𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu allaikum Malam ya kake ya Gida ya haƙuri da mu Mallam don Allah in son ka fahintar DA NI akwai wani Abu ne da yashige min duhu don ALLAH malam mene ne hukuncin Gaba sakanin musulmi da musulmi har yakai ya kawo babu ko sallama Tsakanin su shin koda iyayenka neh da wasu suke irin wannan gaban za ka iyayin biyayya agare su duk dace malamai suna ce Babu biyayya ga ɗan Adam wajen saɓawa ALLAH, Shin har ɗaya daga cikin su ya furta wannan kalman kamar haka
Koda bayan Ransa neh bai
yarda dan gidan makabcinsa ya auri yarsa ba shin kana ganin wannan wasiyar ta
yi kenan malam ALLAH yakaramaka lapiya da imani malam. Jaxakallahu fill jannah
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa’alikumussalam da farkodai
yakamata a bincika meya Haɗasu, sekuma ayi ƙoƙarin
dai-daita su, "domin an fasa sauƙar
da LAILATUL ƘADARI sakamakon fada
da wasu daga Cikin sahabbai sukayi, aka daga ranan zuwan ta izuwa sauran
kwanakin" hakanan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya haramta musulmai su
yi kwana uku batare da sunyi magana da juna ba, wato abin da ya shafi fada,
gaskiya akan wannan akwai Uguba babba, yakamata ku musu nasiha ko kusa a
musu....
Idan ka kasance akwai wata ƙullalliyar gaba a tsakanin ka da wani ɗan-uwanka
musulmi, to ka yi ƙoƙari kaje kuyi sulhu ku shirya da
junanku, domin haƙiƙa babu wani alamun alkhairi a cikin yin
gaba da juna a matsayinku na musulmai baki ɗaya"
"Ko da a ce wani ya
munana maka, to kai ka daure ka kyautata masa, idan ma kana ganin baza ka iya
kyautata masa ɗin ba, to ka daure kada ka ƙullaceshi da gaba, ko da ka yi yunƙurin hakan, to sai ka daure ka tuna
matsayin musuluncinku da ya haneku da yin gaba, tabbas Allah zai gafarta maka
in sha Allahu"
"An sami ruwaya daga
Abi Hurairata Allah ya ƙara
masa yarda ya ce, lallai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, ya ce: ana buɗe ƙofofin aljannah a dukkanin ranar litinin
da ranar alhamis, sai a gafartawa kowane bawa wanda ba ya shirka da Allah, face
sai mutumin da ya kasance akwai gaba a tsakanin shi da ɗan-uwansa.
Sai a ce (da mala'iku) ku rabu da mutane biyun nan har sai sunyi sulhu tukunna.
Ku ƙyale mutane biyun nan har sai sunyi
sulhu tukunna. Ku bar mutane biyun nan har sai lokacin da suka yi sulhu da
junansu tukunna" {Muslim ne ya ruwaito}
Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam, Ya ce: "baya halatta ga musulmi ya ƙauracewa ɗan-uwansa
fiye da kwana uku, zasu haɗu (amma) sai wannan ya kauda
kansa, wancan ma ya kauda kansa (suna kawar da kawunansu ga junansu), to mafi
alkhairin cikinsu, shi ne wanda ya fara yiwa ɗan-uwansa
sallama" Bukhari Da Muslim suka ruwaito
Abin da ya shafi wasici
dayayi kuma wannan bazatayi Amfani ba, matuƙar
Saɓon
ALLAH ne domin ba'ayiwa wani ɗa'a cikin saɓon
ALLAH, da a ce su ɗayan gidan sunada mummunan
dabi'a ne, tofa baza'a hanaka bin wannan Umarnin ba, amma idan kace za ka Aura
daga baya, dan samun maslah wannan ba matsala in sha ALLAH, Domin shi wasiyya ana
yi akan ɗayan
biyu ko wasiya da haƙuri
ko da gaskiya... Kaman yadda Suratul asar ta nuna.
Shiyasa Imam shafi'ie ya ce
"idan da ALLAH be sauƙar
da wata hujja akan halittunsa ba, se wannan surar (suratul asir) da ta
ishesu" usulus salasa
A wani waje ya ce
"lalle mutane ko mafiyya yawan su, basa ta dabburin waccar" suratul
asar....
Tabbas damuna tunani akan
su, da bazamu fada cikin halaka ba, ayata biyu cikin surar ALLAH ya ce:
إِنَّ الْإِنسَانَ لَفِي خُسْرٍ إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَتَوَاصَوْا بِالْحَقِّ وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ
lalle mutum yana cikin
asara. se
waɗanda
sukayi imani, suka aikata aiki me kyau, sukayi wasiyya da gaskiya, kuma sukayi
wasiya da haƙuri!!. (wato cikin
Yima ALLAH biyayya)
Duk wanda ya yi wasici da ɓarna
baza'a aikata ba!! sulhu shiyafi alheri, kubi hanyan gyara tin kafin mutuwa
tazo..
WALLAHU AALAM
Muhammad Auwal Hussain (Abu-Ja'afar)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.