𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Akwai Masu Cewa Allah Yana Ko Ina, Suna Hujja Da Faɗinsa a Suratul Hadid Aya ta huɗu:
هُوَ الَّذِي خَلَقَ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٍ ثُمَّ اسْتَوَىٰ عَلَى الْعَرْشِ ۚ يَعْلَمُ مَا يَلِجُ فِي الْأَرْضِ وَمَا يَخْرُجُ مِنْهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ السَّمَاءِ وَمَا يَعْرُجُ فِيهَا ۖ وَهُوَ مَعَكُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ ۚ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ بَصِيرٌ
ShI ne wanda Ya halitta
sammai da ƙasa a cikin wasu kwãnuka shida, sa'an nan Ya
daidaitu a kan Al'arshi, Yanã
sanin abin da ke shiga cikin ƙasa
da abin da ke fita daga gare ta, da abin da ke sauka daga sama da abin da ke
hawa cikinta, kuma Shĩ yanã tareda ku duk inda kuka
kasance. Kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatãwa.
Dai Wasu Ayoyin, Yaya Abun Yake?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Allah maɗaukakin
Sarki yana Saman Al'arshi, saman dukkan halittu, a wajan Ahlussunnah
Wal-jama'a, Haka dukkan manzanni sukazo da Wannan aƙidar, Allah yana Saman Al'arshi. Kamar
Yanda ya faɗa a cikin Ayoyi maban-banta Masu yawa acikin
Alƙur'ani mai girma.
Allah ya bayyana Ƙarara ya dai-daita a saman Al'arshinsa,
dai-daituwar da ta dace da girmansa da Ɗaukakarsa,
Ba Wani Abun Halitta da yai Kama dashi wajan yanda ya dai-daita. Babu Wanda yai
kama da Allah, ko yake kama dashi.
Annabi Sallallahu Alaihi
Wasallam ya Tambayi Wata baiwa a ina Allah yake? Ta ce yana Sama, Ya ce Ni
Wanene ta ce: Manzan Allah, sai ya cewa: Uban gidanta ka 'yantata tabbas Ita
Muminace. Muslim ya ruwaito.
Wannan ya Nuna Allah yana
Sama can Saman Bakwai Saman Al'arshi sama maɗaukakiya.
Sahabbai sun haɗu
kamar yanda Manzanni Suka haɗu, akan Allah yana Sama,
Saman Al'arshi. Duk Wanda ya ce Allah yana Kowanne waje, ko baya Sama, shi
kafirine, Mai Ƙaryata Allah da
ManzanSa, da ƙaryata Ijma'in
Ahlussunnah Wal-jama'a, Kamar dariƙun
bidi'a irinsu *Jahamiyyah da Mu'utazilawa, da Makamantansu, Waɗannan
suna cikin Waɗanda sukafi kowa kafirci cikin Mutane,
saboda Inkarin sunayen Allah da Siffofinsa.
Fadin Allah maɗaukakin
Sarki acikin Suratul Mujadala aya ta 7:
أَلَمْ تَرَ أَنَّ اللَّهَ يَعْلَمُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۖ مَا يَكُونُ مِن نَّجْوَىٰ ثَلَاثَةٍ إِلَّا هُوَ رَابِعُهُمْ وَلَا خَمْسَةٍ إِلَّا هُوَ سَادِسُهُمْ وَلَا أَدْنَىٰ مِن ذَٰلِكَ وَلَا أَكْثَرَ إِلَّا هُوَ مَعَهُمْ أَيْنَ مَا كَانُوا ۖ ثُمَّ يُنَبِّئُهُم بِمَا عَمِلُوا يَوْمَ الْقِيَامَةِ ۚ إِنَّ اللَّهَ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمٌ
Ashe, ba ka ga cẽwa lalle Allah Yanã sane da abin da yake
a cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa
ba? Wata gãnãwa ta mutum uku bã zã ta kasance ba fãce Allah Shĩ ne na huɗu ɗinta,
kuma bãbu ta mutum biyar fãce Shĩ ne na shida ɗinta,
kuma babu abin da ya kãsa wannan kuma babu abin da yake mafi yawa fãce Shĩ Yanã
tãre da su duk inda suka kasance, sa'an nan Ya bã su lãbãri game da abin da
suka aikata a Rãnar ƙiyãma. Lalle Allah Masani ne ga
dukkan kõme.
Bata nufin Irin yanda ɓatattu
da 'yan bidi'a suke fassara ta, da yanda suke jefa shubuha da ruɗu a
zuƙatan Masu ƙaramin
Sani.
Abunda Ake nufi acikin Ayar shi
ne, Babu wasu mutum uku da zasu zauna suyi zance ko tattaunawa a ɓoye
asirri face sai Allah ya zama Na huɗunsu,
idan Su biyarne ko Ƙasa
da Haka ko sama da haka face Sai Allah ya Zama yana tare dasu, da iliminsa da
Buwayarsa, a duk inda Suka kasance, Babu Abunda zai ɓoyu
agareshi na Al'amarinsu, Sannan ranar Alƙiyama
Ya basu labari akan Abunda Suka aikata, na Alkhairi ko sharri, Sannan yai Musu
sakayya dashi, Tabbas Allah Masanine Akan Komai.
Wannan shi ne Abunda ayar da
Ire-irenta suke nufi, Bata cin karo da Ayoyi da Ingantattun Hadisan da suka
nunar da Allah yana Sama a saman Al'arshi, babu Abunda yake ɓuya
agareshi Na ayyukan bayi aduk inda suka aikata Wani abu, yana tare dasu da
Ilminsa da Buwayarsa.
Duk Wanda kaji yana jidali
da hayaniya akan Abunda ayoyi da Hadisan dai-duwar Allah a saman Al'arshi suka
tabbatar, inma tantirin jahile wanda ya gaji bidi'a a nonon uwarsa, ko kuma
zindiƙine Batacce wanda Allah ya Wulaƙantar dashi ta hanyar aukawa wannan
bata.
Mai Son Ƙarin bayani saiya duba Litattafan
tafsiri musamman Tafsirin ibnu kaseer ƙar-ƙashin wannan aya da Makamantanta, da
Kuma litattafan Aƙida
da Tauhidi.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.