takardar da aka kawo da ke biye da
rakiyar kammalawa da manazarta a ƙarshe.
Manazarta
Bunza, A. M. (2009) Narambaɗa. Ibrash Islamic
Publication Centre ltd. Surulere, Lagos.
Dangambo, A. (1984). Rabe-rabe Hausa da
Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph.
Daura, H. K (2010) “Nazarin kan Waƙar Rayuwa Ta Fati
Musa” Himma Journal Of Contemporary Hausa Studies, Vol. 2, Number 4. Department
Of Nigeria Languages, Umar Musa Yar’adua University, Katsina State
Gusau, S. M. (2008) Waƙoƙin Baka A Ƙasar Hausa:
Yanaye-Yanayensu Da Sigoginsu. Benchmark Publishers Limited, Kano.
Gusau, S.M (1995) Dabarun Nazarin Adabin
Hausa. Fisbas Media Service, Kaduna
Gusau, S.M (2003) Jagoran Nazarin waƙar Baka.Benchmark publishers
ltd.
Kano, B. U. (2006) Ƙamusun Hausa, Cibiyar
Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.
Omar, S. (2013) Fasahar Mazan Jiya: Nazari A
Kan Rayuwa Da Waƙoƙin Malam Mu’azu Haɗeja. Media Service Ltd, Sokoto
Umar, M. B (1985) Ɗanmaraya Jos da Waƙoƙinsa. Ibadan
University Press Limited.
Yahya, A .B (1997) Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna; Fisbas
Media Service, Kaduna
Yahya, A. B. (2001) Salo Asirin Waƙa, Fisbas Media
Service, Kaduna.
[1] Hausa Metalangage shafi na
105
[2] A
dubi Ƙamusun Hausa na Jami’ar
Bayero, Kano shafi na 489
[3]
A dubi Salo Asirin waka na
Abdullahi Bayero Yahya shafi na 67
[4]
Daidai da lamba ta 3 shafi na
73
[5]
A dubi Salo Asirin Waka na A.
B. Yahya shafi na 68
[6]
A dubi Salo Asirin Waka shafi
na 97
[7]
A dubi Narambada shafi na
187-188
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.