Ticker

6/recent/ticker-posts

Na Tuba Daga Leken Tsiraicin Mutane

NA TUBA DAGA LEKEN TSIRAICIN MUTANE

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum wa rahmatullah. Malam na ga tambayar daka amsa game da masu leken tsaraicin mutane, Kuma naga amsar daka bayar. Harga Allah Nima nayi irin wannan abun Abaya wlh abun ya dameni har yanzu Malam na kasa sakewa, na tuba Amma har yanzu inata tsorata mallam mene ne mafita, saboda mutanen dana zalunta ta wannan hanyar?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Mafita ita ce ka yawaita nadama tare da neman gafarar dukkan zunubanka (Istighfari), Kaji tsoron Allah ka kyautata ayyukanka na gaba, sannan ka yawaita ayyukan alkhairi musamman ayyukan jin-kai da taimakon al'ummah domin neman kusanci zuwa ga Allah.

Sannan kaje ka nemi yafewar wadanda ka yiwa wannan laifin idan hakan bazai janyo tashin hankali ba, Koda ba tare da bayyanar musu da irin laifin da ka zaluncesu dashi ba.  Idan kuma hakan ba zata yiwu ba, ka yawaita yi musu addu'ar neman gafara misali acikin addu'o'inka ka rika cewa "YA ALLAH KA GAFARTA WA DUK MUTANEN DA NA ZALUNCESU CIKIN KUSKURE KO RASHIN SANI KODA GANGANCI, KA YAFE MUN SUMA KA YAFE MUSU LAIFUKANSU. KA SANYA ZALUNTARSU DA NAYI TA ZAMA KAFFARA AGARESU DA LADA DA DAUKAKAR DARAJA".

Allah mai yawan falala ne kuma mai jin kai ga bayinsa. In dai ka tuba tare da kyakyawar manufa kuma ka gyara ayyukanka, to tabbas Allah zai yafe maka kuma zai kankare maka zunubanka. Domin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce "ALLAH YANA KARƁAR TUBAN BAWANSA MUTUKAR DAI BAI KAI GARGARA BA (WATO MUTUKAR DAI BAI KAI LOKACIN DAF DA FITAR RANSA BA).

Allah shi yafe mana baki daya.

WALLAHU A'ALAM.

DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments