Ticker

6/recent/ticker-posts

Gajerun Labaran Hausa: Ina Aka Fito? Ina Ake? Ina Aka Dosa?

Dandali ne da za a tattauna kan batun Gajerun Labaran Hausa, masana da manazarta ne za su bi wannan kadada domin zama a wannan dandali su fayyace mana kome kan batun gajerun labaran Hausa ƙarƙashin jagorancin Dr. Ginsau Abdulkadir.

1. Dr Ginsau Abdulkadir haifaffen garin Hadejia ne, ya yi aikin koyarwa a matakai daban-daban, kama daga firamare da ƙarama da babbar Sakandare a Jihar Jigawa, yayin da yanzu ya ke koyarwa a Jami'ar Sule Lamiɗo da ke Kafin-Hausa a jihar Jigawan Nijeriya.  Dr Ginsau mai bincike ne a fannin Tarihi da Adabi da Al'adun Afirka. Ya sami shaidar digirinsa na farko B.A (Hons) Hausa da na biyu (M.A African Cultural Studies) da na uku (Ph.D African Cultural Studies) duk a Jami'ar Ahmadu Bello Zariya, inda bincikensa ya mayar da hankali a fannin Falsafar (Tuntuntuni) al'umma dangane da tarihi da al'adunsu.

2. Dr. Mujaheed Abdullahi shi ne Sahabi na farko kan abinda ya shafi gajerun Labaran Hausa. Dr. Mujaheed malami ne kuma mai bincike a fannin adabi da  al’adun zamani da nazarin nakasa da cigaban zamantakewa da hulɗar al’umma. Malami ne a Jami’ar Jihar Kaduna. Yana da digirin PhD daga Jami’ar Umaru Musa ’Yar’adua, Katsina, inda bincikensa ya mayar da hankali kan nazarin gajerun labaran Hausa. Dr. Mujaheed ya samu digiri na biyu (MA) daga Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, sannan ya samu digirin farko (BA) daga Jami’ar Jihar Kaduna. Kafin shigarsa aikin koyarwa a jami’a, ya yi aiki a matsayin Jami’in Wayar da Kai da Cigaban Al’umma, sannan ya kasance Mataimakin na musamman a kan Bincike da Rubuce-rubuce ga Shugaban Ƙaramar Hukumar Kudan. Haka kuma yana ba Majalisar Ƙaramar Hukumar Kudan shawara a fannonin ilimi da ci gaban zamantakewa.

3. Dr. Kamilu Dahiru Gwammaja. Marubuci ne kuma malamin jami'a da ya samu digirinsa na uku a jami'ar Bayero dake Kano a bangaren Hausa. Shahararsa a rubutu da gudumuwarsa a bangaren adabi a fili take. Zai kasance a wannan tattaunawa domin ƙarawa miya zaƙi kan sauyin fasalin rubutu zube daga dogo zuwa gajere.

4. Fatima Hussaini EL- Ladan marubuciya ce da ke gwagwarmaya kan abin da ya shafi 'yancin mata, ta yi rubuce-rubuce da yawa ta rubuta littafi mai shafukan sama da Dubu da aka ba suna "MUMA 'YA'YA NE" yanzu haka tana digirinta na biyu a fannin nazarin Adabin Hausa a Jami'ar Bayero da ke Kano.

5. Kabir Yusuf Anka marubuci ne da ya ratso zamunna mabambanta, sannan ya bada gudumuwa a dukkan fannoni rubutu da suka haɗa da zube da waƙa da wasan kwaikwayo. Kasancewarsa wanda ya hau turba biyu gajerun labarai da dogaye shi yasa zamu kasance da shi a wannan dandalin baje koli domin sanin zaruruwan da ke tafiyar da rubutun gajerun labaran da dogaye. Kabir Yusuf Anka ya na digiri na biyu a fannin nazarin Adabin Hausa a jami'ar Bayero dake Kano yanzu haka.

Gajerun Labaran Hausa: Ina Aka Fito? Ina Za a? Ina Aka Dosa?

Post a Comment

0 Comments