𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum
warahamatullah Malam ya ibada, Allah ya karbi ibadunmu. Malam dan Allah ina da
tambayar wani Abu daya shige mana duhu wata yarinya ce take zaune a gidan kanin
babanta sai yaron gidan ya ce yana son ta sai ta amince suka fara soyayya sai
yake zuwa mata da maganar alfasha amma ta ki amincewa da shi har ta nuna masa za
ta iya rabuwa, in dai sai ta aikata saɓon
Allah ne to za ta iya rabuwa da shi shi ne ya ci alwashin shi kuma sai ya yi lalata
da ita ya rinjaye ta da kuɗi, kaya, babbar waya amma
duk taki amincewa shi ne ya je ya yi mata asiri ya mallake ta yanzu idan yafadi
magana ba ta isa ta musaba sannan kuma duk lokacin daya nemi lalata da ita za
ta je tana kuka tana komai idan ta dawo ta yi ta rokon Allah ya cire mata son
wannan saurayin yakuma yafe mata a haka har ya yi mata ciki kuma ya ba ta
magani ya zuɓe yanzu haka ta tuba ga Allah kuma ta yi
alkawarin ba za ta sake zuwa gun wannan saurayi ba idan ya kira ta ko zai kashe
ta, To yanzu haka tana kwance ba ta da lafiya tana jinyar olcer sakamakon azumi
shi ne take ganin kamar ba zata warke ba kamar mutuwa za ta yi shi ne take faɗa
min labarin ya ba ni tsoro sosai shi ne na ce bari in tambaye ka. Tambaya anan shi
ne:
1. Shin tana da laifi tun da
asiri ya yi mata kuma ba a son ranta take yi ba?
2. Yaya matsayin zinar da ta
aikata?
3. Ya matsayin tubanta???
HUKUNCIN SAMARI MASU YI WA ƳAN MATA ASIRI, SUNA ZINA DA SU
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam:- Da farko
dai tayaya ta san asiri ya yi mata? Dole kafin hukuncin wanda aka yiwa sihiri
ya hau kanta sai an tabbatar ta dalilin tafiyar hankalinta ko ayyukanta. Domin
Mutane sun iya kawo Uzuri don kaucewa hukuncin Shari'a.
Idan an tabbatar cewa mutum
sihiri aka yi masa, to matu'kar wannan sihiri ya ci galaba a kan hankalinsa ta
yadda yana aikata wasu ayyuka ba bisa hankali ba to a wannan tun da fin
karfinsa aka yi to bazai zama Mukallafi ba balle har laifi ya hau kansa. Amma
idan sihirin bai taɓa tasarrufinsa ba to za a
kirga ayyukansa ayi masa hukunci dasu.
Dan haka da wannan 'ka'idar
za ta auna in dai ya tabbata sihiri ya mata to wannan kamar tilasci ne dan haka
ba ta da laifi.
Duk wanda ya tuba Allah zai
karɓi
tubansa matu'kar ba mutuwa ya yi yana shirka ba ko ransa baizo gargara ba ko
lokacin karɓan tuba ma ƙarshen zamani bai zo ba.
Sannan idan ma da gangan ta
biye mishi ya rage nata tuba kawai za ta yi matukar ta cika sharuddan tuba ta
yadda ba za ta sake maimatawa ba kuma ta yi nadama to tubanta zai karɓu.
Wallahi Ku Ji Tsoron Allah,
Ku Sani Cewa za ku Mutu Ku Je Ku Tarar Da Ubangijin Ku a Ranar da Wayon Ka Bai
Tsinana Maka Komai, Dukiyar Ka Ba Zai Tsinana Maka Komai ba, Yawan Danginka,
MasoyanKa ba za su Tsinana Maka Komai ba Sai Ayyuka Kaɗai.
Kayiwa Ɗiyar Mutane Asiri ka yi Zina da ita
Shikenan Buƙatar ka ta Biya, toh
Ka Sani Cewa Kamar Yadda ka yi zina da Ɗiyar
Wani Kaima Haka za a yi da Naka Ɗiyar
ko Kana so ko baka So, Kana ganin burgewa ne buƙatarka
ya biya Ka ƙeta mata haddin ta ka
raba ta da jin ɗaɗin
ta ka sanya mata bakin ciki da tashin hankali ka cutar da ita, Ka Ci Amanar
Iyayen ta ka Ci Amanar Allah da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam sannan
kace kai za ka zauna Lafiya? Wallahi karya kake yi dole ne kai ma Sai Allah ya
yi maka irin Abin da kayiwa Ɗiyar
Mutane.
Ka Sani Cewa wannan
Yarinyar, Shin Idan Kaine Wani ya yi Zina da Ɗiyar
Ka Me za ka yi da shi? Itama Ɗiyar
wani ne!! Shin Idan wani ya zo ya yi Zina da Mahaifiyar ka? za ka ji daɗin
Hakan? Itama nan gaba Mahaifiyar wani ne? Shin idan Wani ya zo ya yi Zina da
Matar ka za ka ji daɗin Hakan ne? Ka sani Cewa ka
Lalata Rayuwar ta, itama Matar Wani ne, yanzu idan wani ya ji Labarin Cewa ga Abin
da ka yi mata, wani daker zai yarda ya ce zai Aure ta, Shin mene ne ka Jawo
mata? Idan Kaine aka yiwa Ƴar
Uwar ka hakan ko aka yiwa ɗiyar ka hakan me za ka ce?
Wallahi Samari Masu Son
Zuciya Masu Lalata Rayuwar Ƴan
Mata Ku Sani Cewa Allah na ganin ku, kuma Shakka babu Kamar Yadda ka Lalata
Rayuwar Ƴar Mutane kaima Haka za a Lalata naka,
sannan daga nan Duniya za ka fara ganin Sakamakon Ubangijin ka kafin ka je
Lahira ka Tarar da Azabar Allah, daga Cikin Ƙabarin
ka za ka fara ganin Bala'i Har zuwa Ranar Alkiyama. Wajibi ne gare ku, ku ji
tsoron Allah ku Dena Lalata Rayuwar Yaran Mutane.
Ku ma Ƴan Matan da Naku yaya Namiji zai fara
kawo Muku Bayani irin na Alfasha sannan wai ki ci gaba da sake masa Fuska har
kina iya Karɓan abun Hannun sa ko kina iya zuwa Hira
wajen sa? Yaya Asiri ba zai Kama ku ba, kamata ya yi daga Lokacin da Namiji ya
fara Bayyana na miki Siffar Kalmar Batsa na Alfasha ku yi gaggawan Rabuwa da
shi, domin ba shi ba ne ɗan Autan Maza a Duniya
Balletana kice idan kin rasa shi Shikenan babu ke babu yin, idan ya Ƙi, ki Haɗa
shi da Hukuma a ɗauki Mataki a kansa, wallahi
Mutuncin Ki da Kimar ki Darajar Ki Martaban ki wallahi ya wuce Wai Ki Tsaya
Namiji yana furta miki Kalmar Alfasha amma wai kina jin Tsoron ki Gayawa Iyayen
sa akan ya Rabu da ke, sai daga Baya ya zo ya Lallaɓe ki
ya yi Zina da ke a zo ana ta Yin Tambaya wai na yi Nadama, wani Nadama zakiyi? Ai
tun farko ne Ya kamata ki yi Nadama ki Guje shi ki Ja masa layi Ki Rabu da shi.
Amma sai Buƙatar sa ya biya a zo
ana Tambaya, toh ku ji Tsoron Allah wallahi ba a siyar da Mutunci Ko Daraja Ko
Kimar ki ko Martaban ki Ko Budurcin ki a Kasuwa, amma meyasa ke ba zakiyi iya
Kokarin ki wajen koran Kowane ɗan Banza ba wai kina tsoro.
Ai Ko ɗan
Wani gida ne ki fito Ki ɗauki mataki a kansa ki
sanarwa Iyayen ki su nemi Iyayen sa, amma wai sai ku yi Shiru ko mene ne
Amfanin shirun. Allah ya tsare. Allah ya yafe mana ya ba ta lafiya. Ameen 🤲
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.