Ticker

6/recent/ticker-posts

Wacce Addu'a Zan Yi Abin Da Zan Haifa Dan Ya Zama Nagari

WACCE ADDU'A ZAN YI ABIN DA ZAN HAIFA ƊAN YA ZAMA NAGARI?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalam alaikum yan'uwana musulmi Dan Allah inada tambaya ne karku shareni Dan Allah Na kasance ina da ciki ne, kuma ina so abunda Zan Haifa ya kasance nagari Kuma Wanda yakeda ilimin addini ina so ya kasance me tarbiya da tsoron Allah meya kamata na rikayi kafin na haihu saboda yanzu inada ciki wata biyu. Dan Girman Allah Karku Shareni

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumusalam warahmatallahi wabarakatuh.

Allah Ya Baki Lafiya Dake Da Abin da Yake Cikinki. Sababin Farko Shine Kisamu Keda Megidanki Duk Abin da Zakici Ko Sha Ya Baki Halak, Shiyasa Akeso Mace Tagari A Kullin Ko a Sati Sau 2 Tana Tinatarda Mijinta Yaji Tsoron Allah A Wajen Nemansa, Hakan Ba Karamin Tasiri Yake A Zuciyar Namiji ba, Wannan Shine Babban Abu Daza Kiwa Kanki Domin Ittifaqan Duk Mutumin Da aka Gina Jikinsa Da Haram Baya Albarka, Saboda Faɗin Ma'aikin Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Mutumin Da Abincinsa Haram Ruwan Shansa Haram Tufafinsa Haram Yakoshi (Yagirma Da Haram) Tayaya Zaiyi Addu'a Ta Karɓu? (Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam) neYa Fadi Haka, Dan Haka Saimu Kula Kwarai, Sannan Kofar Tuba Kullin Buɗe Take.

Da Hakane Malamai Suke Ganin Cewa Basai Mutum Ya Fito Duniya ba Za a Fara Masa Tarbiya Tin Yana Cikima Za a yi Masa, Haɗe da Kiyaye Addu'o'i Kafin Fara Saduwa.

Sannan Kema Kiyi Kokari Ki Kusanci Allah Sosai, Ki Hakura Kirage Jin Kade-Kade Da Waqe-waqe, Ki yawaita Ibada, Karatun Alkur'ani, Sallah, Zikirai Da Sauransu, Kina Addu'a, Akan Allah Ya Raya Miki Abin Cikinki Yayi Masa Albarka, Yabaki Lafiya Ki Haifeshi Kalau.

Ranar Da aka Haifeshi Malamai Masana Dubbun Nabawi Sukace A Samu Dabino Irin Ajwad, Sai A Tauna A Samu A Fara Bashi Yawun Ruwan Dabinon Nan Yashiga Cikinsa Koda Kaɗan ne, In sha Allah, Allah Zai Bashi Fahimta Da Kaifin Basira. Bayan Wannan Bayani Ba Wata Kebantacciyar Addu'a Da aka Rawaito, Babban Abu Shine Idan Kin Gyara Tsakaninki Da Allah To Tabbas Addu'arki Ga Ɗanki Kowace Iri Kikayi Masa Da Kowane Yare To Batada Hijabi Wurin Allah. Allah Ya Baki Lafiya Dakeda Abin da Ke Cikinki. Allah yasa ki sauka lafiya.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Fadakarwa, Ilimantarwa da tunatarwa...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments