Ticker

6/recent/ticker-posts

Alkur’ani Malamin Mallammai Shaihin Da Shaihuna Ka Roko Fatawa

Citation: Bunza, A.M. (2025). Alƙurani Malamin Mallammai Shaihin Da Shaihuna Ka Roƙo Fatawa. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, 4(1), 41-47. www.doi.org/10.36349/tjllc.2025.v04i01.005.

ALƘUR’ANI MALAMIN MALLAMMAI SHAIHIN DA SHAIHUNA KA ROƘO FATAWA

Daga

Aliyu Muhammadu Bunza
Department of Nigerian Languages
Usmanu Danfodiyo University, Sokoto, Nigeria

Tsakure

Saukar Alƙur’ani na farko ya zo shekarar (610 CE), ya ƙare shekarar (622CE). Alƙur’ani an saukar da shi ga Annabi Muhammadu (SAW) ta hanyar Mala’ika Jibril. Da kalmar “Iqra” aka fara magana. Littafi ne da ke da Surori (114) da aka kasa zuwa hizifi (60). Ayoyi 6,666, kalmomi 157,935 da harufan da suka gina su 668,684; Allah Ka buwaya. Asalin harufan harshen Larabci (28) ne. Daga cikinsu akwai harufu 15 marasa masu ɗigogi, guda 13 kuma masu ɗigogi. Harufa 7 ke da ɗigo ɗaya, 3 ɗigo biyu, 2 ɗigo uku. Manyan wasula su ne “Alu Baƙi" da “Alu Ja” sai “wasulan sama da ƙasa” da “damma da shadda”. Waɗannan suke ba da damar karanta alƙur’ani ga kowa. A fassara Alƙur’ani cikin harsuna 114. A harsuna 47 kawai aka samu wallafa shi cikakke. A fagen masana, an yi tafsiran Alƙur’ani 2,700, amma 300 kawai aka samu wallafawa. A cikin harsunan Nijeriya kimanin 500, an fassara Alƙur’ani cikin fitattun harsuna cikin rubutun bokon harshe, da ajamin harshe. Daga cikinsu akwai: Hausa, Yoruba, Kanuri, Fulfulde, Nupe, Kyanganci da Igbo. A tarihance, Indiya ta fara taron gasar karatun addinai fiye da shekara 100 da suka gabata, shekarar da aka gayyato Musulmi shi ne ya zama zakara. Ta karatun Alƙur’ani an fara ta a Indonesia a shekarar 1940, sai Malaysia (1961), Saudiya ta fara a 1980. A zamanin da muke ciki (2024), Nijeriya ce gaba da yawan mahardata Alƙur’ani wanda Daular Borno ke jagoranta. Harshen da ya fi harsunan Nijeriya ga fassara Alƙur’ani shi ne Hausa. A Najeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo ta fara tsara shi a Kabi a matsayin karo na 39. Akwai buƙatar saka Alƙur’ani cikin tsarin koyarwa daga Firamare zuwa Jami’a, a ƙara fassara Alƙur’ani cikin Harsunan Nijeriya domin tsaro da kyautata shugabanci.

Fitilun Kalmomi: Alƙur’ani, Musulunci, Ƙasar Hausa, Hausawa

Gabatarwa

Masanan duniya ba su yi saɓani ba na kasancewar duniya mazaunin halittu ne da mutane ke shugabanta. Babu wai, mahaliccin mutane, mutane ya ba ragamar jagorar su kan kafa ta har ya zuwa yau. Mutanen da Allah Ya ba jagorar mutane, su ne Annabawa da manzanni. Abin ban sha’awa, kowanensu Allah na ba shi saƙo na baka ko littafen da za a aje. Al’ummar farko annabi Adamu (AS) aka turo musu da cikakken saƙon baka; al’umma ta ƙarshe kuwa (tamu) aka turo Annabi Muhammadu (SAW) da Alƙur’ani da zai shugabance mu har ranar tashin duniya. Alƙur’ani ya zo da shi, duk wani abu da ya saɓa masa kuskure ne babba, gyaran shi dole ne. tabbas Alƙur’ani ya zo da Musulunci, kuma Musulunci ya zo da Alƙur’ani ga yadda abin ya kasance.

