YADDA ALKALI ABUBAKAR AL-BAQILLANIY YA KARE MATAR ANNABI (SAW) A'ISHA (RA) A FADAR PAPAROMA
Abu ne sananne makiya Addinin Muslunci cikin Munafukai da Yahudawa da Nasara da Rafidha 'Yan Shi'a da Mulhidai sun yi gangami sun yi taron dangi sun hada karfi da karfe wajen cin mutuncin Annabi (saw) ta hanyar ba ta shimfidarsa da jifan matarsa A'isha (ra) da alfasha, don su aibanta Annabi (saw) su aibanta Addinin da ya zo da shi.
Wannan ya sa
wani Pastor a fadar Paparoma ya samu daman kai farmaki ga Addinin Muslunci a
gaban Alkali Abubakar Al-Baqillaniy, sai ya jefo tambaya a kan haka. To amma
bari ka ji martanin da Alkali Abubakar Al-Baqillaniy ya mayar masa:
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Mata ne biyu aka danganta musu alfasha; Maryam da
A'isha, amma sai Allah ya wanke su.
Ita dai
A'isha (ra) tana da miji, kuma ba a ga ta zo da d'a ba. Amma ita kuma Maryam
(ra) ta zo da d'a, kuma kowa ya san ba ta da miji.
Saboda haka,
in tuhuma ce, wa ya fi kusa da tuhuma tsakanin mace mai miji da ba ta zo da d'a
ba, da kuma mace maras miji, amma sai ga ta da d'a a hanu?
Don haka
A'isha (ra) ita ta fi nisa da wannar tuhuma, duk da cewa; dukansu biyu sun
kubuta daga wannar tuhuma ta karya. Amma idan hakan ya fado a tunanin mai
lalatacciyar kwakwalwa, to zai fi tuhumar Maryam (ra) Uwar Isa Al-Masihu (as)
fiye da A'isha (ra).
Amma mu a
wajenmu, dukkansu biyu sun tsarkaka daga aikata alfashar da aka tuhume su da
ita. Allah ya wanke su daga saman bakwai.
Amma ku kun
tuhumi wacce take da miji kuma ba ta zo da d'a ba, amma mu kuma mun wanke wacce
ba ta da miji amma ta zo da d'a.
Sai Paparoma
ya ce: Kai Pastor, shin kana da jawabi a kan wannar amsa?
Sai ya
zazzare idanu, ya rasa abin fada 😅.
Ai daga nan
sai majalisi ya watse!
Akwai wata
tambaya da Wazirin Paparoma ya yi wa Alkali Abubakar Al-Baqillaniy a gefe ya ce
masa: Ku Musulmai kuna da kabilanci da ta'assubanci. Me ya sa kuke halasta wa
kawunanku auren mata Yahudawa da Kiristoci amma kuna haramta a auri naku matan,
miye dalili?
Sai Alkali Abubakar
Al-Baqillaniy ya ce: Mu muna auren mata Yahudawa ne saboda mun yi imani da
Annabi Musa (as), muna auren mata Kiristoci saboda mun yi imani da Annabi Isa
(as). Ku ma duk lokacin da kuka yi imani da Annabi Muhammad (saw) to ku zo mu
aura muku 'ya'yanmu mata.
Da aka sake
haduwa a zama na uku, sai Alkali Abubakar Al-Baqillaniy ya kai mummunan farmaki
ga Paparoma ya ce masa: Me ya sa Allah ya hade da mutum (Christ's Humanity and
Divinity, Hypostatic union), ta yaya za ka mana bayani har mu fahimci hakan?
Sai Paparoma
ya ce: Ai abu ne mai sauki, ma'ana Allah yana da surori guda biyu; daya ta
allantaka wato ta Uba, daya kuma ta mutuntaka, wato ta 'Da. Kuma ya yi haka ne
kawai don yana so ya tsiratar da mutane daga halaka.
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Shin ya san cewa; za a kashe shi, a giciye shi
(Cross of Jesus) a yi masa haka?
Idan ka ce
bai san Yahudawa za su yi masa haka ba, to kenan shi ba Allah ba ne kuma ba
d'an Allah ba. Saboda ba zai yiwu a ce Allah bai san gaibi ba.
In kuma ya
san da hakan, amma ya yarda aka yi masa haka bisa saninsa to ba shi da hikima,
saboda hikima tana hana mutum ya afka cikin bala'i. In kuwa ba shi da hikima to
shi ba Allah ba ne ba kuma d'an Allah ba.
Nan da nan
Paparoma ya rikice ya rasa abin fada.
Daga nan sai
aka dage zaman.
Sai Paparoma
ya yi alkawari ga Alkali Abubakar Al-Baqillaniy cewa za su sake haduwa a taro
na musamman cikin tarukan Addinin Kiristanci.
Da ranar ta
zo, Alkali Abubakar Al-Baqillaniy ya halarci wajen taron, taro ya yi taro, an
kawata wajen yadda ya kamata. Sai Paparoma ya girmama Alkali Abubakar
Al-Baqillaniy ya ba shi kujera kusa da shi.
Suna zaune
bisa wannan hali sai ga can babban Pastor (Patriarch) ya iso. Kuma da ma
Paparoma ya fadakar da shi a kan ya kiyayi kaifin basirar Alkali Abubakar
Al-Baqillaniy, ya ce masa: Ka kiyaye shi, kuma ka zama a fadake, don kar ya
disga ka a cikin jama'a.
Sai ga shi
ya iso cikin tawagarsa, ana biye da shi, dogarawa suna dauke da Bible, ana bin
bayansa da turaren wuta, yana isowa wajen aka tashi tsaye don girmama shi. Sai
Paparoma ya ba shi wurin zama a kujerar gefe da shi. Sai ya fiskanci Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: wannan shi ne shugaban fastoci (patriarch),
jagoran Addini, waliyyin Kiristoci.
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya gaishe shi, ya ce: yaya iyalai, yaya yara?
Nan da nan
taro kaure da mamaki, kowa ya murtuke fiska, suna mamakin wannar tambaya, suna
inkari ga Alkali Abubakar Al-Baqillaniy.
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Mene ne abin inkari a cikin maganata?
Za mu karasa
insha Allahu.
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.