𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Wa Ramatullahi Allah ya gafarta malam barka da warhaka, Allah shi qara yi maka jagoranci ya kuma saka maka da mafificin alkhairinSa akan irin qoqarin da ka ke yi amin. malam don ALLAH ina son ataimaka a yi min Qarin haske akan matsayin bukin saukar al-qur'ni mai girma da kuma falalar yanka dabba yayin addu'ar saukar. na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus
salam wa rahmatullahi wa barakatuhu:-
Hakika
Addinin mu na Islama, addini ne wanda komai nasa yake tafe cikin tsari da kuma
dokokin Allah. Kuma Allah ya halasta mana mu nuna Murnar mu da kuma godiyar mu
bisa dukkan wata ni'ima wacce yayi mana. Allah yana cewa;
وَاشْكُرُوا نِعْمَتَ اللَّهِ إِن كُنتُمْ إِيَّاهُ تَعْبُدُونَ
"KU
GODE MA NI'IMAR ALLAH IN HAR KUN KASANCE GARE SHI KUKE YIN BAUTA".
(Suratun Nahli ayah ta 144).
Daga cikin
irin waɗannan ni'imomin
akwai, Aure, Haihuwa, tarewa a sabon gida, Samun lafiya daga wata jinya, Dawowa
daga wata tafiya, Kammala Hadda ko kuma Saukar Alqur'ani, da sauransu. Kuma
mutum zai iya yin wannan godiyar ta hanyar yin wata ibadah ta musamman kamar,
salloli, Azumin tadawwu'i, Yanka dabba domin Allah, ko kuma kiran mutane ka
ciyar da su domin Allah.
A cikin
Tafseerin Suratul Kauthar, Ibnu Taymiyyah yana cewa, "Allah yayi ma
ManzonSa babbar baiwa tunda ya ba shi alkausara. Shi ya sa ya umurce shi da yin
godiya ta hanyar yin Mafificiyar ibadar da ake yi da jiki, wato sallah. Sannan
da kuma Mafificiyar ibadar da za a yi da kuɗi. Ita ce YANKA
domin Allah. Saboda irin wannan godiyar ne Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa
Sallam) ya yanka Rakumma 63 a lokacin hajjin ban-kwana. (A duba Majmu'ul
Fataawah juzu'i na 16, shafi na 532).
Ya halatta
(Mustahabbi ne) mutum ya tara mutane ya ciyar da su, ko kuma yayi yanka ya
sadakar da naman domin nuna murnar sa da godiyar sa ga Allah a bisa ni'imar
Yaron sa ya haddace Alqur'ani, ko kuma ya sauke karatu.
Amma akan
samu kuskuren fahimta daga wasu mutanen, zaka ga suna cewa wai idan ba a yima
yaro wannan sadakar ba, wani mummunan abu zai same shi ko kuma zai haukace.
Wannan ba gaskiya bane.
Hasali ma
Qudurce hakan Shirka ne. Kuma in dai mutum ya kudurce haka toh bai halatta yayi
yankan ba. Kuma idan yayi ma bai halatta a ci naman ba. Don Qarin haske a duba,
ALMAUSU'ATUL FIQHIYYAH, juzu'i na 26 shafi na 180-181. FATAWAL LAJNAH ADDA'IMA
juzu'i na 1 shafi na 114.
Sannan bai
Halatta ace Baban ki bai da Halin yi miki Ƴanka, bai da
Halin yi Siyo Shinkafa da sauran Abunda Za a yi Wannan hidimar da shi, a Saka
Shi Dole-dole Sai ya Karɓo Bashi a ko ina ya zo ya Haɗa Karya da Gaskiya
domin a yi Buƙin Saukar Al Qur'ani ba. Idan bai da shi, mahaifiyar ki
ma ba ta da shi, Shikenan ba Dole bane wai sai kun karɓo bashi domin yin
bukin Saukar Al Qur'ani ba. Idan an yi haka an koma wani Ɓangaren da
Shari'a bai yarda da shi ba.
Sannan
Wannan bukin a yi Shi domin Allah ya Halatta, amma in dai Za a yi shi wai domin
ai ƴar Uwata ma ta yi ko ai Yaran su wane ma an yi musu, kema
ki ce dole sai na yi kuma sai na yi Abun da ya fi nata wanda zai burge duk
wanda ya zo gurin saukar, toh Gaskiya bai Halatta ba, an shigar da RIYA a Cikin
sa da Hasada da kyamaci da son zuciya.
Kuma in dai Za
a haɗa Mata da Maza
sannan a Sanya Suturar da Sharia bai yarda da shi ba, duk Wannan bai Halatta
ace an yi Saukar Alqur'ani ba. Saboda Haka idan mutum zai yi toh ya tabbatar
cewa yayi shi abisa tsari kamar yadda bayani ya gabata a Sama bawai cewa na ga
wasu sun yi kema ki ce sai kin yiwa Yaran ki, ko kema sai kin yi idan kin sauke
ba Kuskure ne wannan.
Idan
Mahaifin ki ko mahaifiyar ki ko ke kanki, duk kuna da Wadatar yi sai ku yi har
da ƴankar a rabawa Jama'a Sadaka a kira Jama'a su ci su Sha a
yi miki fatan Alkhairi, idan babu sai a Siya Shinkafa kawai ba tare da nama ko
Yanka ba, a Dafa a raba kowa ya ci Shikenan, idan babu Wannan ma Shikenan sai a
hakura ba sai an takura mahaifi ko mahaifiya ace dole a karɓo bashi ba an yi
ba.
Sannan kuma
a yi RIYA? Babu Haɗa Mata da Maza a gurin, Babu Sanya Suturar da Addinin ki
bai yarda da shi ba, sannan za ki yi ne domin Allah bawai don wani yayi ko wasu
an yi musu ba, sannan idan kina da hali ne za ki yi bawai ku karɓo bashi ki ce dole
dole sai kin yi ba. idan hakane yadda na lissafa toh ya halatta, saɓanin Wannan toh
gaskiya bai Halatta ba a hakura kawai ya fi.
WALLAHU
A'ALAM
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.