Bayyanar Musulunci a Duniya

Dukkanin addinan da Allah Ya saukar ba su saɓa wa kyakkyawar aƙida ba. Addinin Musulunci an aiko manzonmu Muhammadu ɗan Abdullah (SAW) da shi tare da babban littafenmu Alƙur’ani. Masana tarihi sun yi kirdadon haihuwar Annabi Muhammad (SAW) cewa, ita ce ranar 12 ga Watan Rabi’ul Awwal, wato rana ta uku a watan wadda za a ce Ogusta 29, 570CE, wasu su ce, 20th April 571CE, wasu su ce, an haife shi ranar Litinin. A ganin wasu, Musulunci a yau ya kai shekaru 1,400 domin wahayin Alƙur’ani na farko ya zo a shekarar 610, sai ya yi zuwa Madina shekarar 622.

Har yanzu wasu masana tarihi suna zaton Annabi (SAW) ya karɓo Musulunci shekarar 622CE, kimanin shekaru 1,382 a yau 2024. Daga Makka Musulunci a Afirka ya fara zuwa gabanin ko’ina a duniya. Musulunci ya je a Habasha (Ethiopia) sau biyu, gabanin saukarsa a Madina. A taƙaice, ya nuna littafinmu mai tsarki Alƙur’ani da Makka da Habasha (Afirka) ya fara barbazuwa. Manzo da kansa ya kai shi Jordan, Syria, Ta’if, Madina, Jerusalem, Masjid Al-Qasra da sama ta bakwai. Musulunci ta hannun Sahabbai ya shiga Misra a zamanin sarki Muqawatis, daga nan ya zarce Afirka ta Arewa. Daga nan, ya shiga kudu da gabas na Asiya, daga nan sai India, sai Malysia, da Indonesiya, da China. ‘Yan kasuwar Afirka ta Arewa, da Senegal, su suka yaɗa Musulunci a ƙasashen Afirka. A duniyarmu ta yau, ƙasashe 49 ke da babban tasirin Musulunci a ciki; ƙasar Mauriteniya ita kaɗai ke da kashi 100 na Musulmi a duniya, kuma dukkaninsu ahalil sunnah. A ƙasarmu (Nijeriya) a ƙarni na 9th wani ɗan kasuwa Ali Ibn Ghanim shi ya kawo Musulunci a daular Kanen-Borno. A ƙasar Hausa kuwa, Sarkin Kano Muhammadu Rumfa (1463-1499) ya fara karɓa Musulunci na daula. Ko’ina Musulunci ya bayyana Alƙur’ani ne limaminsa, shi ne mamu, shi ne ladan. Cikin addinan duiya 10,000 da muke da su fitattunsu su ne: Christianity, Islam, Hinduism da Buddhism, suke da 77% na addinan duniya. Alƙur’ani ya fi su littafi raba-gardama.

Mene ne Ƙur’ani?

Kalmar “Ƙur’aani” a nahawun Larabci suna ne da aka ciro daga kalmar “aikatau” mai suna “ƙara’aa” mai nufin “a karanta” ko “a rera”. Tabbas Alƙur’ani da kansa ya ambace kalmar cikin suraa ta 9, aya ta 111, da sura ta 75, aya ta 17-18. Wasu masana sun ce, kalmar tushenta daga harshen Syriac ne wanda ya mamaye Middle East (Gabas da Tsakiya) da Estern Arabia (Gabacin Arebiya), a taƙaice shi ne harshen asali na ƙasar “Syria” wanda asalinsa daga Edissa da tarihin ya fara tun ƙarni na ɗaya. Harshen Syriac wani karin harshe ne na Aramaic da ake magana da shi har yanzu a tsakanin ƙasar Syria da Iraqi, kuma ya samu karɓuwa sosai a Middle East (Gabas ta Tsakiya). A taƙaice, kalmar “Qur’an” mai nufin (karatu da rerawa) tana da tushe daga kalmar harshen Aramaic da ake ce wa karatu: “qeryan-a”. Daga sunayen da Alƙur’ani ya ambata na kansa akwai: Al-ƙur’an, Al-Kitabu, Al-Furƙan, Tanzeel, da Al-Zikir, sun bayyana a cikin ayoyi daban-daban. A nan, za mu ga, dukkanin littafan da Allah Ya saukar karatunsu ake yi da rera su da murya mai armashi tun ƙarni na ɗaya zuwa yau (2024).

