Ticker

6/recent/ticker-posts

Matsayi Da Matsalolin Rayuwar Mata: Nazari Daga Rubutattun Wakoki Na Mata

Citation: Koko, H.S. (2024). Matsayi da Matsalolin Rayuwar Mata: Nazari DagaRubutattun Waƙoƙi na Mata. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 224-232. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.027.

MATSAYI DA MATSALOLIN RAYUWAR MATA: NAZARI DAGA RUBUTATTUN WAƘOƘI NA MATA

Hadiza Salihu Koko
Department of Hausa
Shehu Shagari College of Education, Sokoto

Tsakure:

Mata sun daɗe a harakar adabi, hasali ma da su aka fara, da su aka ci gaba da yi, kuma har yanzu da su ake yi. Mata sun fara rubutu tun lokacin Shehu Ɗanfodiyo, watau 1820, lokacin da Nana Asma’u ‘yar Shehu take rubutu a kan abubuwan da suka shafi addini. Daga cikin rubutunta akwai waƙa wadda ta rubuta a cikin harsunan Larabci da Fulatanci da Ajamin Hausa. Ko a wannan lokaci ta yi waƙe a kan abubuwa da dama, kama daga wa’azi da faɗakarwa da bege da jan hankali zuwa ga al’ummar musulmi musamman ga mata ‘yan uwanta. Don haka, rubutun waƙa ga mata ba sabon abu ba ne yana da daɗaɗɗen tarihi. Bayan su Nana Asma’u, mata sun ci gaba da rubuta waƙoƙi a kan fannonin rayuwa daban daban, kuma a ciki sukan mayar da hankalinsu a kan matsayi da matsalolin mata da al’amurransu tare da yin gargaɗi da faɗakarwa ga jinsin nasu na mata. Wannan muƙala mai taken Matsayi da Matsalolin Rayuwar Mata: Nazari Daga Rubutattun Waƙoƙi na Mata, ta yi nazari ne a kan yadda mata masu rubuta waƙa ke fitowa da irin matsayi da matsalolin da mata ‘yan uwansu ke fuskanta a cikin rubutattun waƙoƙin nasu. An kawo tarihin rubutun waƙa ga mata da matsayin da suke ba jinsinsu na mata da kuma matsalolin mata na rayuwa waɗanda mata ne kaɗai suka san su sosai, kuma su ke iya fito da su. Dukkan misalan da aka kawo daga rubutattun waƙoƙin da mata suka rubuta ne. Daga ƙarshe an gano cewa mata suna fito da mata a matsayin masu daraja da mutunci har dai in sun kama kansu, kuma sun dage da yin sana’a da neman ilimi da neman na kai wanda zai sa su yi mutunci ga idon mutane. An kawo shawarwari a kan yadda za a inganta rubutun mata na waƙa, a fito da su a kuma yi nazarin su a makarantu da wajen tarukan ƙara wa juna sani, don su samu karɓuwa kamar takwarorin su maza.

Fitilun Kalmomi: matsayi, matsaloli, rayuwar mata, rubutattun waƙoƙi

Gabatarwa

Bayan rubuce-rubucen da su Nana Asma’u da suka yi da Ajami, ba a samu wani rubutun mace ba, sai bayan da Turawa suka shigo Ƙasar Hausa suka buɗe makarantu a shekarar 1905. Ko a wannan lokaci mata sun daɗe ba su fara rubutu waƙa da boko ba, saboda ko makarantar mata ta boko daga baya aka buɗe ta. Al’ummar Hausawa kuwa ba su ɗauki ilimin mata na boko a matsayin wani abu mai muhimmanci ba a wannan lokacin, sun ajiye su a matsayin masu rauni da rashin basira da tsananin kishi da gulma, (Jibril, 1995). Wannan naƙasu na rashin samun ilimin boko ga mata da wuri yasa har yanzu ba su kai ga takwarorinsu maza ba wajen yawa da ƙwarewa ga rubuta waƙa.

 Wannan rashin ilimi ga mata ya taimaka wajen rashin jin muryarsu a fagen rubutaccen adabi, sai maza suka mamaye wannan fage har tsawon shekaru 47, (Ibrahim, 2010).

Kasancewar maza ne suka kakace wajen rubuce-rubuce na boko tun tashin farko, yasa suna fitar da mata a matsayin da bai dace ba ko suka mayar da su kurame waɗanda ba za a ji muryarsu ba. Wannan ta sasai mata suka miƙe tsaye ƙem wajen fuskantar matsalolin rayuwarsu ta hanyar jajircewa, domin ganin sun bi matakan cimma gurin rayuwa. Ɗaya daga cikin matakan shi ne ta hanyar adabi, inda suka bijiro da rubuce-rubuce domin ceto mata ‘yan’uwansu daga matsayin da ake ba su zuwa wani matsayi na daban da suke ganin ya dace a ce tun tuni ana fito da mata da shi. Da haka mata suka fara nuna mace a matsayin mai daraja da kuma muhimmanci ga al’umma. Sun gina wannan ra’ayi a sassan adabinsu daban-daban na Hausa kama daga rubutattar waƙa da rubutattar wasan kwaikwayo da rubutun zube da sauran rubuce-rubucensu na yau da kullum.

Wannan matsayin rayuwa da matsaloli da mata ke fito da mata ‘yan uwansu da shi ne wannan muƙala ta duba, tare da kawo misalai daga waƙoƙin da mata suka rubuta.

Tarihin Rubutun Waƙa Ga Mata

Rubutaccen adabi ko adabin zamani, shi ne wanda aka samu bayan shigowar baƙi a ƙasar Hausa. Asalinsa a rubuce yake, saboda sai da Hausawa suka samu ilimin addini da boko sannan suka fara karatu da rubutu har suka san su adana wani abu cikin rubutu. An fara ne da rubutun Ajami wato rubuta sautukan Hausa da haruffan Larabci. Daga baya aka samu rubuta sautukan da haruffan Romanci wanda ake kira boko. Wannan adabin ne ake kira adabin zamani saboda yana tafe ne da zamani. Sassansa sun haɗa da rubutattar waƙa (tun kafin jihadi) da rubutattar wasan kwaikwayo (1930s) da rubutun zube (1933). Duk wani abu da aka gani na adabi a rubuce wanda ba waɗannan ba to, adabin baka ne aka rubuta domin a adana shi.

Idan aka gangaro nan Afirika, sai a ce matan da suka fara rubutu a kan matsalolin mata musamman a waƙa su ne, su Nana Asma’u ‘yar Shehu Ɗanfodiyo da sauran mata, su ke rubuta waƙoƙi a harshen Fulatanci da Larabci da Hausa (ajami) waɗanda ke da ilimin rubuta waƙa tun a shekarar 1820. Waƙoƙin sun danganci matsalolin rayuwarsu, burace-buracensu da matsayinsu a al’umma. Rubuce-rubucen Asma’u ya haɗa da fannonin ilimi da fiƙihu da madahu da tauhidi da yabo da bege da addu’o’i har da siyasa, (Boyd da Mack, 2013). Tun a wannan lokaci ake cin gajiyar Asma’u ‘yar Shehu ta hanyar shirin ilimin mata na ‘Yantaru, inda take da ƙungiyoyi na mata a birane da ƙauyuka ƙarƙashin jagorancin Jaji wadda ke zuwa gida-gida suna ilmantar da mata addininsu da faɗakar da su a kan zamantakewa ta hanyar waƙa, (Boyd da Mack, 1999:9).

Nana Asma’u ta kalli mata a cikin waƙoƙinta a matsayin masu daraja da muhimmanci don haka ta yi kira da a ba su ilimin addini domin a ci moriyarsu. Idan suka sami ilimin suna amfani da shi su yi wa addini aiki da al’umma. Ta yi hakan ne ta hanyar ‘Yantaru da take koya wa karatun addini ta hanyar waƙa, su kuwa su hardace, su je gidaje inda mata suna rerawa don su fitar da su duhun jahilci. Ta jinjina wa irin waɗannan mata a cikin waƙarta ta Tuwassali ga Mata Masu Albarka (1837), inda ta ambaci matan da suka taimaka wa addinin Musulunci saboda ƙwazo da ilimin da suka samu kamar su Joɗa Kanwuri da “Yar Hudu da Habiba da sauransu.

Bayan rasuwar Nana Asma’u a shekarar 1865, an samu wasu mata da suka biyo bayanta, kuma suka ci gaba da mayar da hankali a wajen rubutunsu na waƙoƙi ga al’amurran da suka shafi addini, kama daga wayar da kan al’umma da neman ilimin addini musamman ga mata da yin wa’azi da fiƙihu da siyasa da zamantakewa. Waɗannan mata, kamar yadda Modibbo Kilo ta zayyano wasu daga cikinsu har zuwa ga ita kanta Kilon, a cikin waƙarta ta Hijira da Zaman Modibbo Kilo A Makkah inda take cewa:

Farkon nufa tabsir ga matan Sakkwato,

Ku tsaya ku saurara fa kaziban wuri.

Babbaɗ ɗiya ita matat Tafa,

Da Uwag-gari da Uwad-daje yaransa shi.

Baicin su Dudu, ɗiya ta Abdullahi kau,

 Mata ta Landijo fa ɗanai shahidi.

Sai Ukhitiya ‘yas Sambo sai Janajo ji,

 Ita ad ɗiya matat Tafa Mutafannini.

Bayan su Matar-Modi bint Uwad-Daje,

 Umrinta haƙƙan babu bidi’a zahiri.

Baicin su Dikko ɗiya ta Ahmadu Gwandu ta,

 Haifan Basharun Ukhtiya da Aliyu shi.

Zamaninta Habsatu tay yi gwaggo amaliya,

 Haifan fa malam Mani ta Mutafannini.

Haka nan fa Hauwa ɗiya ta Abdulƙadir,

 Baban fa malam Bube na mashahuri.

Bayansu Saudatu ta Kilon Mahmudu ji,

 Alƙali Ma’aruf na kau addini.

(Mdibbo Kilo: Waƙar Hijira da Zaman Modibbo Kilo a Makkah).

Daga waɗannan baitoci an fahimci matan da suka ci gaba da gudanar da rubuce-rubuce na waƙoƙi, da sauran al’amurran addini bayan gushewar Nana Asma’u. An zayyano su Khadija (matat Tafa) ƙanwar Nana Asma’u da Maryam (Uwad-Daje) da Maryamu (Tamodi) da Dudu ɗiyar Abdullahin Gwandu da Aishatu (Utiya) da Dikko da Habsatu da Hauwa Mammange da ita kanta Saudatu Modibbo Kilo.

An ci gaba da samun mata masu rubuta waƙa a cikin Ajami har zuwa ƙarni na 20. Turawa sun shigo ƙasar Hausa shekara 38 bayan rasuwar Nana Asma’u, kuma sun zo da tsarin karatunsu na boko inda suka fara ba maza dama su koyi karatun kafin su ba mata. Mata ba su samu wannan damar ba sai a shekarun 1930 zuwa 1960 lokacin aka fara kulawa da iliminsu na zamani da bunƙasarsu, (Mack, 2016). Kafin nan maza sun yi nisa da fara rubuta waƙa a cikin Hausar boko, don haka su aka fi sani da buga waƙoƙinsu kafin a san na mata. Mafi yawan matan da ke rubuta waƙa da Hausar boko matan aure ne ko ‘yan mata da ke ƙarƙashin iyayensu, don haka ba su samun fita zuwa wasu wurare (kamar gidajen rediyo da talabijin) don nuna fasaharsu kamar yadda maza ke yi. Bugu-da-ƙari, ba a daɗe da bawa aikin mata muhimmanci ba, balle a yi nazarinsu ko a fito da su duniya ta ji su ta san su. Mata ba su cika samun shawarwari daga ƙwararru game da rubuce-rubucensu, musamman a fagen rubutattar waƙa inda har yanzu ba a jin sunayen mata marubuta waƙoƙi kamar yadda ake jin na maza irin su Aƙilu Aliyu da Aliyu Namangi da Yusuf Kantu da Alƙali Haliru Wurno da sauransu, (Ibrahim, 2010). Ko Nana Asma’u da ta yi suna a fagen waƙa lokacin masu jihadi, ba a daɗe da tattaro waƙoƙinta ba aka sa cikin littafi, kuma mata ne suka yi wannan hoɓɓasar, watau Boyd da Mack.

Duk da haka an samu wasu mata da suka rubuta waƙoƙi a kan addini da neman ilimi musamman na mata da wa’azi. Da yake asalin rubutattar waƙar Hausa daga addini ne, shi ya sa mafi yawan abubuwan da ake tattaunawa ba su wuce na addini ba. Waɗannan matan sun haɗa da Maimuna ‘Yar Isma’ila wadda ta rayu a Kano tsakanin shekarun 1895-1987, da Zainab Ahmad Sufi da Hassana Ahmad Sufi. An kuma samu su Hauwa Gwaram da Hajiya ‘Yar Shehu da ke magana a kan abubuwan rayuwa da na zamani waɗanda ke tusgowa a cikin waƙoƙinsu. Waɗannan mata suna kishin mata kuma su suka gwada muna yadda rayuwar mata take a ƙasar Hausa, musamman dangane da ladabi ga miji da tsaftace gida da kare mutunci da karɓar canjin da zamani ya zo da shi. Watau dai suna nuna ra’ayin mata a kan halin da mata suke ciki a Arewa. Kafin daga baya-bayan nan da aka samu mata da suka fara rubutu a kan soyayya da zamantakewar aure (kishi) da abubuwan da suka shafi zamani da matsalolin rayuwar mata a yanzu, kamar su Hauwa Habibu Alhassan da Zuwaira Isah Jos da Sa’adatu Baba Ahmad da Sadiya Yusuf da sauransu.

Matsayi da Rayuwar Mata a Rubutattun Waƙoƙi Na Mata

Hauwa Gwaram ta yi waƙar ‘Buɗe Kos a Tsohuwar Laburare Sabon Gari’ inda ta nuna yadda mata za su inganta rayuwarsu ta hanyar koyon sana’a don su samu abin dogaro da kai, tana cewa:

Ina so in gargaɗi matan garin nan,

  Ku zan daina yawo ku kama sana’a.

Idan dai lalura ta sa kun fita,

  Ku dawo ku zauna ku kama sana’a.

Ku dubi abin da ake kwanakin nan,

  Ishara da tsoro rashin yin sana’a.

(Hauwa Gwaram: Waƙar ‘Buɗe Kos)

Marubuciyar mace ce mai kishin mata, kuma wadda ke so ta ga rayuwar mata ta inganta. A cikin waɗannan baitoci tana nuni da cewa, mata su daina zaman banza da yawon banza su rungumi sana’a, wadda ba ta iya ba ta je ta koya. Sana’a da ma hanya ce ta samun abin dogoro da cimma burin rayuwar yau da kullum. Duk wadda ba ta sana’a rayuwarta ba za ta inganta ba kamar yadda Salima Auwal Jegara ta ce a cikin shirin Mujallar Iyali a NTA Sokoto cewa: “idan mace tana son ta san kanta, kuma ta taimaki kanta a san ko ita wace ce to, ta rungumi sana’a, saboda garkuwa ce ga ‘ya mace”. (Jegara, 27/12/2015). Wannan haka yake, saboda yanzu zamani ya kawo cewa dole mace ta kasance tana da wani abu da za ta taimaka ga gida. Ko matan masu kuɗi suna da tasu irin sana’a da suke yi cikin gida ko tsakanin ƙasa da ƙasa domin su taimaki kansu da iyalansu da ‘yan uwansu. Bugu-da-ƙari, sana’a na rage tunani, tana kuma hana zaman banza da gulma da tsintse ga mata baya ga maganin ƙananan buƙatoci na yau da kullum.

Gwaram ta sake kallon mata a matsayin masu daraja da mutunci da ya kamata su tashi tsaye su kare wannan mutuncin a duk inda suke. Su kuma kame kansu daga maza maɓannata ta hanyar suturta jikinsu don kada su ba su sha’awa. Hausawa kan ce “Mutunci dai madara ne idan ya zube ba ya kwasuwa”. A cikin waƙarta ta Lulluɓi ta nuna jikin mata yana da martaba da daraja, don haka dole su rufe shi don kare mutunci inda take cewa:

Ƙaddara in ta kira ki,

Kin fito waje za a gan ki,

Sai a gan ki da lulluɓinki,

Dena nunin kyawun jikinki,

 Lulluɓi na kyau da mata.

In kuna waje ko a ɗaki,

Ɗaure kai zai kyau gare ki,

Yafa ɗan gyale sai ɗiyarki,

Sam mutunci gun zamanki,

Lulluɓi na kyau da mata.

Kun ga mataye na sunna,

Ba su kwance zani su zauna,

Kishiyoyi ‘yan uwana,

Ba faɗa balle hiyana,

 Lulluɓi na kyau da mata.

Mumuna mai son ta tsira,

Ita ce ta kula da gyara,

Ba ta yin yawo tsirara,

Ba ta roƙon masu nera,

 Lulluɓi na kyau da mata.

(Hauwa Gwaram: Waƙar Lullubi)

Idan aka dubi waɗannan baitoci da idon basira, za a fahimci cewa suture ta jiki wajibi ce ga mata, ko suna cikin gida ko idan lalurar fita ta kama su. Ana mutunta mace a darajanta ta ta hanyar suturar da ke jikinta wanda zai kare mutuncinta daga mazan banza. Suturta jiki ga mace yana kuma kare ta daga iska (jinnu), domin ta nan ne suke samu su shiga jikin mata, musmman waɗanda ba sa rufe kai ko ɗaura ɗankwali. Marubuciyar a matsayinta na mace, tana so ta ga rayuwar mata ta inganta shi yasa ta ɗauki mata a matsayin masu mutunci musamman idan suna kare mutuncinsu ta hanyar suturta jikinsu da yin lulluɓi a gida ko a waje. Su kuma kama kansu daga kwaɗayin abin duniya kamar kuɗi, musamman a hannun mazan banza wanda shi ke zubar da mutunci, kuma yawo tsirara ke kaisu mahalaka wani lokaci har a yi musu fyaɗe. Ta kuma faɗakar da su kan zamantakewarsu da kishiyoyi da su ɗauke su kamar ‘yan uwa ne, a zauna lafiya don a amfani juna.

Ita kuwa Hajiya “Yar Shehu ta kalli mata a matsayin masu kwaɗayi da son abin duniya, inda har wasu mata ke cutar mazajensu na aure don abin duniya, suna bin mazan banza fasiƙai don su samu kuɗi ko su yi gadaje irin na wasu mata. Hausawa dai kan ce ‘idan ba ki da gashin wance, kada ki ce za ki yi kitson wance’. Wannan shi ne kiran da ‘Yar Shehu ta yi wa mata don su masu daraja ne don haka dole su yi kariyar mutunci da tsare amanar aure inda take cewa:

Gargaɗina ga mata masu bin sunna,

 Ku tsare amana ta aure har da addini.

Ku riƙe mazanku ku daina kula da banzaye,

 Maƙiyan Rasulu abokan nan na shaiɗani.

 ....................................................................

Me za su ba ku ya amfane ku nan duniya?

 Har za ku cutar da kanku ku saɓi Rabbani.

Har ma ku cuci mazanku ku ɓata aurenku,

 Kuma ran ƙiyama ku tashi cikin su fattani.

Don Allah domin ma’aiki na yi roƙon ku,

 Mu daina kallon gadajen nan na zamani.

Mu daina kallon kumbobi gami da kabod,

 Su ne suke sa waɗansu su bi shi shaiɗani.

(‘Yar Shehu: Waƙar Zamani).

Hajiya ‘Yar Shehu mace ce mai son ta ga rayuwar mata da addininsu sun inganta. A waɗannan baitoci ta nuna cewa wasu mata suna da kwaɗayi da son abin duniya da gasa na wance ta yi ni ma sai na yi ko da ba ni da shi, wanda ke kai su ga bin maza banzaye. Akwai kuma wasu maza da ke ƙoƙarin ɓata rayuwar mata musamman waɗanda ba su san darajar aure ba, suna ruɗin matan aure da dukiya, har su sa su keta rigar mutuncinsu su ci amanar mazansu na aure. Wannan waƙar an yi ta da daɗewa, amma har yanzu za ta yi aiki ga mata, don har yanzu ana samun irin waɗannan mata da maza masu halin banza a cikin al’umma.

Sa’adatu Baba Ahmad marubuciya ce ta waƙoƙi da ke taɓo rayuwar mata a cikin waƙoƙinta. Ta wallafa littafi mai suna Muryoyin Zuci inda take faɗin abin da ke ƙarƙashin zuciyarta dangane da rayuwar mata. A ganinta, a ba mata ilimi shi ne mafita ga matsalolinsu, domin ilimi shi ne gishirin zaman duniya. A cikin waƙarta ta ‘Mu Nemo Mafita’ tana cewa:

Mu nemo ilimi a makaranta.

Mu riƙe sana’a kar mu sangarta.

Walau a daraja mun cancanta.

Sai da ƙarin ilimi za mu ƙasaita.

..................................................

Ku taho mu mamaye aikin likita.

Don mu dinga ceto rayuwar mata.

Da aikin shari’a don ƙwato haƙƙin mata.

Kar mu tsaya muna ta yin mita.

Ilimin addini shi ne kaɗai gata.

Mai yawan iso da kyakkyawan fata.

Rabbi temaki rayuwarmu ‘ya’ya mata.

(Sa’adatu Baba Ahmad: Waƙar Muryoyin Zuci).

 

Sa’adatu Baba na kallon mata a matsayin masu ceton ‘yan uwansu mata daga matsalolin rayuwa, musamman idan suna da ilimi na addini da na zamani. Daga waɗannan baitoci za a fahimci cewa duk macen da ke da ilimi ko sana’a ta cancanci a darajanta ta kuma dole ta yi ƙasaita. Don haka, samun ilimi ga mata zai taimaka ga kiyon lafiyarsu da ƙwato wa kansu haƙƙi a ɓangaren shari’a. Ke nan wajibi ne ga mata su nemi ilimi na addini da na zamani domin su kyautata rayuwarsu da ta ‘yan uwansu mata.

Ita kuwa Ruƙayya Sabuwa Nasiru tun a shekarar 1948 ne ta kalli mata a matsayin masu kishi. Ta nuna haka a cikin waƙarta ta ‘Kishi’ cewa akwai mata masu mugun kishi wanda ba ya da amfani kuma yana lalata zamantakewa tsakanin ‘yan uwansu mata. Misali:

Ya ‘yan uwana mata

 A aje kishi a huta ne.

Shi fa kishi wahala ce,

 Kuma kullum fargaba ne.

Kuma koma baya ne,

 ‘Yan uwa da za a gane.

(Ruƙayya Sabuwa Nasiru: Waƙoƙin Hikima)

Wannan marubuciya ta san mata suna da kishi wanda ke wahalar da su a gidan mazajensu, saboda kodayaushe cikin fargaba suke na me zai faru anjima ko gobe na tashin hankali daga kishiya. Shi ya sa ta yi kira gare su da su aje kishi su huta wa rayuwarsu ko za su ci gaba.

Matsalolin Take Haƙƙi Da Cin Zarafin Mata

Idan aka ce take haƙƙi. ana nufin hana wa mutum wasu haƙƙoƙi da ya kamata ya samu a rayuwa. Wahala, da wuya wadda mutum ke sha ko yake fama da ita ta wasu aikace-aikace ko wani abu da ya fi ƙarfinsa ko yake neman ya fi ƙarfinsa wanda aka aza masa dole sai ya yi, alhali ba haƙƙinsa ne ya yi su ba, a nan shi ake kira take haƙƙi. Cin zarafi kuwa shi ne a keta haddin mutum ko a ci mutuncinsa da nufin tozartawa kai shi maƙura.

Duk da yake mata a ƙasar Hausa, sun saba da ayyukan gida da suka haɗa da daka da girki da ɗibar ruwa da shara da wani lokaci kula da dabbobi. To, amma saboda zamani da samun ilimin addini da sanin haƙƙoƙin da addini ya ba su, yanzu mata na ganin waɗannan ayyuka a matsayin matsalolin da yakamata a rage musu ko suna samun sukunin yin wasu abubuwa kamar neman ilimi da kula da yara da yin sana’o’in zamani, wanda rashin yin haka a gare su tamkar take haƙƙi ne. Wannan ya sa wasu marubuta mata suka fara fito da waɗannan ayyuka a cikin adabin da suke ginawa a matsayin matsalolin da ke ci wa mata tuwo a ƙwarya, kuma suke take musu wasu haƙƙoƙi na ci gaban rayuwarsu.

Marubuciya Sa’adatu Ahmad (2010), ta fito da yadda ake take haƙƙin mata a hana su sukuni a al’umma a matsayin matsalar da ke damun mata a cikin waƙarta ta ‘Mu Nemo Mafita’ a littafin Muryoyin Zuci inda take cewa:

Guri da yawa mun sani mata.

Muna shan wahalar bauta.

Wasu surfe da daka suna kanta.

Wata an mutu da ‘ya’ya an bar ta.

Wata an kore ta har ita har ‘ya’yanta.

Wasu wajen haihuwa suke samun cuta.

Ta yoyon fitsari akwai da yawan mata.

Wasu an sake su don sun furta.

Bin tsarin gaskiya da cancanta.

Wajibi ne a kanmu mu gaggauta.

Mu nemo wa kanmu mafita.

Domin a yau lamari ya gawurta.

A na ta take haƙƙin mata.

Shin ina za mu mu nemo mafita.

(Sa’adatu Ahmad: Waƙar Muryoyin Zuci)

Lalle tabbas marubuciya Sa’adatu Ahmad ta fito da matsalolin da mata ke fuskanta a wannan zamani, wanda dole ne mata su tashi tsaye su ƙwato haƙƙinsu su kuma nemo wa kansu mafita. Ta yi magana a kan wahalhalun da mata ke fama da su na aikace-aikacen gida duk da ba su samun kulawa ga lafiyarsu, da matsalolin cututtuka iri-iri da mata ke fama da su a sanadiyar haihuwa ko zamantakewar aure irin su hawan jini da cutar yoyon fitsari, ga take haƙƙinsu da ake yi duk da Musulunci ya buƙaci a tausaya wa mata ba a azabtar da su ba, a sauƙaƙa musu ba a wahalar da su ba, Maƙera, (2017:30). Ana amfani da al’ada ne kawai ana jibga musu ayyuka, kuma ana hana su yin ƙorafi. A ganin Maƙera idan aka ga miji na wulaƙanta matarsa a tabbata ya jahilci Musulunci, haka idan aka ga uba yana wulaƙanta ‘yarsa mace a tabbata ya jahilci Musulunci.

Ita kuwa Hajiya ‘Yar Shehu ta fito da matsalar cin zarafin mata da wasu maza ke yi musamman ga matan aure har ma da ‘yan mata, musamman idan suka gan su a waje sun fito don yin lalura. Wannan takurawar matsala ce ga mata wadda shugabanni da hukumomi ba su cika ɗaukar mataki a kai ba. ‘Yar Shehu na cewa:

Kan tituna kwararo lungu da banzaye,

Ya kai shararai gumakai babu imani.

In sun ga mata na aure sai su dinga kira,

 Ke Binta, ke Hajiya har ma da fige zani.

In an ka sami ta kirki ba ta tankawa,

 In sun ka sami shararu su saɓi Rabbani.

Allah tsare mu da su amin ku ce jama’a,

 Mata maza har da yara masu imani.

To malamai da sarakai ga wasiƙata,

 Na durƙusa na ba ku don ku gani.

 ………………………………………..

Domin faɗar Rabbi na ku anka ba kiwo,

 Daidai muke da makafi waɗanda ba su gani.

Ku za ku ja mana gora har ku kai mu gari,

 Ku fitar da mu daga sharrin nan na shaiɗani.

To shi ya sa na yi ƙara gunku don ku sani,

 Aikinku ne ku tsare haƙƙi na Rabbani.

(Hajiya ‘Yar Shehu: Waƙar Zamani)

Wannan marubuciyar na magana ne a kan matsalar da mata ke fama da ita ta cin zarafinsu da wasu mazan banza ke yi wa matan aure a kan hanya musamman da dare idan lalurar fita ta same su. Ana samun maza masu cafken sunayen mata don su kula su, kuma sukan dace wani lokaci har su samu irinsu sheɗanu. Ta fito ƙarara ta nuna cewa ƙara ce take yi ga shugabanni don su kula, kuma su kawo musu agaji a kan wannan cin zarafi da ake yi wa mata, saboda matsalar tana ci musu tuwo a ƙwarya.

Matsalar Daƙushe Cigaban Mata

An daɗe ana daƙushe cigaban mata a fannoni da yawa na rayuwar yau da kullum, saboda wasu dalilai na daban. Don haka mata na fama da matsalar ci gaban rayuwa da wani lokaci al’umma ke daƙushewa musamman tauye su da ake yi wajen neman ilimin ta hanyoyi da dama. Waɗannan hanyoyi sun haɗa da tusge su daga makaranta da ake yi ana yi musu aure ba tare da sun ci gaba da karatu ba, da kuma hana su samun cikakken ilimi don wata manufa da ma talla da ake sa su yi wadda ke lalalta tarbiyyarsu da rayuwarsu gaba ɗaya. Wani lokaci kuma su ke hana ci gaban kansu da kansu musamman ta ɓangaren sana’a, domin wasu mata sun fi son zaman banza. Misali Sa’adatu Ahmad, a waƙarta ta ‘Mu Nemo Mafita’ a littafin Muryoyin Zuci ta yi kawo matsalar rashin son sana’a da wasu mata ba su son yi, sai dai su dogara ga wasu kuma ba su son neman ilimi saboda lalaci, inda take cewa:

 Waƙa zan tsara manufata.

 Wacce ta shafi rayuwarmu mata.

 A yau babu zancen mu kwanta.

 Ko mu tsaya wajen yin wauta.

 Mu nemo ilimi a makaranta.

 Mu riƙe sana’a kar mu sangarta.

 Walau a daraja muna cancanta.

 Sai da ƙarin ilimi za mu ƙasaita.

(Sa’adatu Ahmad: Muryoyin Zuci)

A nan Sa’adatu ta nuna dalilinta na tsara waƙa shi ne, domin ta jayo hankalin mata a kan zaman banza da suke yi ba su neman ilimi ko yin sana’o’i don inganta rayuwarsu. Ilimi muhimmin abu ne a rayuwar ɗan Adam domin shi ne abin da ke tabbatar da mutuntakar mutum kuma da shi ne Allah (SWT) ya fifita ɗan Adam a kan sauran halittu, (Bugaje, 2011). Ita kuma mace mai ilimi tana samun ƙarin daraja da ƙima a idon al’umma har ta yi ƙasaita.

Marubuciyar ta ci gaba da yin kira ga mata da cewa iliminsu zai taimaki rayuwar mata, inda take cewa:

Ku taho mu mamaye aikin likita

Don mu dinga ceto rayuwar mata

Da aikin shari’a don ƙwato haƙƙin mata

Kar mu tsaya muna ta yin mita

Ilimin addini shi ne kaɗai gata

Mai yawan iso da kyakkyawar fata

Rabbi taimaki rayuwarmu ‘ya’ya mata.

(Sa’adatu Ahmad: Muryoyin Zuci)

A nan marubuciyar ta nuna cewa matsalolin mata sai mata kaɗai ke iya warware su, don wani abu sai mace kamar asibiti da sauran wurare, sannan yin ilimin shari’a ga mata zai taimaka wajen danniyar da ake yi wa mata a fannin shari’a musamman ta gefen aure da zamantakewa.

Hassana Sufi ma a cikin waƙarta ta ‘Ilimi’ ta kawo matsalar talla da wasu iyaye ke jefa ‘ya’yansu a cikin masifa da yarda haƙƙinsu na ba yara ilimi musamman mata don kwaɗayin abin da bai taka kara ya karya ba, inda take cewa:

‘Ya’ya fa haƙƙinsu na nan kan iyayensu,

 Su sa su hanyar karatu don su san ilmu.

Amma yawancin mu ba a kula da ‘yan yara,

 Tun ba a ce mata ba, sai ta girma ba ilimu.

Sai dai a ce “Zo ki ɗau tallar, ki je ki yi man,

 Mu san abin hid da kunya”, ba batun ilmu.

To” in ba kiy talla ba, me za a sayi,

 Kayan da zan kai ki ɗaki”, ki ji matanmu

Ta gantale, ta lalace duk a kan titi,

 Tallar da ba ta ƙulla komai, sai yawan jurmu.

(Hassana Sufi: waƙarta Ilimi)

Marubuciyar na nuna yadda talla da rashin neman ilimi ga ‘ya’ya mata ke zama babbar matsala ga ci gaban rayuwa. Ta nuna iyaye musamman mata ke hana ‘ya’ya mata neman ilmi saboda tallar da ba ta ƙulla masu komai in ban da sa su su lalace su hinjire a sanadiyar talla a tituna.

Sa’adatu Ahmad, ma ta tsoma albarkacin bakinta a kan talla inda ta ce:

Mu riƙe sana’a don samun nagarta

 Kun san wasu da yawa ‘yanmata

 Gun talla maza ke mu su cuta.

(Sa’adatu Ahmad: Muryoyin Zuci)

 

Waɗannan mata suna cikin sahu na farko a ɓangaren rubutattar waƙa da suka fara rubuce-rubuce a kan inganta rayuwar mata da magance matsalolinsu da kawo sauyi a kan kallon da ake yi wa mata a duniya. Ko bayan su akwai ɗimbin mata da ke rubuta waƙoƙi a harshen Hausa waɗanda ba a jin muryoyinsu balle a san saƙon da suke ɗauke da shi, saboda rashin kulawa da ayyukan mata da al’umma ke nunawa.

Dukkan misalan waƙoƙin da aka kawo waɗanda mata suka rubuta ne, kuma suna magana ne a kan matsaloli da matsayin da Allah ya ba mata. Watau dai har yanzu ciwon mace na ‘ya mace ne domin a cikin waƙoƙin da mata suka rubuta kaɗai ake iya samun waɗannan matsaloli suna fitowa, ko an samu a na maza sai dai suka da wa’azi a kan su.

Shawarwari:

·                     Zai yi matuƙar kyau da amfani idan mata marubuta waƙoƙi suka haɗa kansu, suka yi ƙungiya mai ƙarfi wadda za ta fito da ɗimbin ayyukkansu a fili duniya ta san da su, domin suna ɗauke da hikima da fasaha kila ma fiye da na takwarorin su maza.

·                     Da a ce ana saka waɗannan waƙoƙi da mata suke rubutawa a rediyo kamar yadda ake saka na maza da kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

·                     Ya kamata a fara nazarin waƙoƙin da mata suke rubutawa a manyan makarantu domin fito da ɗimbin saƙo da hikimar da ke cikinsu.

·                     Ya kamata a samu waɗanda za su tattaro waƙoƙin da mata suka rubuta, domin a fito da su a matsayin babban kundi ko littafi don madogara, saboda mata ba su cika mayar da waƙoƙin a matsayin littafi ba kamar yadda ake buga na maza, saboda rashin kuɗi da shawarwari.

·                     Ƙwararri da masana su riƙa dubawa tare da yin gyara ga duk macen da ta ƙoƙarta ta rubuta waƙa, domin a samu ci gaba, a kuma ba su ƙwarin guiwa.

·                     A fito da gasa ta musamman ga mata ta rubuta waƙa, kuma a tallafa musu a buga a matsayin littafi bayan sun yi gyare-gyaren da aka yi musu.

 

Kammalawa

Muƙalar a kan yadda mata marubuta ke fito da matsayi da matsalolin rayuwar mata ne a cikin rubuce-rubucen da suke yi na waƙa. daga misalan da aka kawo na wasu baitoci da wasu mata suka gabatar a cikin rubutattun waƙoƙinsu, za a iya kammalawa da cewa mata suna kallon ‘yan uwansu mata a matsayin masu daraja da mutunci musamman idan suka kama kansu kuma suka nemi ilimi tare da riƙa sana’a domin dogaro da kai da kauce wa wulaƙanta.

Haka kuma muƙalar ta gano cewa mata ne suka fi fito da matsalolin mata ‘yan uwansu a cikin waƙoƙin da suke rubutawa don yin gargaɗi ga al’umma da su kansu matan

 An kuma kawo shawarwari waɗanda ake ganin idan an bi su ɗaya bayan ɗaya za a cimma gaci na samun ingantattun litattafai na waƙoƙin da mata suka rubuta, a kuma samu ƙarin ilimi na rayuwa musamman ta mata da zamantakewarsu da gudummuwar da suke bayarwa ga al’umma. Lalle ruwa na ƙasa, sai da rashin tono.

Manazarta

Ahmad, S. B (2010). Muryoyin Zuci (Waƙoƙin Hausa).Kano: Triumph Publishing Company.

Boyd, J. & Mack, B. (1999). The Collected Works of Nana Asma’u, Daughter of Usman Ɗanfodiyo, (1793-1864). Ibadan: Sam Bookman Publishers.

Boyd, J. & Mark, B. (1999). The Caliph’s Sister: Nana Asma’u 1793-1865.Teacher, Poet and Islamic Leader. London: Frank Cass.

Ibrahim, B. (2010). ‘Gudummuwar Mata A Rubutaccen Adabi’. Kundin Digiri na Uku, Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Jibril, S. (1975). ‘The Status of Women in Hausa Literature’. M.A Thesis, Zaria: Ahmadu Bello University.

Mack, B.B. (1981). ‘Waƙoƙin Mata: Hausa Women Poetry in Northern Nigeria’, Ph.D, Madison: Wisconsin University.

Mack, B.B, (1983). Alƙalami A Hannun Mata: Waƙoƙi daga Hajiya Hauwa Gwaram da Hajiya ‘Yar Shehu. Zaria: NNPC.

Mack, B. B. (2016). Full Circle: Muslim Women’s Education from the Magrib to America and Back. Patricia Lercin, New York: Routledge/Taylor and France (UK).

NNPC. (1974). Waƙoƙin Hikima. Zaria.

 Omar, S. (2013). Modibbo Kilo (1901-1976) Rayuwarta Da Ayyukanta (Ta Biyu Ga Nana Asma’u Bint Fodiyo a Ƙarni na 20). Zaria: Ahmadu Bello University Printing Press.

Omar, S. (2014). ‘Yantarun Nana Asma’u Ɗanfodiyo: Tsarinsu da Taskace Waƙoƙinsu. (B.W) Kamfanin Zeetma Investment Ltd.

Omar, S. (2021). ‘Fitattun Malamai Mata na Daular Usmaniyya da Gudummuwarsu a Fannin Rubutacciyar Waƙa a Ƙarni na 19 da 20’. 25th Inaugural Lecture. Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo University.

 Sufi, H. A Cikin Bugaje (2011). Wa’azi a Rubutattun Waƙoƙin Mata na Ƙarni Ashirin. Kundin Digiri na Biyu, Zaria: Jami’ar Ahmadu Bello.

Jarida

Maƙera, S. (2017). “Yadda Musulunci Ya ‘Yanta Mace (2),” Filin Addinnin Musulunci, Shafi na 30. Jaridar Aminiya. 7/7/2017.

Shirin Talabijin

1

Salima Auwal Jegara

Mujallar Mata

NTA Sokoto,

27/12/2015.

 

Mata

Post a Comment

0 Comments