Ticker

6/recent/ticker-posts

Gaba Bayan Kwana Uku

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Na ji an ce idan ka gai da mutum na kwana uku bai amsa ba saboda yana gaba da kai, to ka ƙyale shi kawai. Mene ne gaskiyar wannan?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

Ba za a yarda cewa ka ƙi cigaba da yi masa sallama ba, domin ita sallama haƙƙin musulmi ne a kan ɗan’uwansa musulmi. Abu-Hurairah (Radiyal Laahu Anhu) ya riwaito daga Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam), ya ce: ‘Haƙƙin musulmi a kan musulmi guda biyar ne. A wata riwaya, ya ce: Guda shida ne. Sai kuma ya ce:

«إِذَا لَقِيتَهُ فَسَلِّمْ عَلَيْهِ»

Idan ka haɗu da shi, ka yi masa sallama. (Sahih Al-Bukhaariy: 1240; Sahih Muslim: 2162).

Haka kuma ƙin yi masa sallamar zunubi ne da aka yi ga Allaah Ubangiji (Subhaanahu Wa Taaala), kamar yadda ƙin amsa sallamar shi ma zunubi ne da aka yi wa Ubangiji Taaala.

Kuma a ƙaidar malaman Usuul: Ita ƙofar ɓarna ƙara toshe ta da ƙanƙanta ta ake yi, ba ƙara buɗe ta da faɗaɗa ta ba.

Sannanan asarar da musulmi ke yi ta sanadin gaba da ɗan’uwansa musulmi ba ƙarama ba ce. Hatsarin da ke cikin yin gaba a tsakanin musulmi yana da yawa. Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

« تُفْتَحُ أَبْوَابُ الْجَنَّةِ يَوْمَ الاِثْنَيْنِ وَيَوْمَ الْخَمِيسِ ، فَيُغْفَرُ لِكُلِّ عَبْدٍ لاَ يُشْرِكُ بِاللَّهِ شَيْئًا ، إِلاَّ رَجُلاً كَانَتْ بَيْنَهُ وَبَيْنَ أَخِيهِ شَحْنَاءُ ، فَيُقَالُ: أَنْظِرُوا هَذَيْنِ حَتَّى يَصْطَلِحَا! أَنْظِرُوا هَذَيْنِ حَتَّى يَصْطَلِحَا! أَنْظِرُوا هَذَيْنِ حَتَّى يَصْطَلِحَا! »

Ana buɗe ƙofofin Aljannah a ranar Litini da ranar Alhamis, sai kuma a gafarta wa duk bawan da bai haɗa Allaah da komai ba (bai yi shirka ba). Sai dai mutumin da ya ke akwai gaba a tsakaninsa da ɗan uwansa, sai a ce: Ku ƙyale waɗannan biyun har sai sun sulhunta! Ku ƙyale waɗannan biyun har sai sun sulhunta!! Ku ƙyale waɗannan biyun har sai sun sulhunta!!!

 (Sahih Muslim: 6709).

Sannan kuma Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

« لاَ يَحِلُّ لِمُسْلِمٍ أَنْ يَهْجُرَ مُسْلِماً فَوْقَ ثَلاَثِ لَيَالٍ ، فَإِنْ كَانَ تَصَارَمَا فَوْقَ ثَلاَثٍ فَإِنَّهُمَا نَاكِبَانِ عَنِ الْحَقِّ مَا دَامَا عَلَى صُرَامِهِمَا ، وَأَوَّلُهُمَا فَيْئاً فَسَبْقُهُ بِالْفَىْءِ كَفَّارَتُهُ ، فَإِنْ سَلَّمَ عَلَيْهِ فَلَمْ يَرُدَّ عَلَيْهِ ، وَرَدَّ عَلَيْهِ سَلاَمَهُ ، رَدَّتْ عَلَيْهِ الْمَلاَئِكَةُ ، وَرَدَّ عَلَى الآخَرِ الشَّيْطَانُ ، فَإِنْ مَاتَا عَلَى صُرَامِهِمَا لَمْ يَجْتَمِعَا فِى الْجَنَّةِ أَبَداً »

Bai halatta wani musulmi ya ƙaurace wa wani musulmi sama da kwanaki uku ba. Idan kuwa suka yi gaba da juna na sama da kwanaki uku, to tabbas! Sun karkace daga gaskiya matuƙar dai sun tabbata a kan gabarsu. Wanda ya fi su alkhairi shi ne wanda ya fara komowa: Sai gaggawarsa wurin komowa ya zama kaffara gare shi a kan gabarsa. Idan ya yi wa ɗayan sallama amma shi bai mayar masa da sallamarsa ba, sai mala’iku su mayar masa, kuma shaiɗan ya mayar wa ɗayan. Idan kuma suka mutu a kan gabarsu, to ba za su haɗu da juna a cikin Aljannah ba! (Ahmad: 16694 ya riwaito shi, kuma Al-Albaaniy ya inganta shi a cikin As-Saheehah: 1246).

Wannan kenan.

To, don Allaah! Yaya mai imani zai ji irin waɗannan hadisan sannan ya kauce musu domin kawai wani ya faɗi abin da shi kansa bai san tabbacinsa ba, kuma maganar da ta saɓa wa ƙaidar da malamai suke gudana a kanta na rage faɗin ƙofar ɓarna?!

Wal Laahu A’lam.

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments