𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalam Alaikum. Allah gafarta Mallam, ni ne nake lalata da wata yarinya inama tunanin ni ne farkon fara zina da ita, ni ne silar ɓata mata tarbiya gaba ɗaya. Amma ni yanzu na tuba nabar zina kuma har na yi aure na haihu harda yara. Ita kuma wannan yarinyan har yanzu ina ganinta kan titi tana yawo ta zama karuwa. Idan mun haɗu ko kallonta bana son yi balle ma asan cewa na taɓa kulla wata hulda da ita saboda kariyan mutuncina da kimana. Shin mallan yanzu a hakan meye matsayina gashi ni na tuba amma kuma ita tana kan aikinta na alfasha wanda ni ne sanadiyyar shigarta shi, shin ni bayan neman Allah gafara ya isa ko sai na nemi gafaranta, 'yan uwanta da kuma kila mijinta idan za ta yi aure?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh
Dafarko dai muna tayaka
murna da Allah ya sa kagane wannan danyen aiki daka aikata babban kuskurene tun
mutuwa ba ta riskeka ba, Allah ya sa tubanka ya dore yakuma karbi tuban, ya sa wannan
yarinya ta tuba tadena.
Hakika kaci amanar wannan
yarinya kaci amanar musulunci da al'ummar musulmai ka cutar da rayuwarta ka
cutar da iyayenta kaci Amanar Allah da manzansa, baya kuma da cin zarafinta
amatsayin ta na mace wacce musulunci ya girmamata. Zina dai zunubine mai girman
gaske wanda ke kwashewa mutum albarkar rayuwa.
Sannan kasani tun daga ranar
da ka yaudareta kaci mutuncinta harkai zina da ita wallahi duk wata zina datayi
bayan wacce ka fara yaudararta to kana da kaso na zunubi a cikinta, kasani
Allah ba'azzalumi ba ne bazai barka hakaba.
kai yanzu zakaso ace,
Uwarkace wannan yarinyar? zakaso a ce kanwarkace wani yazamto sanadiyyar
zamanta haka? zakaso a ce yayarkace takasance haka ko zakaso a ce 'yarkace
haka? gashi yanzu kaida kanka bakama so kanuna alamarma kasanta, to kasani zina
bashice wallahi duk wanda yai da uwar wani za ai datasa uwar, inkai da 'yar
wani za a yi da taka, idan ka yi sai da ka ba da kuɗi ko
wani abu najan hankali idan Allah ya ga dama kai taka 'yar ita za ta nema ayi
da ita kuma a cikin gidanka za a yi zinar da ita akyaleka da bakin ciki kamar
yanda kasa iyayen wata bakin ciki, kullum baka da sukuni.
Anan zamu kara fahimtar
fasaha da hikima cikin hadisan Annabi sallallahu Alaihi wasallam wanda ya ce
duk wanda ya assasa wani abu na alkhairi duk wanda yai aiki ko koyi da wannan
alkhairi to asalin wanda ya assasa alkharin zaita samun ladan duk wanda ya yi aiki
da alkhairin ko da shawarace kuwa yabayar wajan wani akin alkhairi har duniya
takare haka wanda ya assasa aikin sharri.
Yanzu kaga wannan baiwar
Allah kaine farkon wanda ya assasa mata zina duk wanda ya yi zina da ita kana
da zunubinka na musamman amatsayinka na wanda ya assasa mata zina.
Amma dangane da neman
yafiyar iyayenta ko mijinta duk wannan bai taso ba, saboda Allah bayasan
bayyana mummunan Abu haka shari'a batasan abin da zai haifar da fitina a
tsakanin al'umma wanda bayyana ma iyayenta da neman gafararsu zai iya buɗe
wata sabuwar kofar fitina da rikici a tsakani, dan haka ka kara zage damtse
wajan nema mata gafara wajan Allah da iyayenta, miji kuwa ba ta samu ba, balle
kanemi gafararsa.
Kadage wajan bin duk wasu
hanyoyi nakaga kajawo hankalinta danta daina wannan mugun aiki, zance baka
kulata dankare mutuncin kanka baima taso ba anan, dole kabi hanyoyin dakabi
wajan yaudararta harka shawo kanta ka yi zina da ita, sune za ka sake bi wajan
jan hankalinta dataji tsoran Allah ta tuba kamar yanda katuba, kanuna mata
kaima ka yi nadamar abin da ka aikata da ita, kuma kanajin ciwon abun atare
dakai, kada ka karaya wajan bin hanyoyin dazaka tabbatar kaci nasara wajan
tadena karuwanci ta tuba.
Idan Allah ya sa ka yi nasara
ta tuba, to tunda kaine kasata wannan hanyar kuma katuba, itama ta tuba, to
ihsanin dazakai mata shi ne ka aureta kazauna da ita itama tasamu zurriya, ko
kuma katashi haikan kashiga nema mata mijin aure nakirki ya aureta danta samu
zurriya dayyiba, dan kasamu ko Allah yakalli tubanka yayafema wancan cin
mutunci dakai mata ko Allah zaisa yakalli niyyarka yakarbi tubanku kai da ita
baki daya.
wannan shi ne kaɗai abin
da za ka yi idan harda gaske ka yi nadamar wanan mugun aikin naka kuma ka
gwammace jin kunyar duniya akan ta lahira agaban mutanenen duniya baki ɗaya,
ta duniya kuwa watakilama iya unguwarkune kawai kuma ba ta kaiwa wata kana
cikinta wannan jin kunyar shi ne Zaman lafiyarka.
Sannan ku kuma mata irin waɗannan
bayanai nayanda ake maida rayuwarku kamar ta dabbobi awulakantaku wulakanci
makaskanci ya isheku izinah akan yanda kuke ba da kanku bori yahau ya yi sukuwa
daka baya ya fi kowa kinku daganinku aruyuwarsa.
'yar uwa yanzu kiduba dai
yanda mai tambayarnan yake bayani waifa yama tuba kenan, amma haɗuwa
da ita kan hanya bayasan yi, shi namiji inzayi zina da mata dubu ba ruwarsa ba
ne bawanda ya isa yagane kuma zaisamu wacce za ta zauna da shi, ayayin da ke
kuma zai lalata miki rayuwa cikin wasu 'yan mintuna biyar zuwa goma dazaki
wulakantar dakanki danki faranta masa rai ki kuma fusata mahaliccinki
mahaliccinsa ga kuma kaskanci da tozarci dazaki janyowa rayuwarki har ta
'yayanki kinci amanarsu, iya abin da wanann mai tambayar yafadi a cikin
tambayarsa ya isa wa'azi da kukan zuci akan yanda kuke sai da rayuwarku da
mutunciku da darajarku da Allah yaimuku ga wasu maikiyanku makiyan rayuwarku,
akan naira dubu ɗaya ko uku da zai baki ki yi
ankon bikin kawarki ko yasaki amotar daya sato kuɗin
babansa ko uwarsa ya iyo hayarta, ko yadakko ba tare da ubansa ya sani ba, ko
saboda kuɗin kifin gwangwani da maltina da
shinkafa dakayan makulashe da zai dunga saya miki kina zuwa da su collage kina
nuna kewata ce alhali mahaukaciya ce wacce dabba tafita tunani maikyau.
Saboda darajar 'ya mace ne
fa musulunci yai umarni daki dunga rufe duk jikinki inzaki fita saboda tsadarsa
ne aka umarceku da hakan, bawai dan atsananta muku ba ne, duk wani abu mai
tsada ɓoyeshi
ake ba a bayyanashi afili shin ba za ku hankaltaba yaku uwayen al'ummar manzan
Allah sallallahu Alaihi wasallam! ko da kuɗi ɓoyesu
ake bakasan kowa yasan nawane alalitarka sai dai kadunga dakkowa kaɗan-kaɗan
kana hidimarka meyasa saboda suna da daraja, to kuma darajarkuce tasa musulunci
ya umarceku da ku kame kanku tahanyar sutura mai kyau, da kin ruduwa da
kyalekyalen duniya.
Mace zinari ce ba ta tsufa,
shiyasa sanda wani yagi sake a lokacin ne kuma wani sai ganki ya ce yana sonki,
kuma babu mummuna cikin mata sai dai inbata gyara kanta ba ne danme zakibar
wani mugu azzalumi makiyinki ya lalalata miki rayuwa da hankalinki da kimarki
da mutuncinki, haka kawai dan wata karamar buƙata
ta duniya, ya kamata mu yi tunani na nutsuwa kugane masu alaka daku danku zauna
da su ku yi rayuwa mai kyau gwargwadon abin da Allah yabasu, ba masu aro mashin
roba-roba, ko masu aro mota suna zuwa suna hure muku kunnuwa kuna mantawa da
irin darajar da Allah ya yi muku ba, ko masu shiga rigar addini suna yaudararku
dasunan cewa sudin na Allah ne, a'a kawai wani abune ajikinki suke buƙatar su ɗanɗana
su ji yaya kuke su gujeku.
Da rayuwa cikin kaskancin da
fushin mutane da fushin Allah dana masu imani gwara rayuwa cikin mutunci da
talauci. Allah ya sa mufahimta kuma mu gane.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.