Zubi da Tsarin Alƙur’ani

Alƙur’ani malamin maluma ne mai tsarin da ya kyautu a tabbatar daga Allah yake; Mala’ika Jibrin ya sadar da shi ga Manzon Allah (SAW). Ga fitattun zubi da tsarin da ya kamata a ce zuciya ta kiyaye shi:

a.      An saukar da Alƙur’ani cikin shekara (22) daga (610CE) zuwa (632CE).

b.      An fara saukar da shi ga Manzo (SAW) yana da shekara (40) aka ƙare shekarar (632CE) shekarar da Manzo (SAW) ya rasu (ƙaura). Allahu akbar!

c.       An wakilta Mala’ika Jibrilun zuwa ga Manzo (SAW); shi kuwa Manzo (SAW) ya isar da shi ga duniya, da baki, ba a rubuce ba.

d.     Alƙur’ani na da surori (114) da Musulmi suka kasa zuwa hijihi/hizufi (60).

e.      Surorin (114) suna da ayoyi (6236) in ba a lisafa da basmala ba, in an sa ta za su kai (6348), akwai masu cewa, ayoyin (6666) saɓanin daga karatu ne, ba ƙari ko ragewa ba.

f.        Kalmomin da suka gina ayoyin (157,935) waɗanda ba a maimaita ba su ne (5277), harafohin da suka gina kalmomin (668,684).

g.      Nassoshin gaba ɗaya an kasa su gida biyu: saukan Makka da na Madina.

Ƙunshiyar Alƙur’ani

Alƙur’ani babbar makaranta ce da duk wani abu da ya shafi ilmi in ya saɓa masa dabirta ce; in ya yi daidai da shi gare shi ya samo. Daga cikin ƙunshiyar Alƙur’ani ne ilmukan namu na duniya suka samu taƙama da cigabansu. Lafiyar ƙwaƙwalwa da zuciya daga cikin Alƙur’ani masana suka gano yadda ake inganta shi. Daga cikin ƙunshiyar Alƙur’ani za mu yi duba cikin tsarinsa, da zubin nassoshinsa. Manyan abubuwa da ya kamata a kula daga ciki su ne:

a.      Cikin surorinsa (114) surar da ta fi tsawo da faɗi, ita ce “Suratul Baƙra” mai ayoyi (286).

b.      Daga cikin ayoyin surorin Alƙur’ani (114) surar da ke da ayar da ta fi kowace aya tsawo ita ce “suratul Baƙraa” ayarta ta bashi, aya ta (282).

c.       Surar da ta fi gajere ga tsawo cikin surori (114) na Alƙur’ani ita ce “Suratul Kawsar” ayoyi (3) kaɗai take da.

d.     Surar da ke da basmala biyu daga cikin surori (114) ita ce “Suratul Namal” sura ta (87) ayoyi na (30) da (90).

e.      Daga cikin surorin Alƙur’ani (114) akwai ayoyi (15) da ake sujada ga karatunsu guda (4) wajibi ne saura (11) mustahabbi.

f.        Daga cikin surorin Alƙur’ani (114) surar da ke da sunan Allah cikin kowace ayarta ita ce, “Almjujadal”.

g.      Sunayen Allah da suka fi mamaye nassoshin ayoyin Alƙur’ani su biyu ne, Al-Ghafur sau (91) da Al-Rahim sau (72).

h.      Sunan Anabin da ya yawaita cikin Alƙur’ani shi ne Musa (AS) sau (136) da Annabi Isa (AS) sau (25); shi ya sa Annabi Musa kawai ne suka yi magana fuska-da-fuska da Allah (SW).

i.        Cikin yardar Allah da ƙaddarowarsa a cikin “Suratul Tauba” babu sunan “allah” a cikin ayoyinta. Allahu akbar!

Harufan Larabci Cikin Rubutun Alƙur’ani

Alƙur’ani da baki Allah Ya ba Jibirilu (AS) domin ya sadar da shi ga Annabi (SAW) ga kunnensa bisa karanta masa shi; shi kuwa shi karantar da duniya shi. Cikin Larabci Jibirilu (AS) yake karanta wa manzo (SAW), shi kuwa Manzo (SAW) cikin Larabci yake koya wa duniya. Sanin ba kowane Balarabe ba, kuma ba kowa ke jin Larabci ba, dole a samu matsaloli cikin karantawa, da rerawa, da yau ake kira (tilawa). Abin lura a nan shi ne:

a.      Harshen Larabci yana da harufa (28) duka waɗanda ke shiga cikin kalmomin Alƙur’ani a karanta su a ji sautinsu.

b.      Larabci a lokacin ba a rubuce yake ba, ko da akwai rubutunsa kaɗan ne ƙwarai.

c.       A rubuce cikin harufan Larabci (28) fiye da rabinsu a fagen furucinsu da rubutu sun yi kusa da juna sai a samu matsalar fitar ma’ana kamar:

Ø  Harafin “ra” iri biyu ne

Ø  Harafin “sa” iri uku ne

Ø  Harafin “wa” a rubuce iri uku ne

Ø  Karafin “ha” iri uku ne

d.     Domin tabbacin ingancin karatu dole sai an yi alamomin da za a gano su, tare da sanin lokacin Manzo (SA) da Jibirilu (AS) ba a yi su ba.

Wasulan Alƙur’ani

Tabbas! Sayyidina Ali (RA) ya gayyato Abu al-Aswad al-Du’ali domin sa wa Alƙur’ani wasula. An yi matakan a matakai daban-daban. Nasarar da aka ci ita ce:

1)      Fara ƙirƙiro ɗigagga ga baƙaƙe na sama da ƙasa:

a)      akwai masu ɗigo ɗaya;

b)     akwai masu ɗigo biyu

c)      akwai masu ɗigo uku

2)      Za mu ga akwai ɗigagga (19) da za mu ce:

a)      Ɗigo ɗaya ga harufa (7)

b)     Ɗigo biyu ga harufa (3)

c)      Ɗigo uku ga harufa (2)

3)      Abin da ya biyo ɗigagga wasula na sama da ƙasa

a)      Wasalin sama

b)     Wasalin ƙasa

c)      Wasulan ƙasa

d)     Wasulan sama

4)      Rufu’a ta biyo daga cikin da nata salo

a)      Na sama ɗaya

b)     Na sama biyu

c)      Rufu’a ba ta zuwa ƙasa sai sama ɗayarta da biyunta

5)      Zancen Shadda

Shadda shi ne ɗaure harafi biyu a furce su a baki su zama ɗaya, domin su kasance aya a furuci, amma biyu a rubutu:

6)      Zancen Ɗauri:

A kowane harshe na duniya akwai ɗauri a furuci da rubutu. A Larabci ɗauri zai kasance da da’ira a sama:

7)      Babbar doka ita ce ta “alif” da aka fara yi a rubuce a littafin Allah, ita ce:

a)      Alu baƙi

b)     Alu ja (Kowanensu launi ke fayyace shi, jan tawada da baƙa)

A karatu “Alu Baƙi" shi ne sama, “Alu Ja” ƙasa. Waɗannan dokoki da alamomi (7) su suka taimaka wajen karatun Alƙur’ani ga dukkanin Musulmin duniya.

Malamin Malaman Duniya

Mutanen da suka biyo bayan saukar Alƙur’ani a duniya, shi ya karantar da su ko da ba su yi na’am da karatunsa ba. Duk wani abu da za a yi amfani ko aiki da shi, ko wani abu da yake a bangon duniya an ambace shi cikin Alƙur’ani. Ga wasu ‘yan misalai a ɗan nazarce su a hankali:

a.      Alƙur’ani ya ambaci wasu mala’iku da sunayensu, wasu kuma da ayyukansu

b.      Cikin Alƙur’ani Aljanu 29 ya ambata

c.       Sunaye ƙabilu 12 aka ambata cikin Alƙur’ani

d.     Sunayen tsirrai 22 aka ambata cikin Alƙur’ani

e.      Sunayen gulabe 4 ya ambata cikin Alƙur’ani

f.        Ya ambaci duwatsu sau 67 cikin Alƙur’ani

g.      Ya ambaci itaccen magani 10 cikin Alƙur’ani

h.      Ya ambaci abinci iri 20 cikin Alƙur’ani

i.        Alƙur’ani ya ambaci yaƙe-yaƙe 7 da ake yi

j.        Ya ambaci laifukan haddi 7 cikin Alƙur’ani

k.      Fiye da ayoyi 200 suka ambaci dabbobi

Wanda Allah Ya hore wa fahimtar Alƙur’ani zai tabbata cewa, littafin Allah bai raga komai da ke cikin duniya ba, sama da ƙasansa. Wannan shi ne dalilin yi masa take da MALAMIN MALUNMA.

Gudumawar Nijeriya ga Haɓaka Tafsirin Alƙur’ani

Aikin farko da Manzo (SAW) ya yi wa Sahabbansa shi ne fashin baƙin Alƙur’ani da Alƙur’ani da Hadisansa. Bayanin Sahabban Annabi (SAW) a kan Alƙur’ani shi ne ingantaccen tafsiri. A Afirka ba a rasa tafsirai a Habasha da Masar da Sudan da Libya da Mauritania da Morocco da sauransu. A ƙasarmu Nijeriya da wuya a ce ba a yi shi Gobir da Kabi ba gabanin jihadin ƙarni na 19th. Waɗanda ake da tabbaci su ne Tafsiran Malam Abdullahi Gwandu guda biyu, Diyaa ul Tawiili da Kifaayatul Du’afahu. Sheikh Abubakar Gumi ya yi Raddul Azhan, Malam Ahmed Helele ya yi Fatahul Basir, da sauransu. Fitattun Shehunai da suka yi tafsiri na baka sun haɗa da Shaikh Nasiru Kabara, Sheikh Dahiru Bauchi, Sheikh Ibrahim Sharif Saleh, Sheikh Sidi Attahiru Sokoto, Sheikh Malam Umar Bawa Jangwarzo Gobir da sauransu. Akwai tabbacin cewa, a wannan ƙarni na duniya babu ƙasar da ta fi Nijeriya ta Arewa mahardata Alƙur’ani musamman in an duba a Daular Borno, da Daular Kano, da Daular Zazzau, da Daular Gwandu. Waɗannan wurare sun fi ƙasar Saudiyya da Asiya da Falasɗinu da Indonesia da Aljeriya da Morocco da sauransu. Mahardata akwai tabban a da a Daular Borno da Zazzau da Kano da Kabi a shekaru (100) da suka gabata babu gidan da babu mahardaci (Alaramma) kuma babu garin da babu Gwani kuma babu zamanin da babu Gangaran har yau 2024.

Rubutun Alƙur’ani da Fassara Shi Cikin Wasu Harsuna

Duniyar mutane tana da kimanin harsuna 7500 a yau (2024). A lokacin Manzo (SAW) yawan harsunan ba su kai haka ba. Abin da magabata da masana cikin Sahabban Annabi (SAW), da Tabi’ai suke fara shi ne fassara Alƙur’ani zuwa wasu harsuna da ba Larabci ba. An fassara Alƙur’ani cikin harsunan duniya (114). Cikakken fassarar Alƙur’ani an yi shi cikin harsuna (47) na duniya. Fassara ta farko ita ce wadda Sarki Mansur (961-976) ya yi a ƙarni na 10 da 12. Ya sa fitattun masana su fassara Tafsir al-Tabari daga Larabci zuwa harshen Persian. Wasu masana na ganin akwai fiye da Tafsiran Alƙur’ani 2,770. Daga cikinsu guda 300 kawai aka wallafa. Tafsir na farko shi ne na Muhammad Ibn Jafar al-Tabari (838-823) wanda ya rubuta Tafsir Al-Tabari. Rubuce-rubucen Tafsir a duniya ya buɗe ƙofar hardar Alƙur’ani domin fitacciyar hanyar gudanar da tafsir ita ce yin tafsirin Alƙur’ani da Alƙur’ani.

Fassarar Alƙur’ani a Harsunan Nijeriya

Nijeriya tana da harsuna 500 wanda ya sa ta kasance ƙasa mai harsuna daban-daban a duniya. Ingilishi ne harshen iko amma manyan harsunanmu sun haɗa da: Hausa, Yoruba, Igbo, Fulfulde, Ibibio, Kanuri da Tiv. Daga cikin Harsunanmu an fassara Alƙur’ani da yawa: A Hausa manyan da suka yi fassarar Alƙur’ani gaba ɗaya akwai:

1)

a.      Sheikh Abubakar Gummi

b.      Sheikh Nasiru Kabara

c.       Farfesa Bello Sa’idu

d.     Farfesa Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemu

e.      Wani mafassari da bai faɗi sunansa ba

f.        Fassarar Jami’ar Masar

g.      Cikakkiyar fassara ta baki “Tafsiri/Fashin Baƙi".

2) Reverend Michael Samuel Cole, Alƙur’ani ni ede Yoruba, 1906 Published 1924, Fassara ta farko a harshen Afirka, da rubutun bokon Yoruba ba Ajami ba.

3) Sheikh Murtala Chukwuemeka a cikin harshen Igbo da rubutun boko Igbo ba Ajami ba.

4) Fassara cikin Kanuri Shetima Kawoi a 1950s cikin Ajamin Kanuri.

5) Fassarar Nupe Kuranu Tsatsana Ndagi Abdullahi cikin Ajamin Nupe.

6) Fassarar Fulani (Fulfulde) King Abdullahi Bin Abdal Aziz Al-Saudi ya wallafa shi cikin Ajami Fulfulde.

7) Aliyu Ibrahim S. Mainagge Fassarar Tafsiri Ibn Kathir (2018).

8) Wannginoore Maanaaji Qu’laanu Nder Fulfulde (2011).

Gasar Karatun Alƙur’ani

Karatun Alƙur’ani wata ibada ce babba a addinin Musulunci. Yadda ya fara a zamanin Manzo (SAW) da zamanin Sahabbai (RTAM) da baki ake karatu; da shi ake koyar da wanda ya musullunta baki da baki. Da lokaci ya yi tsawo Musulunci ya barbazu a duniyar mutane, salon koyar da karantar da Alƙur’ani ya bambanta daga wata ƙabila zuwa wata, ko daga wata ƙasa zuwa wata. A Nijeriya ta Arewa, musamman ƙasar Hausa ga matakin da ake hawa:

a.      Koyar da yaro ko babba karatun hijihi 1-2 da ka

b.      Koyar da harufan Larabci a rubuce daga malami daga farfaru zuwa babbaƙu.

c.       Koyar da karatun daga rubutun da malami ya yi a allo zuwa hizo 2-5

d.     Koyar da yaro rubutu da hannunsa daga hijihi 1-60.

e.      Koyar da karatun Alƙur’ani daga rubutun da aka yi wa Alƙur’ani kai tsaye (Taƙarali)

f.        Karanta Alƙur’ani daga farkonsa zuwa ƙarshe ana kallon nassoshi rubuce a littafi.

g.      Koyar da hardarsa daga farko zuwa ƙarshe tare da kulawar malami.

h.      Tabbata ya iya harda kai tsaye babu kurakurai ya zama “Alarama”.

i.        Koyar da rubuta Alƙur’ani da hannu ba tare da an ɗauko shi ba, wato da kai, an zama “Gwani” ke nan.

j.        Rubuta Alƙur’ani sau bakwai babu kure ga kowane an zama GANGARAM. An ce akwai MAHIRU gaba, babu tabbas.

k.      Shimfiɗa buzun koyar da Alarama da Gwani bita da biyar ƙididdigar Alƙur’ani.

Tarihin Karatun Alƙur’ani a Fagen Tantance Gwani

Taron karatun Alƙur’ani a matsayin fagen fito da gwani fitacce a harda, ba Nijeriya aka fara yin sa ba. An fara yin sa a Indonesia a shekarar 1940s, aka yi shi a Malaysia 1961, a ƙasar Saudiyya a shekarar 1980, ita ce musabaƙa ta 44, wato an fara ta a shekarar 1980 a ƙarƙashin Ma’aikatar kula da harkokin Addini. Sai bayan shekaru (6) aka fara musabaƙa a Nijeirya wato 1986. Ga alama, tsoron da Musulmi suka ji na ganin ba a ba Alƙur’ani wani bagiren zama ba a tsawon ilmin boko, suke ganin dole a yi fito-na-fito ga masu ƙoƙarin taushe Musulmi. Tabban! Ko ba a yaƙe mu da makamai ba, hana Alƙur’ani zama a zukatanmu wata nasara ce babba ga maƙiyanmu a kanmu. Harda tana da shekaru da idan aka zarce su, da wuya ta zauna garau a ƙwaƙwalwa masu yin ta. Duk wani cigaba da wayewar kai, da tsaro, da tattalin arziki, aka samu in babu Alƙur’ani ci baya zai biyo baya. Da za a samu mahardata dubu (1000) aka bincika za a ga fiye da ɗari tara da saba’in (970) tun suna yara suka koyi hardar suka same ta. Ai ƙwararrun malamai sun ce, ana iya hardace Alƙur’ani cikin shekara 2-5.

Tarihin Musabaƙa a Nijeriya

A nawa tunani tushen musabaƙa wasu dabaru ne da jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato. Ta ƙago domin ƙara haɗin kan Musulmi, ƙarfafa harda ga yara maza da mata, soke ta’addanci, farfaɗo zuciyar Musulmi kada jihadi ya yi masa girshi, ɗaukaka Nijeriya cikin duniyar zamaninta da sauransu.

Shekarun Musabaƙa a Tarihance

S/N

Jiha

Hijira

Shekara

Adadi

1.       

Sokoto

1006AH

1986

3

2.       

Borno

1407AH

1987

1

3.       

Kano

1408AH

1988

3

4.       

Oyo

1409AH

1989

1

5.       

Bauchi

1410AH

1990

3

6.       

Plateau

1411AH

1991

1

7.       

Lagos

1412AH

1992

2

8.       

Katsina

1413AH

1993

3

9.       

Niger

1414AH

1994

1

10.   

Kaduna

1415AH

1995

2

11.   

FCT

1416AH

1996

1

12.   

Ogun

1417AH

1997

1

13.   

Adamawa

1419AH

1998/1999

1

14.   

Kwara

1420AH

2000

2

15.   

Sokoto

1421AH

2001

3

16.   

Zamfara

1422AH

2002

3

17.   

Nasarawa

1423AH

2003

2

18.   

Yobe

1424AH

2003/2004

2

19.   

Kebbi

1425AH

2004

2

20.   

Kano

1426AH

2005

3

21.   

Bauchi

1427AH

2006

3

22.   

Kaduna

1428AH

2007

2

23.   

Edo

1430AH

2008/2009

2

24.   

Sokoto

1431AH

2010

3

25.   

Jigawa

1432AH

2011

2

26.   

Katsina

1433AH

2012

3

27.   

Zamfara

1434AH

2013

2

28.   

Jigawa

14435H

2014

2

29.   

Edo

1436AH

2015

1

30.   

Nasarawa

1437AH

2016

2

31.   

Kwara

1438AH

2017

1

32.   

Katsina

1439AH

2018

3

33.   

Gombe

1440AH

2019

1

34.   

Lagos

1441AH

2020

2

35.   

Kano

1442AH

2021

3

36.   

Bauchi

1443AH

2021/2022

3

37.   

Zamfara

1444AH

2022

3

38.   

Yobe

1445AH

2023

2

39.   

Kebbi

1446AH

2024

2

 

Sakamakon Bincike

A farfajiyar addinin Musulunci Alƙur’ani shi ne Malamin Malanmai wanda duk bai fahince shi ba, ba Malan ba ne ko da ana kiran sa UZTAZ. Kasancewar Alƙur’ani tsare a zukatan muminai shi ya hana addininsu ya rafashe. A tarihin tattara masu addini kowa ya fara karanta addininsa ko ya rena saƙonsa, ina jin a ƙasar Indiya aka fara shi shekaru masu yawa tun Musulmi ba su yi tunanin tsara musabaƙa ba. An ce, ba su taɓa sa Musulmai ba, sai shekarar aka kira Musulmi su zo su cika tattare da ba su da yawa a Indiya. Da aka zo suka ce Musulmi ya fara. Ya hau ya fara da “Suratul Rahman”, da ya kamma kowa ya zauna. Aka kira na gaba ya ce, wallahi ba zai je a yi dariyarsa ba. Wannan ya sa wasu suka shiga Musulunci kai tsaye. Wannan ya sa na gano MUSABAƘA wani karatu ne mai koyar da mai karatu, da maras karatu, karatu. Allah Ya yi muna jagora.

Naɗewa

Ɗaya daga cikin zambar da Mulkin Mallaka ya yi muna shi ne, haɓaka karatun boko da rusa karatun Alƙur’ani don kar a yi jihadi da su. A halin da muke ciki yanzu gudunmuwar Alƙur’ani ga rayuwarmu ya fi na boko. Ta’addanci, da yaƙe-yaƙe, da rushewar tarbiya, da sace-sace, da yaudara, da ƙabilanci, da girman kai jahiltar Alƙur’ani ya haddasa su. Babban mataki da ya kyauta mu ɗauka shi ne, a fere wa Alƙur’ani babban wuri cikin manhajar koyar da yaranmu tun daga Firamare har ya zuwa Jami’a. Matuƙar ba a yi fito-na-fito da makircin bokon Ingilishi ba, zaman lafiya ya ƙare a rayuwarmu. Alah Ya yi mana jagora. Amin.

Manazarta

Adamu, M. (1978). The Hausa factor in West African history. Zaria: ABU Press.

Ajayi, J. F. A. (1967). One thousand years of West African history. Ibadan: University Press.

Algar, H. (1980). The Islamic revolution in Iran. London: Open Press University.

Ali, A. Y. (1968). Translation and commentary of the Holy Qur’an. Leicester: Islamic Foundation UK.

Bello, M. (1964). Infaq al-Maisur. Cairo: Dar wa Matba al-Sha’aby.

Buhari, I. (1986). Sahih Albukhaari. Lebanon: Dar-al-Arabia.

Bunza, A. M. (2023). Bahaushen Salo na Taskace Alƙurani da Kiyayeshe. Takarda a Makarantar Yara Mahardata Bunza.

Bunza, A. M. (2024). Karatun Allo Ƙasar Hausa. Takarda, Makarantar Atta’aa’unu Jega.

Clarke, P. B. (1982). West Africa and Islam. Scotland: Thomson Litho Ltd.

Dokaji, A. M. (1978). Kano ta Dabo Ci Gari. Zaria: NNPC.

Gada, A. M. (2000). Islamic scholarship in Hausaland from 16th to the 18th C: A case of Katsina, Gobir, Zamfara and Kebbi (PhD thesis). Usmanu Danfodiyo University, Sokoto.

Gumbi, M. S. (1986). Rayuwar Sheikh Abubakar Mahmud Gumi. Kaduna: N.N.P.C. Nigeria.

Ilori, A. A. (1978). Al-Islam in Nigeria.

Muhammad, A. Y. (2003). Ilm-Al-Tajwid and Qur’anic recitation competition in Northern Nigeria (PhD thesis). Usmanu Danfodiyo University, Sokoto.

Palmer, H. R. (1967). Sudanes memoire (Vol. III). Frankeass.

Redha, M. (2006). Imam Ali Ibn, Abu Talib the fourth Caliph. Lebanon: Daarul al Kutbul Ilmiyya.

Tsiga, I. A., & Adamu, A. U. (Eds.). (1997). Islam and history of learning in Katsina. Ibadan: Spectrum Books Limited.

Zaharadden, M. S. (n.d.). The place of mosque in the history of Kano. In Studies in the history of Kano.

Post a Comment

0 Comments